• English
  • Business News
Sunday, May 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samun Tunanin Kashin Kai Zai Tabbatar Da Damar Ci Gaba

by CGTN Hausa
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Samun Tunanin Kashin Kai Zai Tabbatar Da Damar Ci Gaba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A shekarun baya bayan nan, kasar Amurka tana ta neman yin karin tasiri a nahiyar Afirka. Bisa wannan yunkuri, ana ta samun dimbin rahotanni daga kafofin yada labarai na kasashen yamma dake nuna wai “Amurka da Sin na takara da juna a nahiyar Afirka”, da “ kasashen yamma na takara da kasashen Sin da Rasha, da wasu kasashen dake gabas ta tsakiya, don kwatar damar kulla huldar kawance tare da kasashen Afirka”, da dai sauransu daga kafofin yada labarai na kasashen yamma. Hakan na sa mutum tsammanin cewa, watakila kasashen Afirka ba za su iya kaucewa daukar wani bangare, a tsakanin karfin dake takara da juna a duniya ba. Sai dai abun tambaya a nan shi ne ko kasashen na Afirka suna son yin haka?

Wata kila a ki yin zabi, ko ma a magance yarda da ra’ayin maida kasashen yamma cibiyar duniya, da neman dakile saura, zai fi dacewa ga kasashen Afirka, don neman biyan bukatunsu na kare moriyar kai.

  • Xi Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Shugaban Kasar Mozambique
  • Xi Jinping Ya Yi Shawarwari Tare Da Takwaransa Na Indonesia

A wajen taron musayar ra’ayi tsakanin Sin da Afirka ta fannin wayewar kai karo na 3, da ya gudana a kwanan nan a birnin Beijing na Sin, masana da jami’ai na kasashen Afirka da na kasar Sin sun sake jaddada muhimmancin ra’ayin diplomasiyya na magance daukar wani bangare. Kana wannan ra’ayi ya zama daya da tunanin hadin gwiwar Sin da Afirka, wato maimakon nuna son kai da neman dakile saura, a bude kofa domin kowa ya iya halarta, da aiwatar da tunani na kasancewar dimbin bangarori masu fada a ji a duniya.

Taron na wannan karo ya kunshi dandalin tattaunawa guda 2, daya ya shafi musayar ra’ayi cikin daidaito, kan al’adu da tunani na Sin da Afirka. Daya kuwa ya shafi musayar ra’ayin raya kasa, don aza harsashin hadin gwiwar nan gaba. Kana babbar ma’anar taron ita ce, kamar yadda Rahamtalla M. Osman, jakadan kungiyar tarayyar kasashen Afirka AU a kasar Sin ya fada, “Daidaita ra’ayi da magance bahaguwar fahimta, ta yadda za a karfafa fahimtar juna da girmama juna da hadin gwiwa, ta hanyar yin musayar ra’ayi”.

Nufinsa shi ne, ta hanyar tattaunawa, ake neman kawar da shingen tunani da ra’ayoyi marasa dacewa, da kasar Amurka da wasu kasashen dake yammacin duniya suka sanya wa kasashen Afirka da kasar Sin, da sauran kasashe masu tasowa. Ta yadda za a samu tunani na kai, da yiwuwar dogaro da kai, da samun ci gaban kasa mai dorewa.

Labarai Masu Nasaba

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

Irin wannan cudanyar ra’ayi mai daraja, ta sa ana ta samun tunani masu muhimmanci a tarukan musayar ra’ayi, tsakanin Sin da Afirka ta fannin wayewar kai, da aka taba gudanarwa a baya.

Misali, Rahamtalla M. Osman, jakadan kungiyar kasashen Afirka AU a kasar Sin, ya taba bayyanawa a madadin kungiyar AU cewa, ya kamata a daina ta da rikici tsakanin mabambantan wayewar kai, da neman tabbatar da kasancewarsu tare, da daina ganin al’adun wasu sun fi na wasu, tare da karfafa cudanya, da koyi da juna tsakanin wayin kai daban daban.

Sa’an nan a nasa bangare, shugaban cibiyar nazarin manufofin kasashen Afirka na kasar Kenya Peter Kagwanja, ya taba bayyana cewa, “Aikin zamanantar da kasar Sin, da yadda ake neman zamanantar da kasashen Afirka sun bambanta, amma za a iya kaiwa ga cimma buri guda daya. Saboda haka, ci gaban kasar Sin ya karfafa gwiwar jama’ar kasashen Afirka. Mu ma muna son tabbatar da zamanantarwa bisa dogaro da karfin kanmu.”

Ban da haka, Charles Onunaiju, darektan cibiyar nazarin kasar Sin ta kasar Najeriya, ya taba bayyana cewa, babbar matsala da kasashen Afirka suke fama da ita, ita ce talauci. Kana babban dalilin da ya sa muke kokarin zamanantar da kanmu shi ne don biyan bukatun jama’a. A cewarsa, “ Ya kamata mu koyi dabarun da kasar Sin ta samu, a kokarinta na raya kai. Sa’an nan mu yi kokarin ganowa da daidaita muhimmin bangare dake bukatar a daidaita shi, yayin da muke neman raya tattalin arziki da zaman al’umma na kasashen Afirka. ”

Ta jawabansu za mu iya ganin cewa, jami’ai da masana na kasashen Afirka, sun fara dora karin muhimmanci kan kasancewar mabambantan wayewar kai tare (maimakon samun takara da rikici a tsakaninsu), da dogaro da kai a kokarin neman ci gaban kasa ( maimakon rungumar wai “daidaitaccen tsari” na kasashen yamma na tabbatar da ci gaba), da kokarin biyan bukatun jama’a (maimakon dora nauyi kan tsarin kasuwa mai ‘yanci), da sauran tunani, wadanda suka sha bamban da ra’ayoyin kasar Amurka, da na sauran kasashen yammacin duniya.

 

Hakan ba wani abun ban mamaki ba ne, saboda fasahohin da kasar Sin ta samu a kokarin raya kanta, sun nuna mana cewa, dole ne a samu tunani na kai, kafin a kai ga samun cikakken ‘yancin kai. Kana ya kamata a bi hanyar raya kasa ta musamman, da ta dace da yanayin da kasa ke ciki, har a kai ga samar da hakikanin ci gabanta. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Cikin Kwanaki 20, CBN Ya Sallami Ma’aikata  Fiye Da 100

Next Post

NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda Tare Da Tarwatsa Sansanoninsu A Zamfara 

Related

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka
Ra'ayi Riga

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

4 days ago
Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci
Ra'ayi Riga

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

7 days ago
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

1 week ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

1 week ago
Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba
Ra'ayi Riga

Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba

2 weeks ago
Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
Ra'ayi Riga

Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya

3 weeks ago
Next Post
Jirgin Sojoji Ɗauki Ya Kai Ba Luguden Wuta A Chikun Ba – Gwamnatin Kaduna

NAF Ta Kashe 'Yan Ta'adda Tare Da Tarwatsa Sansanoninsu A Zamfara 

LABARAI MASU NASABA

Masana Kimiyya Na Kasar Sin Sun Gano Wata Sabuwar Hallita A Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar 

Masana Kimiyya Na Kasar Sin Sun Gano Wata Sabuwar Hallita A Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar 

May 17, 2025
Crystal Palace Ta Lashe Kofin FA Karon Farko, Ta Doke Manchester City 1-0

Crystal Palace Ta Lashe Kofin FA Karon Farko, Ta Doke Manchester City 1-0

May 17, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 17, 2025
Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taro Na 34 Na Kasashen Larabawa

Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taro Na 34 Na Kasashen Larabawa

May 17, 2025
Jami’ar FUDMA Ta Ƙara Fadawa Cikin Rikicin Shuagabanci A Katsina

Jami’ar FUDMA Ta Ƙara Fadawa Cikin Rikicin Shuagabanci A Katsina

May 17, 2025
Rokar Kasuwanci Ta Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 6 Zuwa Sararin Samaniya

Rokar Kasuwanci Ta Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 6 Zuwa Sararin Samaniya

May 17, 2025
Gidan Adana Kayayyakin Tarihi Na Amurka Ya Mayarwa Kasar Sin Rubuce-rubucen Hannu Masu Daraja Na Lokacin Yake-yake A Kasar

Gidan Adana Kayayyakin Tarihi Na Amurka Ya Mayarwa Kasar Sin Rubuce-rubucen Hannu Masu Daraja Na Lokacin Yake-yake A Kasar

May 17, 2025
Bude Kofar Kasar Sin Dama Ce Ga Duniya Har Abada

Bude Kofar Kasar Sin Dama Ce Ga Duniya Har Abada

May 17, 2025
Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Mutum 3 Sun Rasu, Wasu Sun Jikkata Yayin Da Bama-bamai Suka Tashi A Hanyar Borno

May 17, 2025
Hukuma Ta Haramta Bikin Ranar Kauyawa A Kano

Hukuma Ta Haramta Bikin Ranar Kauyawa A Kano

May 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.