• English
  • Business News
Tuesday, August 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

by Leadership Hausa
3 days ago
in Siyasa
0
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan ƙaddamar da majalisar dattawa ta 10 a ranar 13 ga Yunin 2023, majalisar na shan suka daga wasu ‘yan Nijeriya waɗanda suke ganin ta zama ‘yar amshin shatan a ɓangaren fadar shugaban ƙasa.

Masana harkokin siyasa sun yi iƙirarin cewa sabbin sanatocin yanzu suna yin aiki ne ba don cika ƙa’idoji ba, suna amincewa da ƙudirorin da ɓangaren zartarwa ya gabatar ko wasu manyan hukumomi suka yanke hukunci, maimakon shiga cikin tsarin samar da dokoki da wakilci na gaskiya da kuma gudanar da bincike da tsarin mulki ya ɗora wa majalisa.

  • Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi
  • Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Masanan sun bayyana damuwarsu kan cewa akwai rashin ‘yancin kai na gaske da kuma sake yin nazari mai zurfi ta yadda majalisar take amincewa da sakamako da aka riga aka yanke.

Wasu ‘yan Nijeriya sun bayyana rashin jin daɗinsu kan cewa sama da sanatoci 40 ba sa yawan halartar taron majalisa da zaman kwamitoci ko kuma ba da gudunmawa a muhawara ake fafatawa a zauren majalisar dattawa.

Hazalika, masana harkokin siyasan sun cewa yawancin ‘yan majalisar dattawan zai yi wuya su halarci zaman majalisar tun daga ranar Talata zuwa Alhamis a kowane mako. Sun nuna matuƙar damuwa kan wannan lamari, wanda ko ma sun zo suna kasancewa masu ɗumama kujera ne kawai ba tare da gabatar da wani ƙudiri ba duk da adadin kuɗaɗen da suke karba a matsayin alawu da albashi da sauran fa’idodi da ake ba su.

Labarai Masu Nasaba

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

Yawancin ‘yan Nijeriya sun nuna damuwa game da yadda majalisar dattawa ta 10 ke gudanar da harkokin majalisa, suna cewa ‘yan majalisar sun gaza bayar da muhimman ayyukan da aka ɗora musu na binciken ɓangaren zartarwa don kare ‘yan Nijeriya.

Ana zargin majalisa dattawa ta 10 da ƙin tilasta wa gwamnatin tarayya wurin magance tarin ƙalubale da ke fuskantar ‘yan Nijeriya, ciki har da tsadar rayuwa, talauci, yunwa, yawan rashin aikin yi da rashin tsaro, da sauran su.

Rahotanni su bayyana cewa akwai tsofaffin gwamnonin 13 da ke majalisar dattawa ta 10 a halin yanzu, wanda suka haɗa da shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio (Akwa Ibom), Aliyu Wammako (Sakkwato), Abdulaziz Yari (Zamfara), Aminu Waziri Tambuwal (Sakkwato) da Adams Oshiomhole (Edo).

Sauran sun haɗa da Ibrahim Hassan Dankwambo (Gombe), Abubakar Bello (Neja), Orji Uzor Kalu (Abiya), Seriake Dickson (Bayelsa), Adamu Aliero (Kebbi), Danjuma Goje (Gombe), Gbenga Daniel (Ogun) da Simon Lalong (Filato).

Masana sun ce daga cikin tsofaffin gwamnonin 13 da ke majalisar, Akpabio, Aliero, Dickson, Oshiomhole, Kalu, Lalong, Daniel, da Goje su ne suke taka rawar gani sosai a lokacin tattaunawan zaman majalisa.

Akwai rahotannin da ke cewa Yari, Dankwambo, Bello, Tambuwal da Wamakko ba sa yawan halartar tarurrukan majalisa ko kuma su shigo cikin muhawara idan sun bayyana. Duk da haka, akwai rahotannin da ke cewa wasu ƙananan ƙudirori ne suka gabatar a zauren majalisar.

Haka zalika, sanatoci irinsu Sahabi Yau, mai wakiltar Zamfara ta Arewa da Eze Kenneth Emeka, mai wakiltar Ebonyi ta tsakiya da Okechukwu Ezea, mai wakiltar Inugu ta Arewa da Anthony Siyako Yaro, mai wakiltar Gombe ta Kudu da Mustapha Khabeeb, mai wakiltar Jigawa ta Kudu da Rufai Hanga, mai wakiltar Kano ta tsakiyar da Binos Dauda Yaroe, mai wakiltar Adamawa ta Kudu da Benson Friday Konbowei, mai wakiltar Bayelsa ta tsakiya da Eteng Jonah Williams, mai wakiltar Kuros Ribas ta tsakiya da Adegbonmire Ayodele, mai wakiltar Ondo ta tsakiyar dukkansu ba su gabatar da wani ƙudiri ba a zauren majalisar dattawa ba har izuwa yanzu.

Haka kuma, akwai sanatoci irinsu Amos Yohanna, mai wakiltar Adamawa ta Arewa da Samaila Kaila, mai wakiltar Bauchi ta Arewa da Ani Okorie, mai wakiltar Ebonyi ta Kudu da Kelɓin Chizoba, mai wakiltar Inugu ta Gabas da Jiya Ndalikali, mai wakiltar, Neja ta Kudu da Onyesoh Allwell, mai wakiltar Ribas ta Gabas da Haruna Manu, mai wakiltar Taraba ta Tsakiya da Napoleon Bali, mai wakiltar Filato ta Kudu da Fadeyi Olubiyi, mai wakiltar Osun ta tsakiya da Shuaibu Isa Lau, mai wakiltar Taraba ta Arewa na daga cikin rukunin sanatocin da ba sa magana a zauren majalisar dattawa.

Sauran su ne Fasuyi Cyril Oluwole, mai wakiltar Ekiti ta Arewa da Osita Ngwu, mai wakiltar Inugu ta Yamma da Onyewuchi Francis, mai wakiltar Imo ta Gabas da Ahmed Madori, mai wakiltar Jigawa ta Arewa maso Gabas da Lawal Adamu Usman, mai wakiltar Kaduna ta Tsakiya da Musa Garba, mai wakiltar Kebbi ta Kudu da Sadiƙ Suleiman Umar, mai wakiltar Kwara ta Arewa da Olajide Ipinsagba, mai wakiltar Ondo ta Arewa da Yunus Akintunde, mai wakiltar Oyo ta Tsakiya da Abdulfatai Buhari, mai wakiltar Oyo ta Arewa da Mpigi Barinda, mai wakiltar Ribas ta Gabas da Babangida Husseini Uba, mai wakiltar Jigawa ta Arewa maso Yamma da Bassey Etim, mai wakiltar Akwa Ibom ta Arewa maso Gabas da Emmanuel Udende, mai wakiltar Benuwai ta Arewa maso Gabas da Godiya Akwashiki, mai wakiltar Nasarawa ta Arewa da Ikra Aliyu Bilbis, mai wakiltar Zamfara ta Tsakiya da Oyewumi Kamorudeen Olarere, mai wakiltar Osun ta Yamma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: SenateSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Next Post

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Related

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

7 hours ago
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

10 hours ago
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027
Siyasa

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

2 days ago
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027
Siyasa

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

3 days ago
ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya
Siyasa

ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

4 days ago
Sai Ƴan Siyasa Sun Haɗa Kansu Sannan Za Su Iya Tunkarar APC A 2027 – Lukman
Siyasa

Sai Ƴan Siyasa Sun Haɗa Kansu Sannan Za Su Iya Tunkarar APC A 2027 – Lukman

4 days ago
Next Post
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto

August 12, 2025
Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

August 12, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

August 12, 2025
Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

August 12, 2025
Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

August 12, 2025
Ma’aikatar Cinikayya Ta Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Kan Batun Saka Wasu Sassa Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Sayar Musu Da Kayayyaki

Ma’aikatar Cinikayya Ta Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Kan Batun Saka Wasu Sassa Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Sayar Musu Da Kayayyaki

August 12, 2025
Ronaldo Zai Daura Aurensa Na Farko A Rayuwa Tare Da Budurwarsa Georgina

Ronaldo Zai Daura Aurensa Na Farko A Rayuwa Tare Da Budurwarsa Georgina

August 12, 2025
Sin Ta Gabatar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakaninta Da Amurka A Stockholm

Sin Ta Gabatar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakaninta Da Amurka A Stockholm

August 12, 2025
Kano

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Kwangilar Hanyoyi 17 Akan Naira Biliyan 40.8

August 12, 2025
Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.