ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

by Leadership Hausa
11 months ago
Baki

A yanzu haka dai cacar baki ta ɓarke tsakanin tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai da jam’iyyar APC mai mulkin Nijeriya kan tallar tazarcen Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu a 2027.

El-Rufai wanda ya kasance tsohon ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, ya yi gargaɗi cewa Nijeriya za ta iya rushewa kwata-kwata idan Shugaba Tinubu ya sami nasara a wa’adin mulki na biyu a 2027.

  • INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12
  • Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

El-Rufai ya bayar da wannan gargaɗin ne a Jihar Sakkwato a lokacin kamfen da haɗakar jam’iyyar adawa ta ADC ta shirya a ƙarshen mako.

ADVERTISEMENT

Sai dai daraktan yaɗa labarai na APC, Bala Ibrahim, ya bayyana shugabannin ADC a matsayin tarin ‘yan siyasa da suke cikin ruɗani waɗanda ba su da abin da za su iya yi wa ‘yan Nijeriya.

Idan za a iya tunawa dai shugabannin adawa sun amince da ADC a matsayin jam’iyyar da za ta ƙalubalanci Shugaba Tinubu a zaɓen 2027.

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

Mambobin haɗakar jam’iyar sun ƙunshi tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar da tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP, Peter Obi da tsohon gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi da tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir Lawal da tsohon shugaban jam’iyyar APC, John Oyegun, da sauran manyan mutane da dama.

A cikin wannan tsarin, haɗakar jam’iyyar ta naɗa tsohon shugaban majalisar dattawa, Daɓid Mark da tsohon ministan cikin gida, Rauf Aregbesola, a matsayin shugaban da sakatare na riƙon ƙwarya.

Tun daga wannan lokaci, jam’iyyar tana ta karɓar masu sauya sheƙa daga sauran jam’iyyun adawa da kuma gudanar da tarurruka domin ƙara masun mambobi a faɗin ƙasar nan kafin zaɓen 2027.

El-Rufai, wanda ya kasance ɗaya daga cikin asalin mambobin APC, ya fice zuwa jam’iyyar SDP a rubi’in farko na wannan shekarar. Haka kuma ya kasance cikin jam’iyyar haɗaka ta ADC.

Ya bayyana cikakken goyon bayansa ga ADC kuma ya yi alƙawarin taimakawa wajen jan hankali ‘yan Nijeriya domin tabbatar da cewa APC ta sha kaye a 2027 a lokacin taron Sakkwato.

Tsohon gwamnan Kaduna ya jaddada cewa idan Tinubu ya samu wa’adi na biyu zai zama barazana mai tsanani ga makomar ƙasar nan.

“Na yi imanin cewa in muka yarda wannan jam’iyya da gwamnatinta ta ci gaba da mulki a zango na biyu, za ta wawuri dukkan abin da ya rage na tattalin arzikin Nijeriya, kuma ba za mu sami ɓarɓushin ƙasarmu ba ko kaɗan. Don haka, wannan yaƙi ne don rayukanmu,” in ji shi.

El-Rufai ya ce dawowarsa cikin harkokin siyasa ba ta ƙashin kansa ba, said ai akwai buƙatar dawowarsa don yaƙar gazawar wannan gwamnati.

Da yake mayar wa El-Rufai martani, sakataren jam’iyyar APC na ƙasa, Sanata Ajibola Basiru, ya buƙaci El-Rufai ya dakatar da yaƙin neman zaɓe 2027 har sai lokaci ya yi, kuma ya jira ya gani yadda jam’iyya mai mulki za ta ƙara yin nasara.

Sakataren APC ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai ta wayar tarho a ƙarshen mako.

Yayin da yake martanin, sakatare APC ya yi kira ga tsohon Gwamnan Jihar Kaduna da ya nemi aiki yi da zai sa ya zama mara zaman banza kafin zaɓen 2027.

Ya nuna cewa za a bayyana jadawalin zaɓen 2027 ne a watan Fabrairun 2026, ya yi mamakin yadda tsohon gwamnan Jihar Kaduna ya fara yaƙin neman zaɓen da ya rage saura shekara biyu.

Baki
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22

MASU ALAKA

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci
Siyasa

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo
Manyan Labarai

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

July 5, 2026
Next Post
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

LABARAI MASU NASABA

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

July 11, 2026
Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

July 11, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK

Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina

July 11, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.