ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

by Leadership Hausa
11 months ago
Sanatocin

Tun bayan ƙaddamar da majalisar dattawa ta 10 a ranar 13 ga Yunin 2023, majalisar na shan suka daga wasu ‘yan Nijeriya waɗanda suke ganin ta zama ‘yar amshin shatan a ɓangaren fadar shugaban ƙasa.

Masana harkokin siyasa sun yi iƙirarin cewa sabbin sanatocin yanzu suna yin aiki ne ba don cika ƙa’idoji ba, suna amincewa da ƙudirorin da ɓangaren zartarwa ya gabatar ko wasu manyan hukumomi suka yanke hukunci, maimakon shiga cikin tsarin samar da dokoki da wakilci na gaskiya da kuma gudanar da bincike da tsarin mulki ya ɗora wa majalisa.

  • Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi
  • Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Masanan sun bayyana damuwarsu kan cewa akwai rashin ‘yancin kai na gaske da kuma sake yin nazari mai zurfi ta yadda majalisar take amincewa da sakamako da aka riga aka yanke.

ADVERTISEMENT

Wasu ‘yan Nijeriya sun bayyana rashin jin daɗinsu kan cewa sama da sanatoci 40 ba sa yawan halartar taron majalisa da zaman kwamitoci ko kuma ba da gudunmawa a muhawara ake fafatawa a zauren majalisar dattawa.

Hazalika, masana harkokin siyasan sun cewa yawancin ‘yan majalisar dattawan zai yi wuya su halarci zaman majalisar tun daga ranar Talata zuwa Alhamis a kowane mako. Sun nuna matuƙar damuwa kan wannan lamari, wanda ko ma sun zo suna kasancewa masu ɗumama kujera ne kawai ba tare da gabatar da wani ƙudiri ba duk da adadin kuɗaɗen da suke karba a matsayin alawu da albashi da sauran fa’idodi da ake ba su.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Yawancin ‘yan Nijeriya sun nuna damuwa game da yadda majalisar dattawa ta 10 ke gudanar da harkokin majalisa, suna cewa ‘yan majalisar sun gaza bayar da muhimman ayyukan da aka ɗora musu na binciken ɓangaren zartarwa don kare ‘yan Nijeriya.

Ana zargin majalisa dattawa ta 10 da ƙin tilasta wa gwamnatin tarayya wurin magance tarin ƙalubale da ke fuskantar ‘yan Nijeriya, ciki har da tsadar rayuwa, talauci, yunwa, yawan rashin aikin yi da rashin tsaro, da sauran su.

Rahotanni su bayyana cewa akwai tsofaffin gwamnonin 13 da ke majalisar dattawa ta 10 a halin yanzu, wanda suka haɗa da shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio (Akwa Ibom), Aliyu Wammako (Sakkwato), Abdulaziz Yari (Zamfara), Aminu Waziri Tambuwal (Sakkwato) da Adams Oshiomhole (Edo).

Sauran sun haɗa da Ibrahim Hassan Dankwambo (Gombe), Abubakar Bello (Neja), Orji Uzor Kalu (Abiya), Seriake Dickson (Bayelsa), Adamu Aliero (Kebbi), Danjuma Goje (Gombe), Gbenga Daniel (Ogun) da Simon Lalong (Filato).

Masana sun ce daga cikin tsofaffin gwamnonin 13 da ke majalisar, Akpabio, Aliero, Dickson, Oshiomhole, Kalu, Lalong, Daniel, da Goje su ne suke taka rawar gani sosai a lokacin tattaunawan zaman majalisa.

Akwai rahotannin da ke cewa Yari, Dankwambo, Bello, Tambuwal da Wamakko ba sa yawan halartar tarurrukan majalisa ko kuma su shigo cikin muhawara idan sun bayyana. Duk da haka, akwai rahotannin da ke cewa wasu ƙananan ƙudirori ne suka gabatar a zauren majalisar.

Haka zalika, sanatoci irinsu Sahabi Yau, mai wakiltar Zamfara ta Arewa da Eze Kenneth Emeka, mai wakiltar Ebonyi ta tsakiya da Okechukwu Ezea, mai wakiltar Inugu ta Arewa da Anthony Siyako Yaro, mai wakiltar Gombe ta Kudu da Mustapha Khabeeb, mai wakiltar Jigawa ta Kudu da Rufai Hanga, mai wakiltar Kano ta tsakiyar da Binos Dauda Yaroe, mai wakiltar Adamawa ta Kudu da Benson Friday Konbowei, mai wakiltar Bayelsa ta tsakiya da Eteng Jonah Williams, mai wakiltar Kuros Ribas ta tsakiya da Adegbonmire Ayodele, mai wakiltar Ondo ta tsakiyar dukkansu ba su gabatar da wani ƙudiri ba a zauren majalisar dattawa ba har izuwa yanzu.

Haka kuma, akwai sanatoci irinsu Amos Yohanna, mai wakiltar Adamawa ta Arewa da Samaila Kaila, mai wakiltar Bauchi ta Arewa da Ani Okorie, mai wakiltar Ebonyi ta Kudu da Kelɓin Chizoba, mai wakiltar Inugu ta Gabas da Jiya Ndalikali, mai wakiltar, Neja ta Kudu da Onyesoh Allwell, mai wakiltar Ribas ta Gabas da Haruna Manu, mai wakiltar Taraba ta Tsakiya da Napoleon Bali, mai wakiltar Filato ta Kudu da Fadeyi Olubiyi, mai wakiltar Osun ta tsakiya da Shuaibu Isa Lau, mai wakiltar Taraba ta Arewa na daga cikin rukunin sanatocin da ba sa magana a zauren majalisar dattawa.

Sauran su ne Fasuyi Cyril Oluwole, mai wakiltar Ekiti ta Arewa da Osita Ngwu, mai wakiltar Inugu ta Yamma da Onyewuchi Francis, mai wakiltar Imo ta Gabas da Ahmed Madori, mai wakiltar Jigawa ta Arewa maso Gabas da Lawal Adamu Usman, mai wakiltar Kaduna ta Tsakiya da Musa Garba, mai wakiltar Kebbi ta Kudu da Sadiƙ Suleiman Umar, mai wakiltar Kwara ta Arewa da Olajide Ipinsagba, mai wakiltar Ondo ta Arewa da Yunus Akintunde, mai wakiltar Oyo ta Tsakiya da Abdulfatai Buhari, mai wakiltar Oyo ta Arewa da Mpigi Barinda, mai wakiltar Ribas ta Gabas da Babangida Husseini Uba, mai wakiltar Jigawa ta Arewa maso Yamma da Bassey Etim, mai wakiltar Akwa Ibom ta Arewa maso Gabas da Emmanuel Udende, mai wakiltar Benuwai ta Arewa maso Gabas da Godiya Akwashiki, mai wakiltar Nasarawa ta Arewa da Ikra Aliyu Bilbis, mai wakiltar Zamfara ta Tsakiya da Oyewumi Kamorudeen Olarere, mai wakiltar Osun ta Yamma.

Sanatocin
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
Siyasa

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Next Post
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.