ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

by Leadership Hausa
10 months ago
Sanatocin

Tun bayan ƙaddamar da majalisar dattawa ta 10 a ranar 13 ga Yunin 2023, majalisar na shan suka daga wasu ‘yan Nijeriya waɗanda suke ganin ta zama ‘yar amshin shatan a ɓangaren fadar shugaban ƙasa.

Masana harkokin siyasa sun yi iƙirarin cewa sabbin sanatocin yanzu suna yin aiki ne ba don cika ƙa’idoji ba, suna amincewa da ƙudirorin da ɓangaren zartarwa ya gabatar ko wasu manyan hukumomi suka yanke hukunci, maimakon shiga cikin tsarin samar da dokoki da wakilci na gaskiya da kuma gudanar da bincike da tsarin mulki ya ɗora wa majalisa.

  • Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi
  • Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Masanan sun bayyana damuwarsu kan cewa akwai rashin ‘yancin kai na gaske da kuma sake yin nazari mai zurfi ta yadda majalisar take amincewa da sakamako da aka riga aka yanke.

ADVERTISEMENT

Wasu ‘yan Nijeriya sun bayyana rashin jin daɗinsu kan cewa sama da sanatoci 40 ba sa yawan halartar taron majalisa da zaman kwamitoci ko kuma ba da gudunmawa a muhawara ake fafatawa a zauren majalisar dattawa.

Hazalika, masana harkokin siyasan sun cewa yawancin ‘yan majalisar dattawan zai yi wuya su halarci zaman majalisar tun daga ranar Talata zuwa Alhamis a kowane mako. Sun nuna matuƙar damuwa kan wannan lamari, wanda ko ma sun zo suna kasancewa masu ɗumama kujera ne kawai ba tare da gabatar da wani ƙudiri ba duk da adadin kuɗaɗen da suke karba a matsayin alawu da albashi da sauran fa’idodi da ake ba su.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Yawancin ‘yan Nijeriya sun nuna damuwa game da yadda majalisar dattawa ta 10 ke gudanar da harkokin majalisa, suna cewa ‘yan majalisar sun gaza bayar da muhimman ayyukan da aka ɗora musu na binciken ɓangaren zartarwa don kare ‘yan Nijeriya.

Ana zargin majalisa dattawa ta 10 da ƙin tilasta wa gwamnatin tarayya wurin magance tarin ƙalubale da ke fuskantar ‘yan Nijeriya, ciki har da tsadar rayuwa, talauci, yunwa, yawan rashin aikin yi da rashin tsaro, da sauran su.

Rahotanni su bayyana cewa akwai tsofaffin gwamnonin 13 da ke majalisar dattawa ta 10 a halin yanzu, wanda suka haɗa da shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio (Akwa Ibom), Aliyu Wammako (Sakkwato), Abdulaziz Yari (Zamfara), Aminu Waziri Tambuwal (Sakkwato) da Adams Oshiomhole (Edo).

Sauran sun haɗa da Ibrahim Hassan Dankwambo (Gombe), Abubakar Bello (Neja), Orji Uzor Kalu (Abiya), Seriake Dickson (Bayelsa), Adamu Aliero (Kebbi), Danjuma Goje (Gombe), Gbenga Daniel (Ogun) da Simon Lalong (Filato).

Masana sun ce daga cikin tsofaffin gwamnonin 13 da ke majalisar, Akpabio, Aliero, Dickson, Oshiomhole, Kalu, Lalong, Daniel, da Goje su ne suke taka rawar gani sosai a lokacin tattaunawan zaman majalisa.

Akwai rahotannin da ke cewa Yari, Dankwambo, Bello, Tambuwal da Wamakko ba sa yawan halartar tarurrukan majalisa ko kuma su shigo cikin muhawara idan sun bayyana. Duk da haka, akwai rahotannin da ke cewa wasu ƙananan ƙudirori ne suka gabatar a zauren majalisar.

Haka zalika, sanatoci irinsu Sahabi Yau, mai wakiltar Zamfara ta Arewa da Eze Kenneth Emeka, mai wakiltar Ebonyi ta tsakiya da Okechukwu Ezea, mai wakiltar Inugu ta Arewa da Anthony Siyako Yaro, mai wakiltar Gombe ta Kudu da Mustapha Khabeeb, mai wakiltar Jigawa ta Kudu da Rufai Hanga, mai wakiltar Kano ta tsakiyar da Binos Dauda Yaroe, mai wakiltar Adamawa ta Kudu da Benson Friday Konbowei, mai wakiltar Bayelsa ta tsakiya da Eteng Jonah Williams, mai wakiltar Kuros Ribas ta tsakiya da Adegbonmire Ayodele, mai wakiltar Ondo ta tsakiyar dukkansu ba su gabatar da wani ƙudiri ba a zauren majalisar dattawa ba har izuwa yanzu.

Haka kuma, akwai sanatoci irinsu Amos Yohanna, mai wakiltar Adamawa ta Arewa da Samaila Kaila, mai wakiltar Bauchi ta Arewa da Ani Okorie, mai wakiltar Ebonyi ta Kudu da Kelɓin Chizoba, mai wakiltar Inugu ta Gabas da Jiya Ndalikali, mai wakiltar, Neja ta Kudu da Onyesoh Allwell, mai wakiltar Ribas ta Gabas da Haruna Manu, mai wakiltar Taraba ta Tsakiya da Napoleon Bali, mai wakiltar Filato ta Kudu da Fadeyi Olubiyi, mai wakiltar Osun ta tsakiya da Shuaibu Isa Lau, mai wakiltar Taraba ta Arewa na daga cikin rukunin sanatocin da ba sa magana a zauren majalisar dattawa.

Sauran su ne Fasuyi Cyril Oluwole, mai wakiltar Ekiti ta Arewa da Osita Ngwu, mai wakiltar Inugu ta Yamma da Onyewuchi Francis, mai wakiltar Imo ta Gabas da Ahmed Madori, mai wakiltar Jigawa ta Arewa maso Gabas da Lawal Adamu Usman, mai wakiltar Kaduna ta Tsakiya da Musa Garba, mai wakiltar Kebbi ta Kudu da Sadiƙ Suleiman Umar, mai wakiltar Kwara ta Arewa da Olajide Ipinsagba, mai wakiltar Ondo ta Arewa da Yunus Akintunde, mai wakiltar Oyo ta Tsakiya da Abdulfatai Buhari, mai wakiltar Oyo ta Arewa da Mpigi Barinda, mai wakiltar Ribas ta Gabas da Babangida Husseini Uba, mai wakiltar Jigawa ta Arewa maso Yamma da Bassey Etim, mai wakiltar Akwa Ibom ta Arewa maso Gabas da Emmanuel Udende, mai wakiltar Benuwai ta Arewa maso Gabas da Godiya Akwashiki, mai wakiltar Nasarawa ta Arewa da Ikra Aliyu Bilbis, mai wakiltar Zamfara ta Tsakiya da Oyewumi Kamorudeen Olarere, mai wakiltar Osun ta Yamma.

Sanatocin
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.