• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sannu A Hankali Nijeriya Na Bankwana Da Matsalar Tsaro – Buhari

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Sannu A Hankali Nijeriya Na Bankwana Da Matsalar Tsaro – Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya shaida cewar a bisa jajircewa, sadaukarwa da kokarin dakarun sojojin Nijeriya, sannu a hankali ana ta bankwana da kalubalen tsaro kuma nan kusa kadan matsalar za ta zama tarihi.

Buhari wanda ke jawabi a lokacin da ya amshi bakwancin suke Fira Ministan Ireland, Micheal Martin a kasar Amurka, kamar yadda kakakinsa, Femi Adesina ya nakalto cikin jawabin Buhari, “A ‘yan watannin da suka gabata, da sabbin dabarun aiki na jami’an tsaron Nijeriya ana samun tagomashi sosai wajen yaki da matsalar tsaro.

  • An Nada Sanatan PDP Cikin Kwamitin Yakin Zaben Tinubu
  • Ministan Wajen Kasar Sin Ya Halarci Taron Ministocin BRICS

“Za mu ci gaba da yin aikin hadin guiwa da kasashen duniya wajen amfani da na’urorin zamani domin ganin Nijeriya ta koyi muhimman abubuwan da suka dace.”

Buhari ya fada wa Firaministan cewa, bisa annobar Korona da aka fuskanta a lokutan baya, akwai bukatar kasashen duniya su kara hada karfi da karfe waje guda domin nemo hanyoyin ci gaba, ya yi kwarin guiwar darurrusan da aka koya a lokacin annobar zai taimaka wa ‘yan Nijeriya wajen maida hankali ta fuskacin tabbatar da zaman lafiya da daurewarsa.

Ya tabbatar wa bakon nasa cewa Nijeriya za ta ci gaba da kyautata alakarta da kasar Ireland musamman a bangaren ilimi, inda ya nuna cewa ‘yan Nijeriya da dama suna karatu da aiki a can kasar don haka kyautata alakar zai kara taimakawa.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Shi kuma Mista Micheal Martin, ya shaida wa shugaban Nijeriya Buhari cewa, Ireland za ta zauna da duba hanyoyin da suka dace wajen kyautatawa da kara dankon zumunci a tsakaninta da Nijeriya.

Ya kuma nuna kwarin guiwarsa na cewa kasar tasa za ta kara fadada alakarta da Nijeriya zuwa fannonin da suka shafi kimiyya, taimaka wa Nijeriya wajen shawo kan matsalolin da suke sashin kiwon lafiya da lamuran tsaro.

Ya kara da cewa tarayyar turai da kasashen duniya yanzu haka ya kamata su sake duba wata hanyar ta daban domin samun hanyoyin samun makamashi tun da yakin Ukraine ya kawo musu cikas ta wannan fannin.

A kuma wata ganawar ta daban da firaministan Greece, Kyriakos Mitsotakis, Buhari ya nemi karin hadin guiwa da Nijeriya a fannonin ilimi, lafiya da tsaro.

Shi kuma a nasa fannin Firaministan ya nemi shugaban kasa Buhari day a samu lokaci wajen ziyartar kasar Greece kafin karewar wa’adin mulkinsa, y ace a shirye suke su fadada hanyoyin alaka tsakanin Nijeriya da kasar don kyautata harkokin da za su taimaki kasashen biyu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariDakarun SojiMatsalar TsaroNijeriya TuraiRashin Tsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin Kasar Sin Ya Nuna Adawa Game Da Tsoma Baki Cikin Harkokin Gidan Burundi Ta Fakewa Da Kare Hakkin Dan Adam

Next Post

Kasashen Sin Da Togo Sun Samu Sakamako Mai Kyau A Fannin Hadin Gwiwa

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

2 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

6 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

7 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

16 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

1 day ago
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Manyan Labarai

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

1 day ago
Next Post
Kasashen Sin Da Togo Sun Samu Sakamako Mai Kyau A Fannin Hadin Gwiwa

Kasashen Sin Da Togo Sun Samu Sakamako Mai Kyau A Fannin Hadin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Nijeriya

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

July 26, 2025
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.