• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sannu A Hankali Nijeriya Na Bankwana Da Matsalar Tsaro – Buhari

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Sannu A Hankali Nijeriya Na Bankwana Da Matsalar Tsaro – Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya shaida cewar a bisa jajircewa, sadaukarwa da kokarin dakarun sojojin Nijeriya, sannu a hankali ana ta bankwana da kalubalen tsaro kuma nan kusa kadan matsalar za ta zama tarihi.

Buhari wanda ke jawabi a lokacin da ya amshi bakwancin suke Fira Ministan Ireland, Micheal Martin a kasar Amurka, kamar yadda kakakinsa, Femi Adesina ya nakalto cikin jawabin Buhari, “A ‘yan watannin da suka gabata, da sabbin dabarun aiki na jami’an tsaron Nijeriya ana samun tagomashi sosai wajen yaki da matsalar tsaro.

  • An Nada Sanatan PDP Cikin Kwamitin Yakin Zaben Tinubu
  • Ministan Wajen Kasar Sin Ya Halarci Taron Ministocin BRICS

“Za mu ci gaba da yin aikin hadin guiwa da kasashen duniya wajen amfani da na’urorin zamani domin ganin Nijeriya ta koyi muhimman abubuwan da suka dace.”

Buhari ya fada wa Firaministan cewa, bisa annobar Korona da aka fuskanta a lokutan baya, akwai bukatar kasashen duniya su kara hada karfi da karfe waje guda domin nemo hanyoyin ci gaba, ya yi kwarin guiwar darurrusan da aka koya a lokacin annobar zai taimaka wa ‘yan Nijeriya wajen maida hankali ta fuskacin tabbatar da zaman lafiya da daurewarsa.

Ya tabbatar wa bakon nasa cewa Nijeriya za ta ci gaba da kyautata alakarta da kasar Ireland musamman a bangaren ilimi, inda ya nuna cewa ‘yan Nijeriya da dama suna karatu da aiki a can kasar don haka kyautata alakar zai kara taimakawa.

Labarai Masu Nasaba

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Shi kuma Mista Micheal Martin, ya shaida wa shugaban Nijeriya Buhari cewa, Ireland za ta zauna da duba hanyoyin da suka dace wajen kyautatawa da kara dankon zumunci a tsakaninta da Nijeriya.

Ya kuma nuna kwarin guiwarsa na cewa kasar tasa za ta kara fadada alakarta da Nijeriya zuwa fannonin da suka shafi kimiyya, taimaka wa Nijeriya wajen shawo kan matsalolin da suke sashin kiwon lafiya da lamuran tsaro.

Ya kara da cewa tarayyar turai da kasashen duniya yanzu haka ya kamata su sake duba wata hanyar ta daban domin samun hanyoyin samun makamashi tun da yakin Ukraine ya kawo musu cikas ta wannan fannin.

A kuma wata ganawar ta daban da firaministan Greece, Kyriakos Mitsotakis, Buhari ya nemi karin hadin guiwa da Nijeriya a fannonin ilimi, lafiya da tsaro.

Shi kuma a nasa fannin Firaministan ya nemi shugaban kasa Buhari day a samu lokaci wajen ziyartar kasar Greece kafin karewar wa’adin mulkinsa, y ace a shirye suke su fadada hanyoyin alaka tsakanin Nijeriya da kasar don kyautata harkokin da za su taimaki kasashen biyu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariDakarun SojiMatsalar TsaroNijeriya TuraiRashin Tsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin Kasar Sin Ya Nuna Adawa Game Da Tsoma Baki Cikin Harkokin Gidan Burundi Ta Fakewa Da Kare Hakkin Dan Adam

Next Post

Kasashen Sin Da Togo Sun Samu Sakamako Mai Kyau A Fannin Hadin Gwiwa

Related

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

8 hours ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

12 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

13 hours ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kai Ziyarar Aiki Jihar Anambra

15 hours ago
APC: Na Bar PDP Ne Domin Ci Gaba Da Amfana Da Ribar Ofishi Na – Kakakin Majalisar Edo
Manyan Labarai

APC: Na Bar PDP Ne Domin Ci Gaba Da Amfana Da Ribar Ofishi Na – Kakakin Majalisar Edo

2 days ago
Kwanaki 40: Iyalan Maharban Da Aka Kashe A Edo Na Neman A Biya Su Diyya
Manyan Labarai

Kwanaki 40: Iyalan Maharban Da Aka Kashe A Edo Na Neman A Biya Su Diyya

2 days ago
Next Post
Kasashen Sin Da Togo Sun Samu Sakamako Mai Kyau A Fannin Hadin Gwiwa

Kasashen Sin Da Togo Sun Samu Sakamako Mai Kyau A Fannin Hadin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

May 8, 2025
An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.