• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sannu A Hankali Nijeriya Na Bankwana Da Matsalar Tsaro – Buhari

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Sannu A Hankali Nijeriya Na Bankwana Da Matsalar Tsaro – Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya shaida cewar a bisa jajircewa, sadaukarwa da kokarin dakarun sojojin Nijeriya, sannu a hankali ana ta bankwana da kalubalen tsaro kuma nan kusa kadan matsalar za ta zama tarihi.

Buhari wanda ke jawabi a lokacin da ya amshi bakwancin suke Fira Ministan Ireland, Micheal Martin a kasar Amurka, kamar yadda kakakinsa, Femi Adesina ya nakalto cikin jawabin Buhari, “A ‘yan watannin da suka gabata, da sabbin dabarun aiki na jami’an tsaron Nijeriya ana samun tagomashi sosai wajen yaki da matsalar tsaro.

  • An Nada Sanatan PDP Cikin Kwamitin Yakin Zaben Tinubu
  • Ministan Wajen Kasar Sin Ya Halarci Taron Ministocin BRICS

“Za mu ci gaba da yin aikin hadin guiwa da kasashen duniya wajen amfani da na’urorin zamani domin ganin Nijeriya ta koyi muhimman abubuwan da suka dace.”

Buhari ya fada wa Firaministan cewa, bisa annobar Korona da aka fuskanta a lokutan baya, akwai bukatar kasashen duniya su kara hada karfi da karfe waje guda domin nemo hanyoyin ci gaba, ya yi kwarin guiwar darurrusan da aka koya a lokacin annobar zai taimaka wa ‘yan Nijeriya wajen maida hankali ta fuskacin tabbatar da zaman lafiya da daurewarsa.

Ya tabbatar wa bakon nasa cewa Nijeriya za ta ci gaba da kyautata alakarta da kasar Ireland musamman a bangaren ilimi, inda ya nuna cewa ‘yan Nijeriya da dama suna karatu da aiki a can kasar don haka kyautata alakar zai kara taimakawa.

Labarai Masu Nasaba

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

Shi kuma Mista Micheal Martin, ya shaida wa shugaban Nijeriya Buhari cewa, Ireland za ta zauna da duba hanyoyin da suka dace wajen kyautatawa da kara dankon zumunci a tsakaninta da Nijeriya.

Ya kuma nuna kwarin guiwarsa na cewa kasar tasa za ta kara fadada alakarta da Nijeriya zuwa fannonin da suka shafi kimiyya, taimaka wa Nijeriya wajen shawo kan matsalolin da suke sashin kiwon lafiya da lamuran tsaro.

Ya kara da cewa tarayyar turai da kasashen duniya yanzu haka ya kamata su sake duba wata hanyar ta daban domin samun hanyoyin samun makamashi tun da yakin Ukraine ya kawo musu cikas ta wannan fannin.

A kuma wata ganawar ta daban da firaministan Greece, Kyriakos Mitsotakis, Buhari ya nemi karin hadin guiwa da Nijeriya a fannonin ilimi, lafiya da tsaro.

Shi kuma a nasa fannin Firaministan ya nemi shugaban kasa Buhari day a samu lokaci wajen ziyartar kasar Greece kafin karewar wa’adin mulkinsa, y ace a shirye suke su fadada hanyoyin alaka tsakanin Nijeriya da kasar don kyautata harkokin da za su taimaki kasashen biyu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariDakarun SojiMatsalar TsaroNijeriya TuraiRashin Tsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin Kasar Sin Ya Nuna Adawa Game Da Tsoma Baki Cikin Harkokin Gidan Burundi Ta Fakewa Da Kare Hakkin Dan Adam

Next Post

Kasashen Sin Da Togo Sun Samu Sakamako Mai Kyau A Fannin Hadin Gwiwa

Related

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

32 minutes ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

2 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

5 hours ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

6 hours ago
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur
Manyan Labarai

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

7 hours ago
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya
Manyan Labarai

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

8 hours ago
Next Post
Kasashen Sin Da Togo Sun Samu Sakamako Mai Kyau A Fannin Hadin Gwiwa

Kasashen Sin Da Togo Sun Samu Sakamako Mai Kyau A Fannin Hadin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

September 12, 2025
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

September 12, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

September 12, 2025
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

September 12, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.