ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sannu A Hankali Nijeriya Na Bankwana Da Matsalar Tsaro – Buhari

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Nijeriya

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya shaida cewar a bisa jajircewa, sadaukarwa da kokarin dakarun sojojin Nijeriya, sannu a hankali ana ta bankwana da kalubalen tsaro kuma nan kusa kadan matsalar za ta zama tarihi.

Buhari wanda ke jawabi a lokacin da ya amshi bakwancin suke Fira Ministan Ireland, Micheal Martin a kasar Amurka, kamar yadda kakakinsa, Femi Adesina ya nakalto cikin jawabin Buhari, “A ‘yan watannin da suka gabata, da sabbin dabarun aiki na jami’an tsaron Nijeriya ana samun tagomashi sosai wajen yaki da matsalar tsaro.

  • An Nada Sanatan PDP Cikin Kwamitin Yakin Zaben Tinubu
  • Ministan Wajen Kasar Sin Ya Halarci Taron Ministocin BRICS

“Za mu ci gaba da yin aikin hadin guiwa da kasashen duniya wajen amfani da na’urorin zamani domin ganin Nijeriya ta koyi muhimman abubuwan da suka dace.”

ADVERTISEMENT

Buhari ya fada wa Firaministan cewa, bisa annobar Korona da aka fuskanta a lokutan baya, akwai bukatar kasashen duniya su kara hada karfi da karfe waje guda domin nemo hanyoyin ci gaba, ya yi kwarin guiwar darurrusan da aka koya a lokacin annobar zai taimaka wa ‘yan Nijeriya wajen maida hankali ta fuskacin tabbatar da zaman lafiya da daurewarsa.

Ya tabbatar wa bakon nasa cewa Nijeriya za ta ci gaba da kyautata alakarta da kasar Ireland musamman a bangaren ilimi, inda ya nuna cewa ‘yan Nijeriya da dama suna karatu da aiki a can kasar don haka kyautata alakar zai kara taimakawa.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Shi kuma Mista Micheal Martin, ya shaida wa shugaban Nijeriya Buhari cewa, Ireland za ta zauna da duba hanyoyin da suka dace wajen kyautatawa da kara dankon zumunci a tsakaninta da Nijeriya.

Ya kuma nuna kwarin guiwarsa na cewa kasar tasa za ta kara fadada alakarta da Nijeriya zuwa fannonin da suka shafi kimiyya, taimaka wa Nijeriya wajen shawo kan matsalolin da suke sashin kiwon lafiya da lamuran tsaro.

Ya kara da cewa tarayyar turai da kasashen duniya yanzu haka ya kamata su sake duba wata hanyar ta daban domin samun hanyoyin samun makamashi tun da yakin Ukraine ya kawo musu cikas ta wannan fannin.

A kuma wata ganawar ta daban da firaministan Greece, Kyriakos Mitsotakis, Buhari ya nemi karin hadin guiwa da Nijeriya a fannonin ilimi, lafiya da tsaro.

Shi kuma a nasa fannin Firaministan ya nemi shugaban kasa Buhari day a samu lokaci wajen ziyartar kasar Greece kafin karewar wa’adin mulkinsa, y ace a shirye suke su fadada hanyoyin alaka tsakanin Nijeriya da kasar don kyautata harkokin da za su taimaki kasashen biyu.

Nijeriya
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Next Post
Kasashen Sin Da Togo Sun Samu Sakamako Mai Kyau A Fannin Hadin Gwiwa

Kasashen Sin Da Togo Sun Samu Sakamako Mai Kyau A Fannin Hadin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.