ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

by El-Zaharadeen Umar
20 seconds ago
Sarakuna

Ministan Muhalli a Nijeriya Balarabe Abbas Lawal ya bayyana irin yadda sarakunan gargajiya za su bada gudunmawa wajen dakile barazanar kwararowar hamada a Nijeriya.

Ministan muhalli yana magana ne a lokacin da ya kai ziyarar ban girma fadar mai Martaba Sarkin Katsina, Alhaji Abdulmumini Kabir Usman domin neman shawarar irin ta iyaye sarakuna.

  • Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
  • An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

A cewar ministan Muhalli Hon. Balarabe Abbas sun zo Katsina ne domin gudanar da babban taron muhalli wanda aka saba shiryawa duk shekara inda a bana za a gudanar da shi a Katsina.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa wasu daga cikin jihohin arewacin Nijeriya ciki harda Katsina suna fuskantar barazanar muhalli da canjin yanayin wanda ya zama kalubalen a duniya baki daya.

Haka kuma ya kara da cewa daga cikin irin abubuwan da za su maida hankali a wannan taron na shekarar 2025 shi ne, rage sare itatuwa ba tare da an shuka wasu ba wanda ya ce hakan na taimakawa wajen gurbatar yanayi a duniya.

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

“Abinda muke so yanzu shi ne, gwamnati ta fito da wasu tsare-tsare da za su taimaka wajen rage yadda ake amfani da itatuwa wajen yin girki ba tare an shuka wasu ba da kuma irin hadarin da mata ke fuskanta a ya yin girki da itatuwa a wannan zamani.’ inji shi

Ministan Muhallin ya ce gwamnatin tarayya ta bullo da wasu sabbin shirye-shirye na maye gurbin amfani da itatuwa wajen yin girki inda za ta samar da wasu sinadarai da za a rika amfani da su don kaucewa dumamar yanayi

Haka kuma ya bayyana cewa idan ta kama sai an sare itatuwa to ana bukatar a shuka guda uku duk inda aka sare guda daya wanda haka zai taimaka wajen bunkasar yanayin mai kyau da al’umma zata amfana da shi wajen samun kyakkyawan yanayi.

Hon. Balarabe Abbas wanda ya ce duk wata nasara da ake bukata dole ne a sanya iyaye sarakuna saboda tasirin su a cikin wannan al’umma.

Da yake jawabi mai Martaba Sarkin Katsina Alhaji Abdulmumini Kabir Usman ya yi na’am da wannan taro wanda ya ce ya yi daidai da halin da al’umma suke ciki na rashin kula da muhallinsu

Sarkin na Katsina ya bada tabbacin goyon bayan masarautar da wajen ganin an cimma nasarar wannan gagarumin aiki na tabbatar da samun kyakkyawar muhalli wanda ya ce muhalli shi ne rayuwa.

Alhaji Abdulmumini Kabir Usman ya ce al’umma ta rasa wadanda za su yi masu jagoranci wajen ganin an kyautata muhallin da ke tafiyar da rayuwar al’umma a kowane lokaci da kuma zamani.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN
Labarai

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025

LABARAI MASU NASABA

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.