• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarkin Zazzau Ya Buƙaci Addu’ar Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Sarkin Zazzau Ya Buƙaci Addu’ar Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai martaba Sarkin Zazzau, Mal. Ahmed Nuhu Bamalli, ya yi kira ga al’ummar Nijeriya da su ƙara duƙufa wajen gudanar da addu’o’in neman zaman lafiya da kwanciyar hankali gami da yin addu’ar neman kawo ƙarshen matsalolin tsaro da suka addabi ƙasar nan.

Sarkin wanda ya yi wannan kiran a yayin bikin baje kolin al’adun gargajiya na shekara-shekara da Masarautar Kaltungo ta jihar Gombe ta saba shiryawa, ya kuma neman ƙarin addu’o’i wa gwamnatoci domin samun nasarar sauƙe nauyin da ke kawukansu wajen shawo kan matsalolin da ake fuskanta a ƙasar nan.

  • Tarihin Katsina Daga Karni Na Goma
  • Cire Tallafin Mai: Magani Mai Daci Ga Kashi 99 Cikin 100 Na ‘Yan Nijeriya

Nuhu Bamalli wanda shi ne uban taron, ya ce, babu wata ƙasa da za ta cigaba ba tare da zaman lafiya da kwanciyar hankali ba, don haka ne ya nemi jama’a da su kauce wa shiga dukkanin wani abun da ka iya janyo matsala ga zaman lafiyar ƙasa.

Ya kuma yaba wa Sarkin Kaltungo, Injiniya Sale Muhammadu Umar da ya kasance mai shirya taron da ke ƙara haɗa kan al’ummar masarautarsa da kuma yadda yake nuna damuwa wajen cigaban al’ummarsa haɗi da kiyaye tarihi da al’adun masarautar.

Sarkin Zazzau

Labarai Masu Nasaba

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Shi kuma a nasa jawabin, gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bada tabbacin gwamnatinsa na cigaba da kiyaye rayuka da dukiyar al’ummar jihar tare da bada gagarumin gudunmawa wajen bunqasa al’adun da jihar ke da su.

Gwamnan wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Dakta Manasseh Daniel Jatau, ya hori jama’a da a kowani lokaci su kasance masu mutunta sarakuna da al’adun gargajiya domin kyautata cigaba mai ɗaurewa.

Shi kuma a nasa ɓangaren, shugaban taro, Hon. James Joseph Damara (Kauran Kaltungo), ya gode wa irin shugabanci na kwarai da sarkin Kaltungon ke yi wajen kasancewa uba ga kowani ɗan masarautar haɗi da ‘yan uwanta da ke ƙara kyautata zaman lafiya a tsakanin al’ummar masmasarautar.

Ya ce, muhimmancin al’ada baya misaltuwa, yana mai cewa, a bisa mutunta al’ada ne manyan baƙi suka fito daga sassa daban-daban domin halartar wannan taron a Kaltungo, ya misalta sarkin garin a matsayin wani jarumin da ke da buƙarin haɗa kan jama’a da bunqasa al’adu da zaman lafiya a kowani lokaci.

A bikin dai wanda sarkin ya saba gudanarwa, ana baje kolin al’adun gargajiya da raye-raye gargajiya haɗi da baje nau’ikan kalolin abinci da ake da su a masarautar Kaltungo da ma makwafta, inda kowace ƙabila ke fitowa ta nuna asalin al’adarta da ke zama gwanin sha’awa ga mahalarta taro.

Taron wanda ake shafe kusan mako gudana a na gudanarwa, sarkin na kuma shirya taron liyafa na musamman wa ‘yan jarida da sarakuna da sauran manyan baƙi.

Sarkin Zazzau

A wajen liyafar da sarkin ya shirya wa ‘yan jarida, tsohon shugaban ƙungiyar ‘yan jarida na jihar Bauchi, Malam Ibrahim Muhammad Malamgoje, ya yi kira ga masu hannu da shuni ko gwamnati da su kafa wata gidan rediyo ko talabijin a ƙaramar hukumar Kaltungo lura da yadda sarkin ke so da qaunar ‘yan jarida haɗi da mutunta aikin nasu.

A cewar Ibrahim wanda wakilin RFI Hausa ne, a dukkanin yankin arewa babu wani sarkin da ke gayyatar ‘yan jarida daga sassa daban-daban na ƙasar nan kawai domin ya zauna da su ya shirya musu ƙasaitaccen liyafa haɗi da jinjina wa irin qoqarin da suke bayarwa wajen cigaban ƙasa.

A nasa ɓangaren, Sarkin Kaltungo, ya ce, ‘yan jarida na da muhimmiyar rawar da suke takawa wajen cigaban ƙasar nan, don haka akwai buƙatar a kasance ana jinjina wa irin ƙoƙarinsu a kowani lokaci. Kazalika ya kuma yaba wa irin ƙoƙarin jami’an tsaro su.

Ita kuma jigon taron, Hajiya Sa’adatu Saad Mustapha, ta ce, a kowani shekara ‘yan jarida sun kasance masu tallata irin al’adu da masarautar ke da su, don haka ne ta nuna ‘yan jarida a matsayin abokan jere.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KaltungoMasarautar BauchiZazzau
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masarautar Adamawa Ta Naɗa Hakimai 3 A Gundumar Ƙaramar Hukumar Hong

Next Post

Zamu Dogara Da Osimhen Don Lashe Gasar AFCON – Peseiro

Related

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

8 hours ago
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi
Labarai

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

9 hours ago
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Labarai

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

9 hours ago
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

10 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

12 hours ago
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 
Labarai

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

13 hours ago
Next Post
Zamu Dogara Da Osimhen Don Lashe Gasar AFCON – Peseiro

Zamu Dogara Da Osimhen Don Lashe Gasar AFCON - Peseiro

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.