• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarkin Zazzau Ya Buƙaci Addu’ar Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Sarkin Zazzau Ya Buƙaci Addu’ar Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai martaba Sarkin Zazzau, Mal. Ahmed Nuhu Bamalli, ya yi kira ga al’ummar Nijeriya da su ƙara duƙufa wajen gudanar da addu’o’in neman zaman lafiya da kwanciyar hankali gami da yin addu’ar neman kawo ƙarshen matsalolin tsaro da suka addabi ƙasar nan.

Sarkin wanda ya yi wannan kiran a yayin bikin baje kolin al’adun gargajiya na shekara-shekara da Masarautar Kaltungo ta jihar Gombe ta saba shiryawa, ya kuma neman ƙarin addu’o’i wa gwamnatoci domin samun nasarar sauƙe nauyin da ke kawukansu wajen shawo kan matsalolin da ake fuskanta a ƙasar nan.

  • Tarihin Katsina Daga Karni Na Goma
  • Cire Tallafin Mai: Magani Mai Daci Ga Kashi 99 Cikin 100 Na ‘Yan Nijeriya

Nuhu Bamalli wanda shi ne uban taron, ya ce, babu wata ƙasa da za ta cigaba ba tare da zaman lafiya da kwanciyar hankali ba, don haka ne ya nemi jama’a da su kauce wa shiga dukkanin wani abun da ka iya janyo matsala ga zaman lafiyar ƙasa.

Ya kuma yaba wa Sarkin Kaltungo, Injiniya Sale Muhammadu Umar da ya kasance mai shirya taron da ke ƙara haɗa kan al’ummar masarautarsa da kuma yadda yake nuna damuwa wajen cigaban al’ummarsa haɗi da kiyaye tarihi da al’adun masarautar.

Sarkin Zazzau

Labarai Masu Nasaba

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

Shi kuma a nasa jawabin, gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bada tabbacin gwamnatinsa na cigaba da kiyaye rayuka da dukiyar al’ummar jihar tare da bada gagarumin gudunmawa wajen bunqasa al’adun da jihar ke da su.

Gwamnan wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Dakta Manasseh Daniel Jatau, ya hori jama’a da a kowani lokaci su kasance masu mutunta sarakuna da al’adun gargajiya domin kyautata cigaba mai ɗaurewa.

Shi kuma a nasa ɓangaren, shugaban taro, Hon. James Joseph Damara (Kauran Kaltungo), ya gode wa irin shugabanci na kwarai da sarkin Kaltungon ke yi wajen kasancewa uba ga kowani ɗan masarautar haɗi da ‘yan uwanta da ke ƙara kyautata zaman lafiya a tsakanin al’ummar masmasarautar.

Ya ce, muhimmancin al’ada baya misaltuwa, yana mai cewa, a bisa mutunta al’ada ne manyan baƙi suka fito daga sassa daban-daban domin halartar wannan taron a Kaltungo, ya misalta sarkin garin a matsayin wani jarumin da ke da buƙarin haɗa kan jama’a da bunqasa al’adu da zaman lafiya a kowani lokaci.

A bikin dai wanda sarkin ya saba gudanarwa, ana baje kolin al’adun gargajiya da raye-raye gargajiya haɗi da baje nau’ikan kalolin abinci da ake da su a masarautar Kaltungo da ma makwafta, inda kowace ƙabila ke fitowa ta nuna asalin al’adarta da ke zama gwanin sha’awa ga mahalarta taro.

Taron wanda ake shafe kusan mako gudana a na gudanarwa, sarkin na kuma shirya taron liyafa na musamman wa ‘yan jarida da sarakuna da sauran manyan baƙi.

Sarkin Zazzau

A wajen liyafar da sarkin ya shirya wa ‘yan jarida, tsohon shugaban ƙungiyar ‘yan jarida na jihar Bauchi, Malam Ibrahim Muhammad Malamgoje, ya yi kira ga masu hannu da shuni ko gwamnati da su kafa wata gidan rediyo ko talabijin a ƙaramar hukumar Kaltungo lura da yadda sarkin ke so da qaunar ‘yan jarida haɗi da mutunta aikin nasu.

A cewar Ibrahim wanda wakilin RFI Hausa ne, a dukkanin yankin arewa babu wani sarkin da ke gayyatar ‘yan jarida daga sassa daban-daban na ƙasar nan kawai domin ya zauna da su ya shirya musu ƙasaitaccen liyafa haɗi da jinjina wa irin qoqarin da suke bayarwa wajen cigaban ƙasa.

A nasa ɓangaren, Sarkin Kaltungo, ya ce, ‘yan jarida na da muhimmiyar rawar da suke takawa wajen cigaban ƙasar nan, don haka akwai buƙatar a kasance ana jinjina wa irin ƙoƙarinsu a kowani lokaci. Kazalika ya kuma yaba wa irin ƙoƙarin jami’an tsaro su.

Ita kuma jigon taron, Hajiya Sa’adatu Saad Mustapha, ta ce, a kowani shekara ‘yan jarida sun kasance masu tallata irin al’adu da masarautar ke da su, don haka ne ta nuna ‘yan jarida a matsayin abokan jere.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KaltungoMasarautar BauchiZazzau
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masarautar Adamawa Ta Naɗa Hakimai 3 A Gundumar Ƙaramar Hukumar Hong

Next Post

Zamu Dogara Da Osimhen Don Lashe Gasar AFCON – Peseiro

Related

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

8 minutes ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

38 minutes ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

1 hour ago
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur
Manyan Labarai

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

2 hours ago
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya
Manyan Labarai

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

3 hours ago
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL
Manyan Labarai

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

5 hours ago
Next Post
Zamu Dogara Da Osimhen Don Lashe Gasar AFCON – Peseiro

Zamu Dogara Da Osimhen Don Lashe Gasar AFCON - Peseiro

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

September 12, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

September 12, 2025
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

September 12, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

September 12, 2025
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

September 12, 2025
Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

September 12, 2025
Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

September 12, 2025
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

September 12, 2025
Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

September 12, 2025
Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.