• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sauya Sheka: Jam’iyyu Na Shirin Tilasta Kafa Dokoki Masu Zafi A Kan ‘Yan Majalisa

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
jam'iyyu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Manyan jam’iyyun siyasa a Nijeriya na neman tilasta wa ‘yan majalisa na jihohi da na tarayya wajen kirkiro dokoki da za su ayyana kujerun ‘yan majalisan da suka sauya sheka bayan an zabe su a matsayin babu kowa.

Jam’iyyun sun hada da APC, PDP, LP da kuma YPP dukkansu sun yi barazanar kai karar ‘yan majalisan jihohi da na tarayya kan kawo sauyi na wannan lamari.

  • Karancin Wuta: Majalisar Dokokin Nasarawa Ta Bai Wa AEDC Makonni 2 Don Gyara Wutar Lantarki
  • Ranar Ma’aikata: Bayan Cike Giɓin Albashin Da Muka Gada, Za Mu Ci Gaba Da Inganta Walwalar Ma’aikata – Gwamnan Zamfara

Jihohin da aka samu sauya sheka na ‘yan majalisa tunn lokacin da aka rantsar da su sun hada da Anambra, Kogi, Inugu, Ribas, Yobe da kuma Kaduna, sai dai lamarin sauya sheka ya fi kamari a jam’iyyar PDP.

A zuwa yanzu dai, dan majalisar tarayya guda daya ne kacal, Sanata Ifeanyi Uba ya sauka sheka daga jam’iyyar YPP zuwa APC.

A Jihar Yobe kuwa, Hon Lawan Musa Majakura shi ne kadai dan majalisar PDP da ya sauya sheka a zauren majalisar Jihar Yobe a 2023, wanda ya ba shi damar zama shugaban majalisar jihar ba tare da wata hamayya ba.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dan majalisa mai wakiltar mazabar Yagba ta yamma a majalisar Jihar Kogi, Idowu Ibikunle,wanda aka zaba a jam’iyyar ADP, amma daga baya ya sauya sheka ya koma APC.
A Jihar Kaduna kuwa, Godfrey Ali Gaiya da ke wakiltar Zango Kataf a zauren majalisar jihar ya bar jam’iyyar PDP ya koma APC.

Bisa ga kundin tsarin mulki sashi na 109 (g) ya bayyana cewa, dan majalisa yana iya asarar kujerarsa idan har ya kasance ya sauya sheka daga jam’iyyar da aka zabe shi ya koma wata jam’iyya kafin karewar wa’adin majalisa. Idan kuma ya samu wasika daga jam’iyyarsa sakamakon yin maja na hadewar jam’iiyu biyu ko wani bangare, to babu komi a kansa.

Sauya shekan ‘yan majalisan jihohi na iya hana jam’iyyun lashe wasu mukamai kamar kujerun tarayya, ofishin gwamna ko ma na shugaban kasa.

‘Yan majalisan suna sauya shekan ne domin samun damar yin nasara a zabe mai zuwa, mafi yawancin jami’an jam’iyyu a jihohi suna fadi zabe a hannun abokan hamayya kan wannan matsala.

A cewar wasu jami’an jam’iyyu da suka tattauna da LEADERSHIP sun bukaci kotun kolli ta ayyana kujerun ‘yan majalisan da suka sauya sheka a matsayin wanda babu kowa.

Shugaban jam’iyyar LP a Jihar Inugu, Barrister Casmir Agbo ya ce za su garzaya kotu kan shugaban majalisar jihar ya ayyna kujerun ‘yan majalisa shida da aka zaba a karkashin jam’iyyar LP suka sauya sheka zuwa PDP a matsayin wadanda babu kowa.

Agbo ya bayyana haka ne lokacin da yake zantawa da LEADERSHIP a Inugu. Ya ce za su shigar da kara kan lamarin a mako mai zuwa.

Idan za a iya tunawa dai, a watan da ya gabata ne ‘yan majalisan LP su shida suka bayyana ficewa daga jam’iyyar zuwa PDP. ‘Yan majalisan sun bayyana sauya shakarsu ne a lokacin zaman majalisa.
‘Yan majalisan da suka sauya shakan sun ce sun dauki wannan matakin ne sakamakon rashin jituwa da rikici da ke cikin jam’iyyar LP a kasa da kuma dukkan jihohin Nijeriya.

“Abun takaici, jam’iyyar ta fada cikin rashin jituwa da rarrabuwar kayuna da suka kai ga kotuna tare da lalacewar ikidan mutane. A baya, jam’iyyar ta kasance tana da akidu masu kyau, amma a halin yanzu rikicin cikin gida ya sa ta samu nakasu tun bayan kammala zabe.”

Sun kara da cewa rikicin Abure da Apapa da na ma’ajin jam’iyyar na kasa sun kara haddasa rarrabuwar kawuna a jam’iyyar. Sun bayyyana fatansu cewa PDP za ta zama musu tsani da za su ci gaba da cika burikan mutane, sannan sun kuma gode wa shugabannin LP bisa goyon bayan da suka samu.

Cikin wadanda suka sauya shekan sun hada da mai tsawatarwa na majalisar jihar mai wakiltar mazabar Igboeze na arewa, Hon Ejike Eze da jagoran majalisar jihar mai wakiltar Inugu ta arewa, Hon Johnson Ugwu da dan majalisa mai wakiltar Inugu ta kudu, Hon Princess Ugwu.

Kazalika, kungiyoyin fararen hula sun shigar da kara a babban kkotun tarayya da ke Fatakwai bisa kalubalantan ‘yan majalisa 27 na PDP da suka sauya sheka zuwa APC.

Jam’iyyar PDP a Jihar Ribas ta bayyana cewa kwanan nan za ta shiga kotu na neman aiwatar da kundin tsarin mulki kan ‘yan majalisa 27 da suka sauya sheka.

Baban sakataren yada labarai na PDP,Tambari Sydney Gbara, shi ya bayyana hakan lokacin da yake zantawa da LEADERSHIP a Fatakwai. Gbara ya ce tuni aka ayyana kujerun ‘yan majalisan 27 a matsayin babu kowa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: jam'iyyun Siyasar NijeriyamajalisaSanatociSauya Sheka
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministan Wajen Hungary Na Fatan Ziyarar Xi Za Ta Bude Sabon Babi Na Dangantakar Hungary Da Sin

Next Post

Gidauniyyar TY Buratai Ta Nemi A Hukunta Shagunan ‘Yan Kasashen Waje Da Ke Nuna Wariya Ga ‘Yan Nijeriya

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 day ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

2 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

2 days ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

1 week ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

1 week ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

2 weeks ago
Next Post
Gidauniyyar TY Buratai Ta Nemi A Hukunta Shagunan ‘Yan Kasashen Waje Da Ke Nuna Wariya Ga ‘Yan Nijeriya

Gidauniyyar TY Buratai Ta Nemi A Hukunta Shagunan 'Yan Kasashen Waje Da Ke Nuna Wariya Ga 'Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.