• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

by Sulaiman and Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
HND

Masu shaidar karatun babbar difiloma ta kasa da aka fi sani da (HND)da suka yi makarantun fasaha da wasu makarantu a fadin tarayyar Njeriya suna iya rasa dama ta tafiya yiwa kasa hidima’ (NYSC) saboda sabon tsarin manufar da aka fitar ya nuna cewa dole ne sai an samu satifiket na shaidar yin sanin makamar aiki na shekara daya, kafin wadanda suka halarci irin wadancan makarantu a yarda masu su tafi yiwa kasa hidima.

 

Hukumar ta NYSC, ta kafar sadarwarta ta Facebook ta bayyana wadanda suka mallaki HND dole su nuna sheda cewa sun yi sanin makamar aiki na shekara daya kafin ayi masu rajista a wuraren da aka tura su yiwa kasa hidima.

  • Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Na Duniya Da Rahoto Gaskiya Kan Nijeriya
  • Cututtukan Da Suka Fi Addabar Kajin Gidan Gona Lokacin Damina

Sanarwar ta nuna, “Wadanda suke da babbar difiloma ta kasa (HND) ana bukatar da su nuna shedar sun kammala yin shekara daya ta sanin makamar aiki, bugu da kari tare da satifiket da sakamakon jarabawa na ND HND.”

 

LABARAI MASU NASABA

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Wannan na nuna kenan wadanda suka kammala makarantun fasaha da makamantansu wadanda za su je aikin yiwa kasa hidima na Batch B stream II,ba tare da shedar da ke nuna sun yi sanin makamar aiki na shekara daya,ba za su tafi aikin yiwa kasa hidima ba.

 

Wannan sabon tsari na nuna ba tare da satifiket mai nuna an yi aikin sanin makamar aiki na shekara daya, masu shaidar babbar difiloma ta kasa HND,ba za su samu damar yin aikin yiwa kasa hidima ba, da za a fara yin rajista ranar 28 ga Agusta 2024.

 

Binciken da LEADERSHIP ta yi ya nuna dole ne aikin sanin makamar aiki na shekara daya ne abinda ake bukata kafin amincewa tafiya yiwa kasa hidimam kamar yadda abin yake a dokar hukumar.

 

Dokar ta nuna wadanda suka kammala makarantun fasaha da makamantansu dole ne sai sun yi aikin sanin makama na shekara daya, wanda satifiket ne zai sheda cewar sun yi kafin a basu damar samun gurbi na karatun babbar difiloma, ana son makarantar ta tabbatar da hakan kafin ta bada damar yin hakan.

 

Sai dai kuma kash! Ya samu labarin yawancin makarantu amsu bada shaidar babbar difiloma ta HND basu tabbatar da hakan ba kafin su bada gurbin karatun ,yanzu sun yaye dubban dalibai wadanda yanzu suna cikin ni ‘yasu dangane zuwa yi ma kasa hidima NYSC.

 

Har ila yau binciken ya nuna shekarun baya wasu makarantun fasaha sun yi watsi da dokar,inda suka ba dalibai damar karatu ba tare da sun tabbatar da akwai satifiket na aikin sanin makama na shekara daya ba.

 

Da take bada dalili shugabar ofishin NYSC ta Jihar Legas,Yetunde Baderinwa, ta ce, “An gano bada dadewa ba wasu makarantun sun bada damar gurbin karatu, ba tare da tabbatar da bin tsarin aikin sanin makama ba na shekara daya.

 

“Dole ne sai sun yi aikin sanin makama na shekara daya tare da shedar sun yi hakan kafin a bsu damar su samu gurbin yin tsarin karatu na HND, dole ne kuma makarantun su yi hakan kafin su basu damar yin karatun na HND.”

 

Sai dai kuma wasu daga cikin wadanda suka kammala HND abin ya shafe su, sun yi roko a yi masu ahuwa suna bukatar NYSC ta shiga cikin lamarin tayi wa makarantun su magana a kyalesu , su tafi yi wa kasa hidima, domin an riga an sa su cikin Batch B Stream II.

 

Sun ce makarantu ne ke da laifi saboda sun basu damar karatu ba tare da sun tantance ko sun yi aikin sanin hidima na shekara daya ba, ko sanar da su akan bukatar da su yi hakan.

 

Yayin da suka gana da LEADERSHIP wasu daga cikinsu sun nuna rashin jin dadi, na cewar basu da satifiket mai nuna cewar sun yi aikin sanin makama na shekara daya, ballantana ace su je su yi rajistar lokacin da aka bude damar rajista ta yi wa kasa hidima a wannan watan.

 

Wadda ta kammala makarantar fasaha ta JIhar Kaduna wadda tace sunanta Hauwa, cewa ta yi ta kagara ta tafi aikin yiwa kasa hidima, bayan ita hukumar NYSC ta kira ta, wancan sanarwar ce ta bata lamarin.

 

Ta ce, “Ina mai matukar farinciki in fara in fara yi wa kasa hidima sai dai kuma damuwata it ace ba za a tantance ni ba (admitted) lokacin da za a fara ranar 28 ga watan Agusta 2024 saboda bukatar satifiket na sanin makamar aiki na shekara daya.Makaranta ta bata yi mana bayani ba mu samar da satifiket din wanda yake dole ne, tsoro na shi ne lamarin na iya sa ace ba zan tafi ba.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

gombe
Ilimi

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma
Ilimi

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
ASUU
Ilimi

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Next Post
Lokuta Da Yawa Nakan Dakata In Yi Kuka Ma’ishi Kafin Na Ci Gaba Da Rubutu – Fatima Gurin

Lokuta Da Yawa Nakan Dakata In Yi Kuka Ma'ishi Kafin Na Ci Gaba Da Rubutu – Fatima Gurin

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

October 21, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Wata Tankar Mai Ta Sake Fashewa A Neja

Da Ɗumi-ɗumi: Fashewar Tankar Man Fetur Ta Yi Ajalin Rayuka 30 A Neja

October 21, 2025
Sin Ta Bayar Da Tallafin Dala Miliyan 3.5 Ga Shirin Samar Da Abinci A Zambia

Sin Ta Bayar Da Tallafin Dala Miliyan 3.5 Ga Shirin Samar Da Abinci A Zambia

October 21, 2025
Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

October 21, 2025
An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba

An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba

October 21, 2025
Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 21, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

October 21, 2025
NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

October 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Ɗan Fashi Sanye Da Kayan NYSC A Enugu

October 21, 2025
Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.