ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Na Duniya Su Riƙa Bayar Da Rahoton Gaskiya Kan Nijeriya

by Sulaiman
2 years ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya buƙaci kafafen yaɗa labarai na ƙasa da ƙasa da su riƙa bin ƙa’idojin adalci da sahihanci a cikin rahotannin su da suka shafi Nijeriya.

 

Idris ya bayyana hakan ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin wata tawaga daga BBC a ofishin sa a ranar Alhamis.

ADVERTISEMENT
  • Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 5 Da Karbar Wadanda Suka Yi Saranda 44 A Borno
  • Al’ummar Arewa: Bango Ne Ya Tsage Kadangare Ya Samu Wurin Shiga

A wata sanarwa da Mataimakin Ministan na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai, Rabiu Ibrahim, ya fitar, an bayyana cewa ministan ya ce yayin da manufofin gwamnatin Tinubu ke ci gaba da tabbatar da ‘yancin ‘yan jarida, gwamnati na sa ran ƙungiyoyin yaɗa labaran duniya su tabbatar da gaskiya da adalci a cikin rahotonnin su.

 

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Ministan ya jaddada muhimmancin daidaito da rashin son kai wajen bayar da rahotanni, kuma ya bayyana cewa yayin da Nijeriya, kamar kowace ƙasa, take fuskantar ƙalubale, yana da matuƙar muhimmanci kafafen yaɗa labarai na duniya su ba da cikakken bayani, maimakon mayar da hankali kan abubuwa marasa kyau.

 

Ya ce, “Za mu kuma roƙe ku da ku ci gaba da daidaita labaran ku don jin ta bakin mu kan labari. Ba kawai munanan abubuwan da ke fitowa daga Nijeriya ba, akwai abubuwa masu kyau da yawa kuma na tabbata wakilan ku da ke nan sun ga cewa muna da abubuwa masu kyau da muke yi a ƙasar nan kuma akwai cigaba zuwa ga wadata da muke gani.

 

“Ina so in bayyana maku ƙudirin gwamnatin Nijeriya ga kowace ƙungiya mai tattara labarai. Ƙudurin mu shi ne cewa muna son mu kasance cikin mai da hankali da rashin son zuciya kuma cikin ‘yanci.”

 

Ministan ya tabbatar da cewa gwamnatin Nijeriya ba ta samu wani rahoto da ya shafi cin zarafin ‘yan jarida da ke aiki da kafafen yaɗa labarai na duniya a ƙasar ba.

 

Ya ce, “Manufar gwamnatin Tinubu ita ce kowace ƙungiya ta labarai tana da ‘yancin gudanar da wannan sana’a kuma ina farin ciki da ba ku kawo mana rahoton wani ma’aikacin ku ba, wanda aka ci zarafin sa ko kuma ya fuskanci matsin lamba daga gwamnatin Nijeriya ba.”

 

Idris ya yaba wa irin hazaƙar da BBC ta yi wajen mayar da ɗakin watsa labarai na Sashen Hausa daga birnin Landan zuwa Abuja, inda masu kallo da kasuwanni suke, yana mai jaddada cewa wannan gagarumin shiri ya sa aka haɗa ‘yan Nijeriya kusan 200 da ke aiki da BBC a faɗin ƙasar.

 

Ministan ya bayyana jin daɗin sa da ɗorewar amana da mutunta juna tsakanin BBC da masu saurare a Nijeriya, dangantakar da ke da ƙarfi tun kusan shekaru 60.

 

Ya ce, “Haƙiƙa al’ummar Nijeriya abokan haɗin gwiwa ne da BBC kuma wannan ƙawancen ya fara shekaru da dama da suka wuce kuma ba a daina wannan sadaukarwar da muka ji a BBC da kuma mutuntawa da amincewar mutanen mu tun shekaru biyar zuwa sittin da suka gabata.”

 

Ya jinjina wa BBC kan yadda ta fara aikin gina ƙwarewar wasu ‘yan jarida da ke aiki da ƙungiyoyin yaɗa labarai na gwamnati, ya kuma yi kira ga BBC da su yi makamancin hakan ga kafafen yaɗa labarai masu zaman kan su.

 

A nasa jawabin, Daraktan Labaran Duniya kuma Mataimakin Shugaban BBC, Mista Jonathan Munro, wanda ya zo Nijeriya a karon farko, ya ce ya yi matuƙar farin ciki da shaharar BBC a ƙasar.

 

Ya ce BBC ta faɗaɗa zuwa kafofin watsa labarai da yawa a Nijeriya kuma yanzu tana yaɗa shirye-shiryen ta a cikin harsunan Pijin da Hausa da Ibo da kuma Yarbanci domin isa ga masu sauraro daban-daban a ƙasar.

 

Mista Munro, wanda ya bayyana Nijeriya a matsayin ƙasa mai ƙarfin faɗa-a-ji a duniya, ya ce kimanin mutane miliyan 30 ne ke ziyartar sashen labarai na BBC a Nijeriya a duk mako, wanda hakan ya sa Nijeriya ta zama ta uku a duniya wajen tallata BBC bayan Amurka da Indiya.

 

Mista Munro ya samu rakiyar Shugaban Harsunan Yammacin Afirka, Ehizojie Okharadia; Shugaban Sashen Labarai na Afirka, Juliet Njeri, da Shugaban Sashen Hausa na BBC, Malam Aliyu Tanko.

Minista
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Dakatar Da Harajin Shigowa Da Abinci: Gwamnati Za Ta Yi Asarar Kudin Shiga Naira Biliyan 188.37 

Dakatar Da Harajin Shigowa Da Abinci: Gwamnati Za Ta Yi Asarar Kudin Shiga Naira Biliyan 188.37 

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.