ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

by Sulaiman and Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
HND

Masu shaidar karatun babbar difiloma ta kasa da aka fi sani da (HND)da suka yi makarantun fasaha da wasu makarantu a fadin tarayyar Njeriya suna iya rasa dama ta tafiya yiwa kasa hidima’ (NYSC) saboda sabon tsarin manufar da aka fitar ya nuna cewa dole ne sai an samu satifiket na shaidar yin sanin makamar aiki na shekara daya, kafin wadanda suka halarci irin wadancan makarantu a yarda masu su tafi yiwa kasa hidima.

 

Hukumar ta NYSC, ta kafar sadarwarta ta Facebook ta bayyana wadanda suka mallaki HND dole su nuna sheda cewa sun yi sanin makamar aiki na shekara daya kafin ayi masu rajista a wuraren da aka tura su yiwa kasa hidima.

ADVERTISEMENT
  • Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Na Duniya Da Rahoto Gaskiya Kan Nijeriya
  • Cututtukan Da Suka Fi Addabar Kajin Gidan Gona Lokacin Damina

Sanarwar ta nuna, “Wadanda suke da babbar difiloma ta kasa (HND) ana bukatar da su nuna shedar sun kammala yin shekara daya ta sanin makamar aiki, bugu da kari tare da satifiket da sakamakon jarabawa na ND HND.”

 

LABARAI MASU NASABA

An Tantance Masu Neman Aikin Koyarwa 500 A Jigawa

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Amincewar Guraben Karatu Zuwa 30 Satumba

Wannan na nuna kenan wadanda suka kammala makarantun fasaha da makamantansu wadanda za su je aikin yiwa kasa hidima na Batch B stream II,ba tare da shedar da ke nuna sun yi sanin makamar aiki na shekara daya,ba za su tafi aikin yiwa kasa hidima ba.

 

Wannan sabon tsari na nuna ba tare da satifiket mai nuna an yi aikin sanin makamar aiki na shekara daya, masu shaidar babbar difiloma ta kasa HND,ba za su samu damar yin aikin yiwa kasa hidima ba, da za a fara yin rajista ranar 28 ga Agusta 2024.

 

Binciken da LEADERSHIP ta yi ya nuna dole ne aikin sanin makamar aiki na shekara daya ne abinda ake bukata kafin amincewa tafiya yiwa kasa hidimam kamar yadda abin yake a dokar hukumar.

 

Dokar ta nuna wadanda suka kammala makarantun fasaha da makamantansu dole ne sai sun yi aikin sanin makama na shekara daya, wanda satifiket ne zai sheda cewar sun yi kafin a basu damar samun gurbi na karatun babbar difiloma, ana son makarantar ta tabbatar da hakan kafin ta bada damar yin hakan.

 

Sai dai kuma kash! Ya samu labarin yawancin makarantu amsu bada shaidar babbar difiloma ta HND basu tabbatar da hakan ba kafin su bada gurbin karatun ,yanzu sun yaye dubban dalibai wadanda yanzu suna cikin ni ‘yasu dangane zuwa yi ma kasa hidima NYSC.

 

Har ila yau binciken ya nuna shekarun baya wasu makarantun fasaha sun yi watsi da dokar,inda suka ba dalibai damar karatu ba tare da sun tabbatar da akwai satifiket na aikin sanin makama na shekara daya ba.

 

Da take bada dalili shugabar ofishin NYSC ta Jihar Legas,Yetunde Baderinwa, ta ce, “An gano bada dadewa ba wasu makarantun sun bada damar gurbin karatu, ba tare da tabbatar da bin tsarin aikin sanin makama ba na shekara daya.

 

“Dole ne sai sun yi aikin sanin makama na shekara daya tare da shedar sun yi hakan kafin a bsu damar su samu gurbin yin tsarin karatu na HND, dole ne kuma makarantun su yi hakan kafin su basu damar yin karatun na HND.”

 

Sai dai kuma wasu daga cikin wadanda suka kammala HND abin ya shafe su, sun yi roko a yi masu ahuwa suna bukatar NYSC ta shiga cikin lamarin tayi wa makarantun su magana a kyalesu , su tafi yi wa kasa hidima, domin an riga an sa su cikin Batch B Stream II.

 

Sun ce makarantu ne ke da laifi saboda sun basu damar karatu ba tare da sun tantance ko sun yi aikin sanin hidima na shekara daya ba, ko sanar da su akan bukatar da su yi hakan.

 

Yayin da suka gana da LEADERSHIP wasu daga cikinsu sun nuna rashin jin dadi, na cewar basu da satifiket mai nuna cewar sun yi aikin sanin makama na shekara daya, ballantana ace su je su yi rajistar lokacin da aka bude damar rajista ta yi wa kasa hidima a wannan watan.

 

Wadda ta kammala makarantar fasaha ta JIhar Kaduna wadda tace sunanta Hauwa, cewa ta yi ta kagara ta tafi aikin yiwa kasa hidima, bayan ita hukumar NYSC ta kira ta, wancan sanarwar ce ta bata lamarin.

 

Ta ce, “Ina mai matukar farinciki in fara in fara yi wa kasa hidima sai dai kuma damuwata it ace ba za a tantance ni ba (admitted) lokacin da za a fara ranar 28 ga watan Agusta 2024 saboda bukatar satifiket na sanin makamar aiki na shekara daya.Makaranta ta bata yi mana bayani ba mu samar da satifiket din wanda yake dole ne, tsoro na shi ne lamarin na iya sa ace ba zan tafi ba.

 

HND
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
HND
Idris Aliyu Daudawa
+ posts Bio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Rayuwar Galadiman Kano Alhaji Tijjani Hashim (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kyamar Baƙi: An Sake Kwaso Ƴan Nijeriya 83 Daga Afirka Ta Kudu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 60 Da Kayan Aiki A Edo
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tsohon Shugaban Ƙasa Jonathan Ya Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Ƙasa 18 A Jihar Bauchi

MASU ALAKA

HND
Ilimi

An Tantance Masu Neman Aikin Koyarwa 500 A Jigawa

August 31, 2026
HND
Ilimi

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Amincewar Guraben Karatu Zuwa 30 Satumba

August 29, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Ilimi

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
Next Post
Lokuta Da Yawa Nakan Dakata In Yi Kuka Ma’ishi Kafin Na Ci Gaba Da Rubutu – Fatima Gurin

Lokuta Da Yawa Nakan Dakata In Yi Kuka Ma'ishi Kafin Na Ci Gaba Da Rubutu – Fatima Gurin

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.