• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

SERAP Ta Maka Tinubu A Kotu Kan Haramta Wa ‘Yan Jarida 25 Dauko Rahotonni A Fadar Shugaban Kasa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Serap
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata kungiya mai fafukatar yaki da cin hanci a Nijeriya (SERAP) ta maka gwamnatin shugahan kasa Bola Ahmed Tinubu a kotu bisa abin da ta kira “Haramtaccen hanawa da dakatar da ‘yan jarida 25 da aka tantance daukowa da yada labarai daga fadar shugahan kasa.”

A cewar rahotonni, gwamnatin tarayya a ranar 18 ga watan Agustan 2023 ta janye izinin tantancewa da sahalewar ‘tags’ da ke bai wa ‘yan jarida 25 da gidajen yada labarai damar shiga fadar shugaban kasa domin dauko rahotonnin abubuwan da ke faruwa a fadar shugaban kasa, Abuja.

  • Gwamnatin Zamfara Ta Rufe Wasu Kasuwannin Shanu A Jihar

An shaida wa ‘yan jaridan da lamarin ya shafa da su mika shaidar izinin shiga da aka basu ‘tags’ a mashigar babbar kofar fadar shugaban kasa.

Sai dai, SERAP ta ce haramcin ya saba da doka kuma bai dace ba kwata-kwata.

A kara mai lambar alama (FHC/L/CS/1766/23) da SERAP ta shigar a gaban babban kotun tarayya da ke Legas, ta roki, “Kotu da ta bada umarni da tilasta wa shugaban kasa Bola Tinubu janye haramta wa ‘yan jarida 25 da gidajen watsa labarai daga dauka da yada harkokin da suke faruwa a Villa.”

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

Kazalika, SERAP ta roki kotun da ta hana shugaba Tinubu, kowace hukuma, wani ko wasu daga janye izinin shiga fadar shugaban kasa ga ‘yan jarida masu farauto labarai ba tare da dalili na doka ba domin kauce wa tauye hakkin fadin albarkacin baki, take hakkin samun bayanai da kuma tauye wa gidajen jaridu hakkinsu.

A cewar SERAP idan har ba a tilasta wa gwamnatin janye wannan matakin nata ba, akwai yiyuwar hakan ya bude ma wasu dama su dukufa tauye hakkin samun bayanai, kasancewa cikin lamura da ‘yancin gidajen yada labarai.

Lauyoyi Ebun-Olu Adegboruwa (SAN), Kolawole Oluwadare, da Ms Valentina Adegoke, su ne suka shigar da karar a madadin SERAP, kungiyar ta ce, ‘yan jarida na taka muhimmiyar rawa don haka da bukatar su samu cikakken damar samun bayanai domin kyautata demukuradiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Fadar Shugaban KasaVilla
ShareTweetSendShare
Previous Post

Menene Sabon Karfin Ingizawa Zai Kawowa Duniya

Next Post

Ronaldo Ya Ci Kwallo Ta 850 A Tarihin Kwallonsa

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

5 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

6 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

15 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

17 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

18 hours ago
Next Post
Ronaldo Ya Ci Kwallo Ta 850 A Tarihin Kwallonsa

Ronaldo Ya Ci Kwallo Ta 850 A Tarihin Kwallonsa

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.