• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

SERAP Ta Maka Tinubu A Kotu Kan Haramta Wa ‘Yan Jarida 25 Dauko Rahotonni A Fadar Shugaban Kasa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Serap
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata kungiya mai fafukatar yaki da cin hanci a Nijeriya (SERAP) ta maka gwamnatin shugahan kasa Bola Ahmed Tinubu a kotu bisa abin da ta kira “Haramtaccen hanawa da dakatar da ‘yan jarida 25 da aka tantance daukowa da yada labarai daga fadar shugahan kasa.”

A cewar rahotonni, gwamnatin tarayya a ranar 18 ga watan Agustan 2023 ta janye izinin tantancewa da sahalewar ‘tags’ da ke bai wa ‘yan jarida 25 da gidajen yada labarai damar shiga fadar shugaban kasa domin dauko rahotonnin abubuwan da ke faruwa a fadar shugaban kasa, Abuja.

  • Gwamnatin Zamfara Ta Rufe Wasu Kasuwannin Shanu A Jihar

An shaida wa ‘yan jaridan da lamarin ya shafa da su mika shaidar izinin shiga da aka basu ‘tags’ a mashigar babbar kofar fadar shugaban kasa.

Sai dai, SERAP ta ce haramcin ya saba da doka kuma bai dace ba kwata-kwata.

A kara mai lambar alama (FHC/L/CS/1766/23) da SERAP ta shigar a gaban babban kotun tarayya da ke Legas, ta roki, “Kotu da ta bada umarni da tilasta wa shugaban kasa Bola Tinubu janye haramta wa ‘yan jarida 25 da gidajen watsa labarai daga dauka da yada harkokin da suke faruwa a Villa.”

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

Kazalika, SERAP ta roki kotun da ta hana shugaba Tinubu, kowace hukuma, wani ko wasu daga janye izinin shiga fadar shugaban kasa ga ‘yan jarida masu farauto labarai ba tare da dalili na doka ba domin kauce wa tauye hakkin fadin albarkacin baki, take hakkin samun bayanai da kuma tauye wa gidajen jaridu hakkinsu.

A cewar SERAP idan har ba a tilasta wa gwamnatin janye wannan matakin nata ba, akwai yiyuwar hakan ya bude ma wasu dama su dukufa tauye hakkin samun bayanai, kasancewa cikin lamura da ‘yancin gidajen yada labarai.

Lauyoyi Ebun-Olu Adegboruwa (SAN), Kolawole Oluwadare, da Ms Valentina Adegoke, su ne suka shigar da karar a madadin SERAP, kungiyar ta ce, ‘yan jarida na taka muhimmiyar rawa don haka da bukatar su samu cikakken damar samun bayanai domin kyautata demukuradiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Fadar Shugaban KasaVilla
ShareTweetSendShare
Previous Post

Menene Sabon Karfin Ingizawa Zai Kawowa Duniya

Next Post

Ronaldo Ya Ci Kwallo Ta 850 A Tarihin Kwallonsa

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

46 minutes ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

3 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

5 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

7 hours ago
‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki
Labarai

‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

8 hours ago
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

9 hours ago
Next Post
Ronaldo Ya Ci Kwallo Ta 850 A Tarihin Kwallonsa

Ronaldo Ya Ci Kwallo Ta 850 A Tarihin Kwallonsa

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Serap

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

July 26, 2025
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.