• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shan Rubutu Yayin Nakuda Ne Ke Haifar Da Mutuwar Masu Ciki — Likita

bySalim Sani Shehu
2 years ago
Rubutu

Kasashe masu tasowa na fama da yawan mace-macen mata masu juna biyu da jariran da ake haifa saboda yawan matsaloli da ake samu tun daga rainon ciki har zuwa haihuwa. 

Wasu na rasa rayukansu saboda sakaci na iyalansu, wasu kuma na rasa rayukansu ne saboda sakaci irin na likitoci da ungozoma a asibitoci.

  • NRC Ta Dakatar Ma’aikacinta Kan Karbar Kudin Fasinja Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Yadda Barakar PSG Ta Sake Fitowa Fili

Dokta Abdulsalam Muhammad, kwararren likita ne da ke kula da mata masu juna biyu a Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano (AKTH), ya bayyana wasu abubuwa da ke haddasa yawan mace-macen da kuma wasu wahalhalu da sauran hanyoyi da masu juna biyu ke jikkata.

Likitan ya fara bayani ne kan yadda ciki yake da kuma lokacin da yake kai wa har zuwa lokacin haihuwa ko kuma nakuda.

Daga ciki akwai batun karbo rubutu da ya yi, wanda ya bayyana cewa sun yi bincike kan lamarin kuma sun samo sakamako.

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Matsalar Tasgadewar Kashin Baya

“Mun lura yanzu ana samun matsala idan aka kawo mace haihuwa, ko da kuwa tana zuwa asibiti kuma tana bin duk dokokin da aka gindaya mata, amma kuma daga baya za a samu matasala lokacin da nakudar tai nisa ko kuma bayan ta haihu.

“Daga cikin abin da muka lura shi ne duk wata mata da aka kawota asibiti kuma tai amfani da wani ruwa, wanda suka bayyana da cewa rubutu ne, to sai ta samu wannan matsala.

“Ko dai matsalar yawan zubar jini, ko kuma rubewar mahaifa ko kuma ma rasa rai a tsakanin mai juna biyu da kuma jaririn da aka haifa.”

Wadannan matsaloli da ya ambata dai su ne kanwa uwar gamin da ake ganin su ne suka fi bayar da matsala ga mata a kasashen da suke tasowa, saboda karancin wayewar harkar kiwon lafiya ko kuma sakaci dangane da yadda asibitin yake.

“Daga karshe bincikenmu ya gano cewa wannan rubutun da mata suke amfani da shi lokacin da suka fara nakuda ko kuma dab da haihuwa ba rubutu ba ne! Wata kwayar magani ce da ake kira da ‘Misoprostol’ wadda ake amfani da ita a asibiti yayin da mace ta kasa haihuwa da kanta, kuma ana sa rai za ta iya haihuwar ba tare da an mata aiki ba”, in ji Dokta Labaran.

Har wa yau, ya yi tsokaci kan wannan magani da ake cewa rubutu ne a cikin shirin ‘Barka da Hantsi’ na gidan rediyon Freedom da ke Kano.

“Maganin yana da nauyi Miligiram 200, kuma idan za mu yi amfani da wannan maganin muna raba shi hudu ne, sai mu saka wa mace maganin a kasanta, ba ta baki ake ba da shi ba, sai bayan awa shida idan an duba yanayin ta dana jaririn sai a sake saka mata shi.

“To amma mu mun gano cewa masu ba da wannan maganin da sunan rubutu, suna hada kamar kwaya guda 50 ne sai su jika a botiki, sannan sai su zuba a kananan robobi su ringa siyarwa da sunan rubutu.”

Duba mara lafiya da bayar da magani a Nijeriya ba tare da zuwa wajen kwararru ba ya zama ruwan dare, wanda kuma masana lafiya ke alakanta hakan da barkewar cuttutuka a tsakanin al’umma ba tare da sun farga ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?
Kiwon Lafiya

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
Matsalar Tasgadewar Kashin Baya
Kiwon Lafiya

Matsalar Tasgadewar Kashin Baya

September 27, 2025
Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja
Kiwon Lafiya

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

September 8, 2025
Next Post
Kotun Ta Tabbatar Da Zaben Gwamna Nasiru A Kebbi

Kotun Ta Tabbatar Da Zaben Gwamna Nasiru A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version