• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shan Rubutu Yayin Nakuda Ne Ke Haifar Da Mutuwar Masu Ciki — Likita

by Salim Sani Shehu
2 years ago
in Kiwon Lafiya
0
Shan Rubutu Yayin Nakuda Ne Ke Haifar Da Mutuwar Masu Ciki — Likita
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasashe masu tasowa na fama da yawan mace-macen mata masu juna biyu da jariran da ake haifa saboda yawan matsaloli da ake samu tun daga rainon ciki har zuwa haihuwa. 

Wasu na rasa rayukansu saboda sakaci na iyalansu, wasu kuma na rasa rayukansu ne saboda sakaci irin na likitoci da ungozoma a asibitoci.

  • NRC Ta Dakatar Ma’aikacinta Kan Karbar Kudin Fasinja Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Yadda Barakar PSG Ta Sake Fitowa Fili

Dokta Abdulsalam Muhammad, kwararren likita ne da ke kula da mata masu juna biyu a Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano (AKTH), ya bayyana wasu abubuwa da ke haddasa yawan mace-macen da kuma wasu wahalhalu da sauran hanyoyi da masu juna biyu ke jikkata.

Likitan ya fara bayani ne kan yadda ciki yake da kuma lokacin da yake kai wa har zuwa lokacin haihuwa ko kuma nakuda.

Daga ciki akwai batun karbo rubutu da ya yi, wanda ya bayyana cewa sun yi bincike kan lamarin kuma sun samo sakamako.

Labarai Masu Nasaba

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

“Mun lura yanzu ana samun matsala idan aka kawo mace haihuwa, ko da kuwa tana zuwa asibiti kuma tana bin duk dokokin da aka gindaya mata, amma kuma daga baya za a samu matasala lokacin da nakudar tai nisa ko kuma bayan ta haihu.

“Daga cikin abin da muka lura shi ne duk wata mata da aka kawota asibiti kuma tai amfani da wani ruwa, wanda suka bayyana da cewa rubutu ne, to sai ta samu wannan matsala.

“Ko dai matsalar yawan zubar jini, ko kuma rubewar mahaifa ko kuma ma rasa rai a tsakanin mai juna biyu da kuma jaririn da aka haifa.”

Wadannan matsaloli da ya ambata dai su ne kanwa uwar gamin da ake ganin su ne suka fi bayar da matsala ga mata a kasashen da suke tasowa, saboda karancin wayewar harkar kiwon lafiya ko kuma sakaci dangane da yadda asibitin yake.

“Daga karshe bincikenmu ya gano cewa wannan rubutun da mata suke amfani da shi lokacin da suka fara nakuda ko kuma dab da haihuwa ba rubutu ba ne! Wata kwayar magani ce da ake kira da ‘Misoprostol’ wadda ake amfani da ita a asibiti yayin da mace ta kasa haihuwa da kanta, kuma ana sa rai za ta iya haihuwar ba tare da an mata aiki ba”, in ji Dokta Labaran.

Har wa yau, ya yi tsokaci kan wannan magani da ake cewa rubutu ne a cikin shirin ‘Barka da Hantsi’ na gidan rediyon Freedom da ke Kano.

“Maganin yana da nauyi Miligiram 200, kuma idan za mu yi amfani da wannan maganin muna raba shi hudu ne, sai mu saka wa mace maganin a kasanta, ba ta baki ake ba da shi ba, sai bayan awa shida idan an duba yanayin ta dana jaririn sai a sake saka mata shi.

“To amma mu mun gano cewa masu ba da wannan maganin da sunan rubutu, suna hada kamar kwaya guda 50 ne sai su jika a botiki, sannan sai su zuba a kananan robobi su ringa siyarwa da sunan rubutu.”

Duba mara lafiya da bayar da magani a Nijeriya ba tare da zuwa wajen kwararru ba ya zama ruwan dare, wanda kuma masana lafiya ke alakanta hakan da barkewar cuttutuka a tsakanin al’umma ba tare da sun farga ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AKTHLikitaMasu CikiNakudaRubutu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Atiku Zai Yi Jawabi Kan Shaidar Karatun Tinubu Ta Jami’ar Chicago

Next Post

Kotun Ta Tabbatar Da Zaben Gwamna Nasiru A Kebbi

Related

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja
Kiwon Lafiya

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

1 week ago
Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi
Kiwon Lafiya

Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

1 week ago
Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa
Kiwon Lafiya

Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa

3 weeks ago
Matsalar Gishiri Ga Lafiyar Zuciya
Kiwon Lafiya

Matsalar Gishiri Ga Lafiyar Zuciya

1 month ago
Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu
Kiwon Lafiya

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

1 month ago
Nijeriya Na Asarar Kusan Naira Tiriliyan 17.9 Duk Shekara Sakamakon Cutar Hanta — Gwamnati
Kiwon Lafiya

Nijeriya Na Asarar Kusan Naira Tiriliyan 17.9 Duk Shekara Sakamakon Cutar Hanta — Gwamnati

2 months ago
Next Post
Kotun Ta Tabbatar Da Zaben Gwamna Nasiru A Kebbi

Kotun Ta Tabbatar Da Zaben Gwamna Nasiru A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.