ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shan Rubutu Yayin Nakuda Ne Ke Haifar Da Mutuwar Masu Ciki — Likita

by Salim Sani Shehu
3 years ago
Rubutu

Kasashe masu tasowa na fama da yawan mace-macen mata masu juna biyu da jariran da ake haifa saboda yawan matsaloli da ake samu tun daga rainon ciki har zuwa haihuwa. 

Wasu na rasa rayukansu saboda sakaci na iyalansu, wasu kuma na rasa rayukansu ne saboda sakaci irin na likitoci da ungozoma a asibitoci.

  • NRC Ta Dakatar Ma’aikacinta Kan Karbar Kudin Fasinja Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Yadda Barakar PSG Ta Sake Fitowa Fili

Dokta Abdulsalam Muhammad, kwararren likita ne da ke kula da mata masu juna biyu a Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano (AKTH), ya bayyana wasu abubuwa da ke haddasa yawan mace-macen da kuma wasu wahalhalu da sauran hanyoyi da masu juna biyu ke jikkata.

ADVERTISEMENT

Likitan ya fara bayani ne kan yadda ciki yake da kuma lokacin da yake kai wa har zuwa lokacin haihuwa ko kuma nakuda.

Daga ciki akwai batun karbo rubutu da ya yi, wanda ya bayyana cewa sun yi bincike kan lamarin kuma sun samo sakamako.

LABARAI MASU NASABA

Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

“Mun lura yanzu ana samun matsala idan aka kawo mace haihuwa, ko da kuwa tana zuwa asibiti kuma tana bin duk dokokin da aka gindaya mata, amma kuma daga baya za a samu matasala lokacin da nakudar tai nisa ko kuma bayan ta haihu.

“Daga cikin abin da muka lura shi ne duk wata mata da aka kawota asibiti kuma tai amfani da wani ruwa, wanda suka bayyana da cewa rubutu ne, to sai ta samu wannan matsala.

“Ko dai matsalar yawan zubar jini, ko kuma rubewar mahaifa ko kuma ma rasa rai a tsakanin mai juna biyu da kuma jaririn da aka haifa.”

Wadannan matsaloli da ya ambata dai su ne kanwa uwar gamin da ake ganin su ne suka fi bayar da matsala ga mata a kasashen da suke tasowa, saboda karancin wayewar harkar kiwon lafiya ko kuma sakaci dangane da yadda asibitin yake.

“Daga karshe bincikenmu ya gano cewa wannan rubutun da mata suke amfani da shi lokacin da suka fara nakuda ko kuma dab da haihuwa ba rubutu ba ne! Wata kwayar magani ce da ake kira da ‘Misoprostol’ wadda ake amfani da ita a asibiti yayin da mace ta kasa haihuwa da kanta, kuma ana sa rai za ta iya haihuwar ba tare da an mata aiki ba”, in ji Dokta Labaran.

Har wa yau, ya yi tsokaci kan wannan magani da ake cewa rubutu ne a cikin shirin ‘Barka da Hantsi’ na gidan rediyon Freedom da ke Kano.

“Maganin yana da nauyi Miligiram 200, kuma idan za mu yi amfani da wannan maganin muna raba shi hudu ne, sai mu saka wa mace maganin a kasanta, ba ta baki ake ba da shi ba, sai bayan awa shida idan an duba yanayin ta dana jaririn sai a sake saka mata shi.

“To amma mu mun gano cewa masu ba da wannan maganin da sunan rubutu, suna hada kamar kwaya guda 50 ne sai su jika a botiki, sannan sai su zuba a kananan robobi su ringa siyarwa da sunan rubutu.”

Duba mara lafiya da bayar da magani a Nijeriya ba tare da zuwa wajen kwararru ba ya zama ruwan dare, wanda kuma masana lafiya ke alakanta hakan da barkewar cuttutuka a tsakanin al’umma ba tare da sun farga ba.

Rubutu
Salim Sani Shehu
+ postsBio
  • Salim Sani Shehu
    https://hausa.leadership.ng/author/salim-sani-shehu/
    Gwamnan Kwara Ya Yi Tankaɗe Da Rairaye, Ya Kori Hadimansa
  • Salim Sani Shehu
    https://hausa.leadership.ng/author/salim-sani-shehu/
    Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda, Sun Ƙwato Makamai Da Abubuwan Fashewa
  • Salim Sani Shehu
    https://hausa.leadership.ng/author/salim-sani-shehu/
    Gwamnatin Jigawa Ta Bayar Da Umarnin Bincikar Tsohon Gwamnan Jihar Badaru
  • Salim Sani Shehu
    https://hausa.leadership.ng/author/salim-sani-shehu/
    An Sake Samun Ɓullar Cutar Korona A Nijeriya

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Kiwon Lafiya

Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina

July 11, 2026
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
Kiwon Lafiya

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

June 20, 2026
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
Kiwon Lafiya

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Next Post
Kotun Ta Tabbatar Da Zaben Gwamna Nasiru A Kebbi

Kotun Ta Tabbatar Da Zaben Gwamna Nasiru A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.