ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shan Rubutu Yayin Nakuda Ne Ke Haifar Da Mutuwar Masu Ciki — Likita

by Salim Sani Shehu
3 years ago
Rubutu

Kasashe masu tasowa na fama da yawan mace-macen mata masu juna biyu da jariran da ake haifa saboda yawan matsaloli da ake samu tun daga rainon ciki har zuwa haihuwa. 

Wasu na rasa rayukansu saboda sakaci na iyalansu, wasu kuma na rasa rayukansu ne saboda sakaci irin na likitoci da ungozoma a asibitoci.

  • NRC Ta Dakatar Ma’aikacinta Kan Karbar Kudin Fasinja Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Yadda Barakar PSG Ta Sake Fitowa Fili

Dokta Abdulsalam Muhammad, kwararren likita ne da ke kula da mata masu juna biyu a Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano (AKTH), ya bayyana wasu abubuwa da ke haddasa yawan mace-macen da kuma wasu wahalhalu da sauran hanyoyi da masu juna biyu ke jikkata.

ADVERTISEMENT

Likitan ya fara bayani ne kan yadda ciki yake da kuma lokacin da yake kai wa har zuwa lokacin haihuwa ko kuma nakuda.

Daga ciki akwai batun karbo rubutu da ya yi, wanda ya bayyana cewa sun yi bincike kan lamarin kuma sun samo sakamako.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida

“Mun lura yanzu ana samun matsala idan aka kawo mace haihuwa, ko da kuwa tana zuwa asibiti kuma tana bin duk dokokin da aka gindaya mata, amma kuma daga baya za a samu matasala lokacin da nakudar tai nisa ko kuma bayan ta haihu.

“Daga cikin abin da muka lura shi ne duk wata mata da aka kawota asibiti kuma tai amfani da wani ruwa, wanda suka bayyana da cewa rubutu ne, to sai ta samu wannan matsala.

“Ko dai matsalar yawan zubar jini, ko kuma rubewar mahaifa ko kuma ma rasa rai a tsakanin mai juna biyu da kuma jaririn da aka haifa.”

Wadannan matsaloli da ya ambata dai su ne kanwa uwar gamin da ake ganin su ne suka fi bayar da matsala ga mata a kasashen da suke tasowa, saboda karancin wayewar harkar kiwon lafiya ko kuma sakaci dangane da yadda asibitin yake.

“Daga karshe bincikenmu ya gano cewa wannan rubutun da mata suke amfani da shi lokacin da suka fara nakuda ko kuma dab da haihuwa ba rubutu ba ne! Wata kwayar magani ce da ake kira da ‘Misoprostol’ wadda ake amfani da ita a asibiti yayin da mace ta kasa haihuwa da kanta, kuma ana sa rai za ta iya haihuwar ba tare da an mata aiki ba”, in ji Dokta Labaran.

Har wa yau, ya yi tsokaci kan wannan magani da ake cewa rubutu ne a cikin shirin ‘Barka da Hantsi’ na gidan rediyon Freedom da ke Kano.

“Maganin yana da nauyi Miligiram 200, kuma idan za mu yi amfani da wannan maganin muna raba shi hudu ne, sai mu saka wa mace maganin a kasanta, ba ta baki ake ba da shi ba, sai bayan awa shida idan an duba yanayin ta dana jaririn sai a sake saka mata shi.

“To amma mu mun gano cewa masu ba da wannan maganin da sunan rubutu, suna hada kamar kwaya guda 50 ne sai su jika a botiki, sannan sai su zuba a kananan robobi su ringa siyarwa da sunan rubutu.”

Duba mara lafiya da bayar da magani a Nijeriya ba tare da zuwa wajen kwararru ba ya zama ruwan dare, wanda kuma masana lafiya ke alakanta hakan da barkewar cuttutuka a tsakanin al’umma ba tare da sun farga ba.

Rubutu
Salim Sani Shehu
+ postsBio
  • Salim Sani Shehu
    https://hausa.leadership.ng/author/salim-sani-shehu/
    Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda, Sun Ƙwato Makamai Da Abubuwan Fashewa
  • Salim Sani Shehu
    https://hausa.leadership.ng/author/salim-sani-shehu/
    Gwamnatin Jigawa Ta Bayar Da Umarnin Bincikar Tsohon Gwamnan Jihar Badaru
  • Salim Sani Shehu
    https://hausa.leadership.ng/author/salim-sani-shehu/
    An Sake Samun Ɓullar Cutar Korona A Nijeriya
  • Salim Sani Shehu
    https://hausa.leadership.ng/author/salim-sani-shehu/
    Ƙarin Farashin Man Fetur: TUC Ta Shawarci Gwamnati Ta Tallafawa Matatun Mai Na Cikin Gida

MASU ALAKA

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir
Kiwon Lafiya

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

May 30, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Kiwon Lafiya

Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida

May 23, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Yi Wa Mutane 6,842 Tiyata Kyauta A Kashi 17 Na Shirin Tallafin Lafiya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Yi Wa Mutane 6,842 Tiyata Kyauta A Kashi 17 Na Shirin Tallafin Lafiya

May 21, 2026
Next Post
Kotun Ta Tabbatar Da Zaben Gwamna Nasiru A Kebbi

Kotun Ta Tabbatar Da Zaben Gwamna Nasiru A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.