• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Burin Kasar Sin Na Samun Bunkasar GDP Da Kashi 5% A Bana Zai Cika

by yahuzajere
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sharhi: Burin Kasar Sin Na Samun Bunkasar GDP Da Kashi 5% A Bana Zai Cika
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masu zantukan hikima kan ce “da icce mai kama ake kota”, tabbas haka ne, domin duk lokacin da wata kasa ta tasa wani buri a gaba, a kan duba a ga ko abin nan da take son cimmawa mai yiwuwa ne ko zai zama tamkar gurguwa da auren nesa bisa la’akari da matakai da ta dauka da kuma waiwayen abubuwan da ta gudanar a baya.

A bana, kasar Sin ta kudiri aniyar bunkasa tattalin arzikinta da a kalla kashi 5% (cikin dari), kamar yadda firmanistan kasar, Li Keqiang ya sanar a cikin rahoton ayyukan gwamnati da ya gabatar a taron wakilan majalisar jama’ar kasar, ranar 5 ga watan Maris din nan, baya ga kuma za ta samar da sabbin ayyukan yi miliyan 12, daidaita zaman kashe wando a birane da kashi 5.5, karin kashi 3% a mizanin farashin masu amfani da kayan masarufi.

Wannan kudiri da kasar Sin ta tsara cimmawa mai yiwuwa ne saboda dama kasar ba ta kwanta sai da zakara. Da farko abin da za a yi la’akari da shi, shi ne yadda kasar ta rika samun matsakaicin bunkasar tattalin arziki da mizanin 5.2% a cikin shekaru 5 da suka wuce, da kuma iya cin jarrabawar da bullar cutar COVID-19 ta yi mata, sai kuma wasu matakai da a halin yanzu ta dauka don cimma burin nata na samun ci gaba da kashi 5%.

Duk da cewa a shekarar 2022, kasar ba ta iya cimma kason da ta yi hankoron cimmawa a farko-farkon 2022 ba saboda wasu dalilan da suka shafi annobar COVID-19 da koma-bayan tattalin arzikin duniya, amma ta yi kokari da ta samu ci gaba da kashi 3% domin ba abu ne mai sauki a iya samun hakan ba a yanayi mai wuyar sha’ani da kan fado waka’an (ba-zata).

Har ila yau, matakan da kasar ta dauka domin tayar da komada daga COVID-19 a karshen bara da yadda kasar ta nuna kwazo a hada-hadar sarrafa kaya da cinikinsu da kuma ci gaban da ta samu na GDP a sulusin karshe na 2022 da kashi 2.9, duk sun zarce hasashen da aka yi na samun bunkasa, don haka wannan manuniya ce ga yiwuwar cimma burin kasar na bunkasa GDP da kashi 5%.

Labarai Masu Nasaba

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Bugu da kari, tun a farkon wannan shekarar, tattalin arzikin Sin ya samu ci gaba sakamakon kyawawan tsare-tsare da manufofi da gwamnatin kasa da ta kananan hukumomi suka dauka ta bangaren kudi, zuba jari, inganta yanayin kasuwanci da amfani da kayan masarufi da sauransu.

Bayanan da Hukumar Kididdiga ta Sin ta fitar a ranar 1 ga Maris, sun nuna an samu ci gaban sayen kayan da kasar Sin ta sarrafa a watan Fabrairu fiye da na watan Janairu da kashi 2.5. Wannan ya kara gaskata bayanan da aka fitar kwanan baya game da yadda farfadowar tattalin arzikin Sin ke samun ci gaba.

Don haka ma, galibin cibiyoyin da ke auna bunkasar tattalin arziki na duniya sun yi yakini game da habakar tattalin arzikin kasar Sin a bana, inda suka rika daga ma’aunin mizanin da suke hasashe a kai a kai. Misali, Asusun Ba da Lamuni na Duniya (IMF), ya yi hasashen cewa tattalin arzikin Sin zai bunkasa zuwa kashi 5.2% a bana. Haka nan mizanin Cibiyar Nomura Securities ya kyautata hasashen ci gaban zuwa kashi 5.3% daga kashi 4.8%. Ita ma Cibiyar Goldman Sachs ta yi hasashen abin zai kai 5.5%, sai kuma Morgan Stanley da hasashenta ya dara na kowa a cikinsu da ta ce tattalin arzikin na Sin zai bunkasa ne da kashi 5.7%.

Sakamakon dunkulewar tattalin arzikin duniya, ba shakka, ci gaban tattalin arzikin kasar Sin zai taimakawa ci gaban duniya.

Misali a Afirka, kasar Sin ta zama gagarabadau wajen bunkasa manyan ayyukan more rayuwa a kasashe daban-daban da suka hada da hanyoyi, sufurin jiragen kasa, madatsun ruwa, filayen jiragen sama, tashoshin teku da sauransu. Aikin da aka kammala na gina tashar teku mai zurfi na Lekki a jihar Legas da ke Nijeriya da ya kai kimanin Dala Biliyan 1.5, daya ne daga cikin ire-irensa masu dimbin yawa a Afirka. Don haka samun ci gaban tattalin arzikin Sin da kashi 5% zai ba ta dama ta samar da karin ayyukan ci gaba a Afirka.

Idan aka fadada zuwa duniya kuwa, ci gaban da kasar Sin za ta samu da kashi 5% zai taimaka wajen cike gibin da ake da shi a duniya, domin cinikayyar fitar da kaya da shigar da su a tsakanin Sin da kasashe za ta habaka. Kana ana sa rai Sin ta ba da gudunmawa ga bunkasar ci gaban duniya a 2023 da kashi 30 cikin 100.

Wannan tsari baro-baro a fili yake cewa babu tantama hakar kasar ta Sin za ta cimma ruwa bisa fafutikar da take yi wajen gina kasa ta zamani mai bin tsarin gurguzu a dukkan sassan rayuwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ighalo Yana Son Osimhen Ya Koma Manchester United

Next Post

Zaben Shugaban Kasa: Kotu Ta Amince Da Bukatar INEC Na Sake Inganta BVAS

Related

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

20 hours ago
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

21 hours ago
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12
Daga Birnin Sin

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

22 hours ago
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana
Daga Birnin Sin

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

23 hours ago
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

24 hours ago
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa
Daga Birnin Sin

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

1 day ago
Next Post
Zaben Shugaban Kasa: Kotu Ta Amince Da Bukatar INEC Na Sake Inganta BVAS

Zaben Shugaban Kasa: Kotu Ta Amince Da Bukatar INEC Na Sake Inganta BVAS

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.