• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Burin Kasar Sin Na Samun Bunkasar GDP Da Kashi 5% A Bana Zai Cika

by yahuzajere
3 years ago
Kasar Sin

Masu zantukan hikima kan ce “da icce mai kama ake kota”, tabbas haka ne, domin duk lokacin da wata kasa ta tasa wani buri a gaba, a kan duba a ga ko abin nan da take son cimmawa mai yiwuwa ne ko zai zama tamkar gurguwa da auren nesa bisa la’akari da matakai da ta dauka da kuma waiwayen abubuwan da ta gudanar a baya.

A bana, kasar Sin ta kudiri aniyar bunkasa tattalin arzikinta da a kalla kashi 5% (cikin dari), kamar yadda firmanistan kasar, Li Keqiang ya sanar a cikin rahoton ayyukan gwamnati da ya gabatar a taron wakilan majalisar jama’ar kasar, ranar 5 ga watan Maris din nan, baya ga kuma za ta samar da sabbin ayyukan yi miliyan 12, daidaita zaman kashe wando a birane da kashi 5.5, karin kashi 3% a mizanin farashin masu amfani da kayan masarufi.

Wannan kudiri da kasar Sin ta tsara cimmawa mai yiwuwa ne saboda dama kasar ba ta kwanta sai da zakara. Da farko abin da za a yi la’akari da shi, shi ne yadda kasar ta rika samun matsakaicin bunkasar tattalin arziki da mizanin 5.2% a cikin shekaru 5 da suka wuce, da kuma iya cin jarrabawar da bullar cutar COVID-19 ta yi mata, sai kuma wasu matakai da a halin yanzu ta dauka don cimma burin nata na samun ci gaba da kashi 5%.

Duk da cewa a shekarar 2022, kasar ba ta iya cimma kason da ta yi hankoron cimmawa a farko-farkon 2022 ba saboda wasu dalilan da suka shafi annobar COVID-19 da koma-bayan tattalin arzikin duniya, amma ta yi kokari da ta samu ci gaba da kashi 3% domin ba abu ne mai sauki a iya samun hakan ba a yanayi mai wuyar sha’ani da kan fado waka’an (ba-zata).

Har ila yau, matakan da kasar ta dauka domin tayar da komada daga COVID-19 a karshen bara da yadda kasar ta nuna kwazo a hada-hadar sarrafa kaya da cinikinsu da kuma ci gaban da ta samu na GDP a sulusin karshe na 2022 da kashi 2.9, duk sun zarce hasashen da aka yi na samun bunkasa, don haka wannan manuniya ce ga yiwuwar cimma burin kasar na bunkasa GDP da kashi 5%.

LABARAI MASU NASABA

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Bugu da kari, tun a farkon wannan shekarar, tattalin arzikin Sin ya samu ci gaba sakamakon kyawawan tsare-tsare da manufofi da gwamnatin kasa da ta kananan hukumomi suka dauka ta bangaren kudi, zuba jari, inganta yanayin kasuwanci da amfani da kayan masarufi da sauransu.

Bayanan da Hukumar Kididdiga ta Sin ta fitar a ranar 1 ga Maris, sun nuna an samu ci gaban sayen kayan da kasar Sin ta sarrafa a watan Fabrairu fiye da na watan Janairu da kashi 2.5. Wannan ya kara gaskata bayanan da aka fitar kwanan baya game da yadda farfadowar tattalin arzikin Sin ke samun ci gaba.

Don haka ma, galibin cibiyoyin da ke auna bunkasar tattalin arziki na duniya sun yi yakini game da habakar tattalin arzikin kasar Sin a bana, inda suka rika daga ma’aunin mizanin da suke hasashe a kai a kai. Misali, Asusun Ba da Lamuni na Duniya (IMF), ya yi hasashen cewa tattalin arzikin Sin zai bunkasa zuwa kashi 5.2% a bana. Haka nan mizanin Cibiyar Nomura Securities ya kyautata hasashen ci gaban zuwa kashi 5.3% daga kashi 4.8%. Ita ma Cibiyar Goldman Sachs ta yi hasashen abin zai kai 5.5%, sai kuma Morgan Stanley da hasashenta ya dara na kowa a cikinsu da ta ce tattalin arzikin na Sin zai bunkasa ne da kashi 5.7%.

Sakamakon dunkulewar tattalin arzikin duniya, ba shakka, ci gaban tattalin arzikin kasar Sin zai taimakawa ci gaban duniya.

Misali a Afirka, kasar Sin ta zama gagarabadau wajen bunkasa manyan ayyukan more rayuwa a kasashe daban-daban da suka hada da hanyoyi, sufurin jiragen kasa, madatsun ruwa, filayen jiragen sama, tashoshin teku da sauransu. Aikin da aka kammala na gina tashar teku mai zurfi na Lekki a jihar Legas da ke Nijeriya da ya kai kimanin Dala Biliyan 1.5, daya ne daga cikin ire-irensa masu dimbin yawa a Afirka. Don haka samun ci gaban tattalin arzikin Sin da kashi 5% zai ba ta dama ta samar da karin ayyukan ci gaba a Afirka.

Idan aka fadada zuwa duniya kuwa, ci gaban da kasar Sin za ta samu da kashi 5% zai taimaka wajen cike gibin da ake da shi a duniya, domin cinikayyar fitar da kaya da shigar da su a tsakanin Sin da kasashe za ta habaka. Kana ana sa rai Sin ta ba da gudunmawa ga bunkasar ci gaban duniya a 2023 da kashi 30 cikin 100.

Wannan tsari baro-baro a fili yake cewa babu tantama hakar kasar ta Sin za ta cimma ruwa bisa fafutikar da take yi wajen gina kasa ta zamani mai bin tsarin gurguzu a dukkan sassan rayuwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka
Daga Birnin Sin

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Next Post
Zaben Shugaban Kasa: Kotu Ta Amince Da Bukatar INEC Na Sake Inganta BVAS

Zaben Shugaban Kasa: Kotu Ta Amince Da Bukatar INEC Na Sake Inganta BVAS

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Ɗan Fashi Sanye Da Kayan NYSC A Enugu

October 21, 2025
Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025
Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.