• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Raunin Jam’iyyun Adawa Da Barazana Ga Dimokuradiyyar Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Adawa

Daya daga cikin babbar barazana ga Dimokuradiyyar ita ce, raunin jam’iyyun adawa, wanda mutane da dama na ganin hakan zai sa kasar ta kama tsarin jam’iyya guda daya.

A cikin tsarin mulkin dimokuradiyya, ‘yan adawa na matukar taka muhimmiyar rawa wajen kalubalantar gwamnati ta yadda za a gyara tsarin da bai yi daidai da tsarin mulkin dimokuradiyya ba. Ko da gwamnati ba ta yi amfani da kiraye-kirayen ‘yan adawa wajen gyara kuskure, tana amfana da su wajen gudanar da bincike a kan korafin da suka gabatar ta yadda za a samu damar yin gyara.

  • Kano: Kotun Daukaka Kara Ta Bukace Lauyoyin Su Mayar Da Kwafin Takardun Shari’ar
  • Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Uruguay

Tsarin mulki na shugabancin kasa ya kawo ka’idoji ta yadda jam’iyyun adawa za su iya gudanar da bincike wajen gudanar da harkokin gwamnati.

A ko da yaushe, jam’iyyar adawa na sa jam’iyya mai mulki ta tashi tsaye wajen gudanar da tsare-tsare da kuma shirye-shiryenta. Haka nan kuma suna dakile wuce gona da iri da muguwar mulkin kama-karya.

A jamhuriya ta daya da ta biyu, Nijeriya tana da al’adar gudanar da siyasar adawa. Marigayi Cif Obafemi Awolowo na jam’iyyar ‘Action Group’ (AG), wanda daga ta koma jam’iyyar ‘Unity Party of Nigeria’ (UPN), a matsayinsa na dan adawa, ya tunkari gwamnatin da ke kan karagar mulki da hujjoji masu tsauri da alkaluma ta yadda za a ceto Nijeriya. Hatta Dakta Nnamdi Azikiwe da sauran su duk ’yan adawa wadanda suke kalubalantar wuce gona da iri na jam’iyya mai mulki da ke rake da gwamnati.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

Ko a lokacin mulkin soja, an sami manyan kungiyoyin fararen huda kamar irin su ‘Campaign for Democracy (CD)’, ‘Mobement for National Reformation (MNR)’, kwamitin kare hakkin Dan’adam (CDHR), kungiyar lauyoyin Nijeriya (NBA), kungiyar kwadago (NLC) da dai sauran su, sun yi tsayan daka wajen yakar mulkin kama-karya da rashin gudanar da mulki yadda ya kamata.

Irinsu Cif Gani Fawehinmi, Farfesa Wole Soyinka, Aka Bashorun, Olisa Agbakoba, Femi Falana, Beko Ransom-Kuti, Ayo Obe, Ken Saro-Wiwa da dai sauransu sun shiga gidan yari saboda sukar gwamnati.

Amma a yau a siyasar Nijeriya babu wata adawa mai karfi da yadda zai iya kawo sauyi ga manufofin gwamnati wadanda ba dace da tsarin mulki ba. Tun bayan kammala zabukan da suka gabata, jam’iyyun adawa sun yi barci, lamarin da ya sa jam’iyyar APC mai mulkin gwamnatin tarayya take jagorantar ‘yan Nijeriya yadda take so.

Yanzu haka dai a Nijeriya manyan jam’iyyun adawar sun hada da jam’iyyun PDP da LP, amma babu daya daga cikinsu da ta iya kalubalantar jam’iyyar APC mai mulki yadda ya kamata a wurin gudanar da mulkin Nijeriya.

A yanzu haka dai, ‘yan Nijeriya sun zura ido don ganin yadda PDP da LP za su iya amsar mulki a hannun jam’iyyar APC.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Hujjojin Obasanjo Na Cewa “Dimokuradiyyar Turawan Yamma Ba Ta Karbi Afirka Ba”

Hujjojin Obasanjo Na Cewa “Dimokuradiyyar Turawan Yamma Ba Ta Karbi Afirka Ba”

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

October 10, 2025
Adawa

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

October 10, 2025
Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

October 10, 2025
Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

October 10, 2025
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.