ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hujjojin Obasanjo Na Cewa “Dimokuradiyyar Turawan Yamma Ba Ta Karbi Afirka Ba”

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Obasanjo

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya jaddada cewa tsarin dimokuradiyyar Turawan yamma da kasashen Afirka suka kwaikwaya bai karbe su ba, inda ya bayar da hujjojinsa kan fadar haka.

Da farko Obasanjo ya ce dimokuradiyyar turawan ba ta dace da yanayin tarihi, al’adu da kabilun mutanen yammacin Afirka ba.

  • An Gudanar Da Bikin Reel Africa A Birnin Shanghai
  • Ya Zuwa Karshen Shekarar Bara Tsayin Manyan Titunan Mota Na Kasar Sin Ya Kai Kilomita 177,000

Haka nan, tsohon shugaban kasar ya bayyana cewa salon dimokuradiyyar kasashen yammacin duniya ya gaza a Nahiyar Afirka domin ba ta la’akari da ra’ayin mafi yawan jama’a.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana hakan ne a lokacin da yake gabatar da jawabin a wani babban taron tuntuba kan sake tunanin dimokuradiyyar Turawan yamma a Afirka, wanda ya gudana a Abeokuta, Babban Birnin Jihar Ogun.

Obasanjo, wanda ya kira taron, ya kuma siffanta dimokaradiyyar turawan na yamma a matsayin gwamnatin mutane kalilan da ke mulkan mutane masu dimbin yawa, kuma wadannan tsirarun mutane ne kawai wakilan wasu daga cikin jama’a, amma ba wakilan al’umma ba.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

Ya ba da shawarar a sauya dimokuradiyyar Turawan yamma a kasashen Afirka.

A cewarsa, kasashen Afirka ba su da wata alaka wajen tafiyar da tsarin gwamnati wanda ba su da hannu a cikinsa.

Obasanjo ya ce, “Rauni da gazawar dimokuradiyyar Turawan yamma dai ya kunshi yadda ake aiwatar da ita ya saba da al’adun kasashen Afirka.

“Da zarar ka tashi wakiltar mutane, za ka fara fuskantar kalubale da matsaloli. Ga wadanda suka ayyanata a matsayin mulkin mafi rinjaye, shin ya kamata a yi watsi da tsiraru.?

“A takaice, muna da tsarin gwamnati wanda ba mu da hannun wajen tsarawa da kuma aiwatarwa, bai kamata mu ci gaba da amfani da shi ba, alhalin mun san ba ya mana aiki.

“Wadanda suka kawo mana shi a yanzu suna kokwanton sahihancinsa da suka kirkira, a yanzu kuma bai dace ba idan har ba za a gyara ba.

“Muhimmancin kowane tsarin gwamnati shi ne walwala da jin dadin al’ummar kasa.

“A nan, dole ne mu yi duba yanayin kwazon dimokuradiyyar Turawan yamma da suka gadar mana tun lokacin mulkin mallaka.

“Mun taro a nan ne don yin tunani a matsayinmu na jagororin ilimi da kuma na siyasa wajen fitar da matsaya kan dimokuradiyyar Turawan yamma.”

Obasanjo
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Duniya Na Bukatar Matasa Masu Ilimin Fasaha Domin Magance Tarin Matsaloli – Gwamnatin Tarayya

Duniya Na Bukatar Matasa Masu Ilimin Fasaha Domin Magance Tarin Matsaloli – Gwamnatin Tarayya

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.