• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Sin Da Amurka Ba Su Bukatar Zama Abokan Gabar Juna 

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sharhi: Sin Da Amurka Ba Su Bukatar Zama Abokan Gabar Juna 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yanzu haka sakatariyar baitulmalin kasar Amurka Janet Yellen na yin ziyarar aiki ta kwanaki hudu a kasar Sin, wadda kuma ta kasance ta biyu daga cikin manyan jami’an gwamnatin Biden da suka kawo ziyara a kasar Sin, biyo bayan ziyarar da sakataren harkokin wajen kasar Antony Blinken ya yi a watan da ya gabata. A labarin da aka bayar, an ce, da mista Antony Blinken da Madam Yellen dukkansu sun bayyana cewa, Amurka na son tabbatar da daidaiton da shugabannin kasashen biyu suka cimma a yayin ganawarsu a gefen taron kolin G20, wanda aka gudanar a bara a tsibirin Bali na kasar Indonesia, wato su martaba juna, da zama lafiya da juna, da kuma yi hadin gwiwa ta cin moriyar juna, kuma Amurka ba ta son ganin rarrabuwar kawuna a tsakaninta da kasar Sin. 

Amurka ta tura manyan jami’anta zuwa kasar Sin tare da yin kalaman da suka kasance tamkar neman kyautata hulda da kasar Sin, sai dai ba lallai al’amarin haka yake ba, kasancewar bayan da mista Blinken ya koma gida, ya bayyana wa ’yan jarida cewa, “sabanin dake tsakanin Sin da Amurka ba wani boyayyen abu ba ne. Kuma Amurka za ta ci gaba da kare moriyarta da akidunta, haka kuma za ta ci gaba da yin abin da kasar Sin ba ta son gani, tare da furta abubuwan da Sin din ba ta son ji.”

  • Ziyarar Xi Jinping A Jiangsu Na Da Nufin Inganta Aikin Gina Tsarin Masana’antu Na Zamani Na Kasar Sin

A hakika, sabanin da ke tsakanin Sin da Amurka ya samo asalinsa ne daga irin akidun da kasar ta Amurka ke da shi. A ganin kasar Amurka, moriyarta, da tsaronta, sun fi muhimmanci fiye da na sauran kasashe. Tana kuma yayata irin salon ’yanci da dimokuradiyya, da hakkin dan Adam nata a duniya, ta yadda duk wata kasar da ba ta yi mata biyayya ba, to za ta dauke ta a matsayin abokiyar gaba, har ma za ta yi kokarin dakile ta, da rushe mulkinta, har ma kaddamar da yaki a kanta, kuma irin wannan misali ba ya lasaftuwa.

Kasar Sin a nata bangaren tana daukar matsayi akasin haka, inda ta gabatar da shawarar “raya daukacin kasashen duniya baki daya”, shawarar da ta jaddada muhimmancin rashin barin wata kasa a baya, baya ga kuma shawarar “kiyaye tsaron bai daya na kasashen duniya” da kasar ta gabatar, wadda ta jaddada muhimmancin kiyaye zaman lafiya da tsaro na bai daya na daukacin kasashen duniya. Sai kuma shawarar “raya mabambantan wayewar kai na duniya” da kasar Sin ta gabatar, wadda ta jaddada muhimmancin martaba kasancewar mabambantan wayewar kai a duniya.

Manufofi mabanbanta da Amurka da Sin ke yayatawa, na da nasaba ne da banbancin tunani. Amurka a bangaren ta, na da imanin cewa, idan wani ya samu kudi, hakan na nufin wani zai rasa nasa, yayin da a nata bangare kasar Sin ke ganin mutane da dama, na iya ci daga kwarya guda, sabo da za a iya girka abincin da zai ishi kowa. Bugu da kari, Amurka na ganin ba zai yiwu teku daya ya ishi manyan kasashe biyu wanka ba; A daya bangaren kuma, Sin na ganin wannan duniya ta ishi kowa watayawa, da samun ci gaban bai daya, da wadatar daukacin kasashen duniya, ciki har da Sin da ita kan ta Amurka.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Kafin Madam Yellen ta tashi zuwa kasar Sin, wani dan jarida da ya bi ta a wannan ziyara, ya wallafa wata makala mai taken “Yellen za ta kai ziyara kasar Sin don daidaita dangantakar tattalin arziki tsakanin kasashen biyu” a jaridar “New York Times”, kuma a bangaren ra’ayoyin masu karatu, akwai Amurkawa da suka karanta makalar da suka bayyana cewa, da fatan Yellen za ta bude sabon babi da kasar Sin, sabo da Sin da Amurka ba su bukatar zama abokan gaba ga juna.

Abin haka yake. A hakika, Sin da Amurka sun kasance suna cin moriyar juna a huldarsu ta tattalin arziki, kuma kowanensu ba zai amfana da yakin ciniki ko rarrabuwar kawuna a tsakaninsu ba, kuma abu ne mai kyau kasashen biyu mafiya karfin tattalin arziki a duniya su zauna su yi musayar ra’ayi da juna.

Madam Yellen na ci gaba da wannan ziyara a kasar Sin, mu kuma muna zuba ido don gani abin da za ta fada, musamman abin da za ta aikata daga baya.

 

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bangare Japan Da Ya Dage Sai Ya Zubar Da Dagwalon Ruwan Nukiliya Cikin Teku Zai Sha Kunya Ta Tsawon Tarihi

Next Post

‘Muna Cikin Fargabar Yiwuwar Ambaliyar Ruwa A Daminar Bana’

Related

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar
Daga Birnin Sin

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

57 minutes ago
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta
Daga Birnin Sin

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

2 hours ago
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila
Daga Birnin Sin

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

4 hours ago
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

23 hours ago
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

24 hours ago
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

1 day ago
Next Post
‘Muna Cikin Fargabar Yiwuwar Ambaliyar Ruwa A Daminar Bana’

‘Muna Cikin Fargabar Yiwuwar Ambaliyar Ruwa A Daminar Bana’

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.