• English
  • Business News
Tuesday, September 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 hours ago
in Ra'ayi Riga
0
Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Kasa da kasa su kasance suna zaman daidaito da juna wajen sa hannun gudanar da harkokin duniya da ma yanke shawara da cin moriya” “Kada a tilasta kakaba dokokin cikin gida na wasu kasashe a kan sauran kasashe” “Nuna rashin amincewa da daukar matakai na kashin kai” “A yi kokarin daidaita gibin da ke tsakanin kasashe masu tasowa da kasashe masu ci gaba” “A dauki hakikanan matakai na hadin gwiwa”. A ranar 1 ga wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya jagoranci taron kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai (SCO) Plus a birnin Tianjin da ke arewacin kasar Sin, inda ya gabatar da Tsarin Shugabanci na Duniya wato “GGI” a takaice, shawarar da ta samar da mafita ga duniyar da ke fama da tashe-tashen hankula a halin yanzu.

A duniyar yau, aukuwar rikicin shiyya shiyya da matsalolin ci gaban tattalin arziki da rashin bin ka’idoji da dokoki da daukar matakai na kashin kai da kariyar ciniki da rashin tsarin shugabanci nagari a duniya, duk suna addabar kasashen duniya. Ta yaya za a inganta tsarin shugabanci na duniya, ya zama abin da ke bukatar a gano bakin zaren warware shi ga gamayyar kasa da kasa. To, faduwa ta zo daidai da zama bisa yadda kasar Sin ta gabatar da shawarar GGI.

“Ya kamata mu bi tsarin daidaito a kan ‘yancin yankunan kasa sau da kafa, ya kamata mu kiyaye bin dokokin kasa da kasa, ya kamata mu aiwatar da tsarin mu’amala da bangarori daban daban, ya kamata mu yi yekuwar amfani da tsarin da zai fi mayar da hankali a kan al’umma, kana ya kamata mu mai da hankali kan daukar matakai na hakika.” Ka’idoji biyar ke nan da ke cikin shawarar GGI, wadanda suka mai da hankali a kan ainihin matsalolin da ake fuskanta a tsarin shugabanci na duniya, tare da bayyana matsayi da dabarun da suka kamata a dauka domin gyara tsarin. Daga cikinsu “tsarin daidaito a kan ‘yancin yankunan kasa” ya zama tushen tsarin shugabanci na duniya. Kasa da kasa, manya da kanana, masu karfi ko marasa karfi, ya kamata su kasance daidai-wa-daida wajen sa hannu ga harkokin duniya. Ya zama dole a kawo karshen yadda wasu ‘yan tsirarrun kasashe kawai ke fada a ji a harkokin duniya, kuma ya kamata “a kara wakilcin kasashe masu tasowa da fito da muryoyinsu a duniya”, don kara inganta adalcin tsarin duniya. Sa’an nan, dokokin kasa da kasa su kasance masu tabbaci ga tsarin shugabanci na duniya, wadanda ya kamata kasa da kasa su rubuta su, da kiyaye su, da ma aiwatar da su. Har wa yau, yin mu’amala da bangarori daban daban ya zama hanyar da za a bi wajen gudanar da tsarin shugabancin duniya, kasancewar tsarin shugabancin duniya na shafar kowa da kowa, ya kamata a daidaita hadin gwiwa da juna a maimakon nuna fin karfi. Kazalika, ya kamata a mai da hankali a kan al’umma, a sabili da yadda kyautata rayuwar al’umma shi ne jigon ainihin burin da ake neman cimmawa wajen inganta tsarin shugabanci na duniya. Daga karshe, daukar hakikanan matakai ya kasance ginshiki na tsarin shugabancin duniya, don daidaita matsalolin da ke addabar kasa da kasa, musamman ma kasashe masu tasowa.

Bana ake cika shekaru 80 da samun nasarar yaki da mulkin danniya a duniya da ma kafa majalisar dinkin duniya(MDD). A shekaru 80 da suka wuce, al’ummun duniya sun hada karfi da karfe wajen samun nasarar yaki da mulkin danniya, kuma kasancewar kasar Sin daga cikin muhimman kasashen da suka cimma nasarar yakin, ta hada kai da kasa da kasa wajen kafa MDD. A yau kuma, lokacin da tsarin shugabanci na duniya ke fuskantar sabbin matsaloli, kasar Sin a matsayinta na babbar kasa da ke kokarin sauke nauyin da ke bisa wuyanta, za ta tsaya tsayin daka wajen kiyaye tsarin duniya da ke karkashin ginshikin MDD, ta hada kai da kasashe masu neman ci gaba, don dada yin kokarin gina al’ummar duniya mai kyakkyawar makoma ta bai daya, da ma tabbatar da zaman lafiya da ci gaba ga dukkanin bil Adama.

 

Labarai Masu Nasaba

Yadda Kasar Sin Ta Nuna Wa Afirka Asalin Ma’Anar Hakkin Dan Adam Sabanin Irin Na Kasashen Yamma

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

Next Post

NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano

Related

Yadda Kasar Sin Ta Nuna Wa Afirka Asalin Ma’Anar Hakkin Dan Adam Sabanin Irin Na Kasashen Yamma
Ra'ayi Riga

Yadda Kasar Sin Ta Nuna Wa Afirka Asalin Ma’Anar Hakkin Dan Adam Sabanin Irin Na Kasashen Yamma

4 days ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki

5 days ago
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka
Ra'ayi Riga

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

1 week ago
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya
Ra'ayi Riga

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

1 week ago
Tunawa Da Tarihi Tana Da Ma’anar Musamman
Ra'ayi Riga

Tunawa Da Tarihi Tana Da Ma’anar Musamman

2 weeks ago
Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Ra'ayi Riga

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

3 weeks ago
Next Post
NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano

NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya

Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya

September 2, 2025
Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

September 2, 2025
Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya

Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya

September 2, 2025
Kuri’ar CGTN Ta Nuna Gamsuwar Al’ummu Da Rawar Da Sin Ta Taka Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na 2

Kuri’ar CGTN Ta Nuna Gamsuwar Al’ummu Da Rawar Da Sin Ta Taka Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na 2

September 2, 2025
Rashin Shugabanci Nagari Ne Har Yanzu Ƙananan Yara Ke Mutuwa Saboda Zazzaɓin Cizon Sauro

Rashin Shugabanci Nagari Ne Har Yanzu Ƙananan Yara Ke Mutuwa Saboda Zazzaɓin Cizon Sauro

September 2, 2025
Wang Yi Ya Yi Bitar Nasarorin Da Aka Cimma Yayin Taron Kolin SCO Na Tianjin

Wang Yi Ya Yi Bitar Nasarorin Da Aka Cimma Yayin Taron Kolin SCO Na Tianjin

September 2, 2025
NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano

NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano

September 2, 2025
Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

September 2, 2025
NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

September 2, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Masu Safarar Makamai A Katsina, Sun Ƙwato Makamai

September 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.