• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarar Tabbatar Da Tsaron Duniya: Sin Ta Zo Da Mafita Ga Alkaba’in Tashe-tashen Hankula

by Abdulrazaq Yahuza
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Shawarar Tabbatar Da Tsaron Duniya: Sin Ta Zo Da Mafita Ga Alkaba’in Tashe-tashen Hankula
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ko dan jariri da ke cikin mahaifiyarsa ya san irin alkaba’in da ke addabar duniya a halin yanzu ta fuskar tabarbarewar tsaro. Tsoro da firgici na ci gaba da haifar da razani a tsakanin al’umma. An mayar da kwararar da jinin Bil’adama ba a bakin komi ba. Ana kashe mata da kananan yara, haka nan tsofaffi da dattawa duk babu wanda ya tsira. Dokokin kiyaye kisan kare-dangi tamkar ba su aiki saboda munafurcin Turawan yamma. Wanda suke so shi ne da gaskiya komai zaluncinsa wanda ya zamo dan adawarsu kuwa shi ne tunku-uwar-laifi duk irin gaskiyarsa.

Tauye ‘yancin kasashe masu cin gashin kansu ya yawaita, karfafa abokan hulda masu tayar da zaune tsaye a kasashen da suka ki bayar da kai bori ya hau ya zama ruwan dare game da duniya. Duk wadannan abubuwa an gan su a Zahiri sun faru a Iraki, Libiya, Venezuela da wasunsu da dama. Sai kuma rikicin cikin gida da ake rurawa da kusan yau a duniya kasashe daidai ne suka tsira daga makircin su Amurka kan haka.

Al’ummar duniya ta gaji da alkaba’in rashin tsaron da ake fama da shi, wanda wani lokaci mutumin da yake rayuwa a doron kasa musamman a yankunan da abin ya fi kamari yake burin ina ma shi ne a cikin kabari. Kazantacciyar zubar da jinin da ake yi a yankin Gaza tun daga watan Oktobar bara zuwa yau ya isa abin misali baya ga rikicin da ya zama kamar cin kwan makauniya irin na Somaliya ko Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, sannan ga wanda ake fama da shi a tsakanin Rasha da Ukraine. Tambayar da kowa ke yi ita ce, yaushe masu haddasa wannan husuma za su bar al’ummar duniya ta numfasa?

  • Kasar Sin Ta Bayyana Damuwa Game Da Halin Da Ake Ciki Tsakanin Iran Da Isra’ila
  • Bangaren Kera Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Kasar Sin Ya Yi Kira Ga EU Da Ya Gudanar Da Bincike Bisa Adalci

Mai karatu, na ci karo da wata kwakkwarar amsa a yayin da na samu labarin shawarar da kasar Sin ta gabatar mai taken Yunkurin Tabbatar da Tsaron Duniya, wadda Shugaba Xi Jinping ya ambata a jawabinsa na bude taron Dandalin Boao, ranar 21 ga watan Afrilun 2022.

Wannan shawara cikin hikima da basira tana nuna matsayin kasar Sin na neman samar da ingantaccen tsaro mai amfanarwa tare da wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya.

Labarai Masu Nasaba

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Kasar Sin ta ba da shawarar kafa sabuwar hanyar tsaro bisa manufar tabbatar da tsaro na bai daya, da zai zama cikakke bisa hadin gwiwa wanda zai dore tare da mutunta juna a matsayin babban ginshiki. Haka nan shawarar tana neman a samar da wani tsari da zai sanya rashin rarraba tsaro a matsayin muhimmiyar ka’ida, da sanya burin samar da al’umma mai cikakkiyar tsaro a gaba.

Karin wani abin sha’awa game da wannan shawarar ta Yunkurin Tabbatar da Tsaron Duniya da kasar Sin ta gabatar shi ne, yadda ta kawo maslaha da tattaunawa da hadin gwiwa a matsayin mafita a maimakon amfani da adawa ko kawance na taron dangi.

Alamu sun nuna wannan shawara za ta samu nasara bisa yadda kasashe fiye da 100 da kungiyoyin yanki da na kasa da kasa suka yi na’am da ita tare da shigar da ita cikin kundayen huldar da ke tsakaninsu da kasar Sin, inda hakan ya sa ta zama abu mai muhimmanci ga sha’anin tsaron duniya.

Wannan tsari da shawarar ta kawo ya sha bamban da irin na kasashen yamma kamar su Amurka da ya jefa mu cikin alkaba’in tashe-tashen hankulan da muke gani a duniya. A tsarin tsaron su Amurka, kansu kawai suka sani ba ruwansu da saura da yi wa abin tanadi na fitar hankali kamar yadda Amurka ta ware Dala biliyan 886 a kasafinta na 2024 a fannin soja kawai. Wannan adadi da ya karu da kimanin Dala biliyan 30 a kan na bara, ba a taba ganin irin sa a tarihin kasar ba.

Har ila yau, sun hana duniya zaman lafiya domin kare muradun kansu ta hanyar kirkiro da kawance na soji daban-daban masu rarraba kawunan kasashe da kakaba takunkumai na karya tattalin arziki da tauye hakkoki da muradun kasashe wadanda dokokin duniya suka halatta da kuma zama kanwa uwar gami na wargaza sha’anin tsaron kasashe kamar yadda muke gani a Palasdinu da Tekun Kudancin Sin da Yankin Koriya.

Wannan ya sa nake da yakinin shawarar tabbatar da tsaron duniya da kasar Sin ta gabatar za ta wanzar da adalcin da ake fatan gani da zai zama silar magance alkaba’in duniya da kawar da tarnakin bunkasa ci gaban tattalin arzikin kasashe.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaDuniyaRashin TsaroShawaraTashe-Tashen HankulaTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

APC A Kano Ta Kori Shugabannin Jam’iyyar A Matakin Unguwa Da Suka Dakatar Da Ganduje 

Next Post

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Related

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
Ra'ayi Riga

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

6 days ago
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

1 week ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

1 week ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

2 weeks ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

2 weeks ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

2 weeks ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce - El-Rufai

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

September 15, 2025
Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

September 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

September 15, 2025
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

September 15, 2025
Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

September 15, 2025
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

September 15, 2025
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.