ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarar Tabbatar Da Tsaron Duniya: Sin Ta Zo Da Mafita Ga Alkaba’in Tashe-tashen Hankula

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
Tsaro

Ko dan jariri da ke cikin mahaifiyarsa ya san irin alkaba’in da ke addabar duniya a halin yanzu ta fuskar tabarbarewar tsaro. Tsoro da firgici na ci gaba da haifar da razani a tsakanin al’umma. An mayar da kwararar da jinin Bil’adama ba a bakin komi ba. Ana kashe mata da kananan yara, haka nan tsofaffi da dattawa duk babu wanda ya tsira. Dokokin kiyaye kisan kare-dangi tamkar ba su aiki saboda munafurcin Turawan yamma. Wanda suke so shi ne da gaskiya komai zaluncinsa wanda ya zamo dan adawarsu kuwa shi ne tunku-uwar-laifi duk irin gaskiyarsa.

Tauye ‘yancin kasashe masu cin gashin kansu ya yawaita, karfafa abokan hulda masu tayar da zaune tsaye a kasashen da suka ki bayar da kai bori ya hau ya zama ruwan dare game da duniya. Duk wadannan abubuwa an gan su a Zahiri sun faru a Iraki, Libiya, Venezuela da wasunsu da dama. Sai kuma rikicin cikin gida da ake rurawa da kusan yau a duniya kasashe daidai ne suka tsira daga makircin su Amurka kan haka.

Al’ummar duniya ta gaji da alkaba’in rashin tsaron da ake fama da shi, wanda wani lokaci mutumin da yake rayuwa a doron kasa musamman a yankunan da abin ya fi kamari yake burin ina ma shi ne a cikin kabari. Kazantacciyar zubar da jinin da ake yi a yankin Gaza tun daga watan Oktobar bara zuwa yau ya isa abin misali baya ga rikicin da ya zama kamar cin kwan makauniya irin na Somaliya ko Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, sannan ga wanda ake fama da shi a tsakanin Rasha da Ukraine. Tambayar da kowa ke yi ita ce, yaushe masu haddasa wannan husuma za su bar al’ummar duniya ta numfasa?

ADVERTISEMENT
  • Kasar Sin Ta Bayyana Damuwa Game Da Halin Da Ake Ciki Tsakanin Iran Da Isra’ila
  • Bangaren Kera Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Kasar Sin Ya Yi Kira Ga EU Da Ya Gudanar Da Bincike Bisa Adalci

Mai karatu, na ci karo da wata kwakkwarar amsa a yayin da na samu labarin shawarar da kasar Sin ta gabatar mai taken Yunkurin Tabbatar da Tsaron Duniya, wadda Shugaba Xi Jinping ya ambata a jawabinsa na bude taron Dandalin Boao, ranar 21 ga watan Afrilun 2022.

Wannan shawara cikin hikima da basira tana nuna matsayin kasar Sin na neman samar da ingantaccen tsaro mai amfanarwa tare da wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Kasar Sin ta ba da shawarar kafa sabuwar hanyar tsaro bisa manufar tabbatar da tsaro na bai daya, da zai zama cikakke bisa hadin gwiwa wanda zai dore tare da mutunta juna a matsayin babban ginshiki. Haka nan shawarar tana neman a samar da wani tsari da zai sanya rashin rarraba tsaro a matsayin muhimmiyar ka’ida, da sanya burin samar da al’umma mai cikakkiyar tsaro a gaba.

Karin wani abin sha’awa game da wannan shawarar ta Yunkurin Tabbatar da Tsaron Duniya da kasar Sin ta gabatar shi ne, yadda ta kawo maslaha da tattaunawa da hadin gwiwa a matsayin mafita a maimakon amfani da adawa ko kawance na taron dangi.

Alamu sun nuna wannan shawara za ta samu nasara bisa yadda kasashe fiye da 100 da kungiyoyin yanki da na kasa da kasa suka yi na’am da ita tare da shigar da ita cikin kundayen huldar da ke tsakaninsu da kasar Sin, inda hakan ya sa ta zama abu mai muhimmanci ga sha’anin tsaron duniya.

Wannan tsari da shawarar ta kawo ya sha bamban da irin na kasashen yamma kamar su Amurka da ya jefa mu cikin alkaba’in tashe-tashen hankulan da muke gani a duniya. A tsarin tsaron su Amurka, kansu kawai suka sani ba ruwansu da saura da yi wa abin tanadi na fitar hankali kamar yadda Amurka ta ware Dala biliyan 886 a kasafinta na 2024 a fannin soja kawai. Wannan adadi da ya karu da kimanin Dala biliyan 30 a kan na bara, ba a taba ganin irin sa a tarihin kasar ba.

Har ila yau, sun hana duniya zaman lafiya domin kare muradun kansu ta hanyar kirkiro da kawance na soji daban-daban masu rarraba kawunan kasashe da kakaba takunkumai na karya tattalin arziki da tauye hakkoki da muradun kasashe wadanda dokokin duniya suka halatta da kuma zama kanwa uwar gami na wargaza sha’anin tsaron kasashe kamar yadda muke gani a Palasdinu da Tekun Kudancin Sin da Yankin Koriya.

Wannan ya sa nake da yakinin shawarar tabbatar da tsaron duniya da kasar Sin ta gabatar za ta wanzar da adalcin da ake fatan gani da zai zama silar magance alkaba’in duniya da kawar da tarnakin bunkasa ci gaban tattalin arzikin kasashe.

 

Tsaro
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce - El-Rufai

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.