• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shehu Mahy Inyass Ya Sanar Da Sauye-sauye A Tafiyar Tijjaniya A Nijeriya

by Bello Hamza and Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Shehu Mahy Inyass Ya Sanar Da Sauye-sauye A Tafiyar Tijjaniya A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani gaggarumar ci gaba da aka samu a tafiyar darikar Tijjaniya, Khalifa Sheikh Mahy Sheikh Ibrahim Inyass ya sanar da wasu sauye-sauye domin karfafa zumunci da hadin kai na darikar a fadin duniya baki daya, an bayyana haka ne a sanarwar da Khalifan ya fitar bayan tattaunawa tare da manyan masu ruwa da tsaki da manyan Shehunai.

 

Shawarar ta biyo bayan kammala bikin mauludin da aka yi na kwanan nan inda aka samu halartar ‘yan darikar Tijjaniyyah daga ko’ina a fadin duniya. Khalifa ya taya al’ummar Musulmai murnar wadannan bukukuwan da aka yi, ya kuma bukaci karin hadin kai a tsakanin al’umma da karin riko da koyarwar addinin Musulunci.

Manyan shawarwarin da akia cimma sun hada da:

Dakatar da Ofishin Khalifan Tijjaniya A Nijeriya

Labarai Masu Nasaba

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

A wata shawara mai cike da tarihi, an dakatar da tafiyar da ofishin Khalifan Tijjaniyyah a Nijeriya. Sanarwar ta kuma bayyana cewa, haka na tattare da komawar Khalifa Muhammad Sanusi II kan karagar sarautar Kano. Sheikh Mahy ya ce, an yanke wannan shawarar ce domin saukaka tafiyar da shugabanci a tsakanin ‘yan darikar Tijjaniyyah a fadin Nijeriya.

 

Manyan Shehunan Tijjaniyyah Za Su Ci Gaba da Tafiyar Da Al’amurra

A halin yanzu manyan Shaihunai biyu na Darikar Tijjaniyyah a Nijeriya, Sheikh Tahir Usman Bauchi da Sheikh Sharif Ibrahim Saleh Al-Husaini ne za su ci gaba da kula da al’amurra. “Iliminsu, basirarsu da tsayuwarsu zai taimaka wajen jagorantar mabiya darika a Nijeriya kamar yadda suka yi a shekarun da suka gabata,” in ji Khalifah.

 

Shugabancin Kwamitin Maulud Na Kasa

A halin yanzu, gudanar da Mauludin Sheikh Ibrahim Niasse na Nijeriya zai zama karkashin jagorancin Sheikh Mahy Niasse kai tsaye tare da hadin gwiwar sauran Shehunai da Mukaddamai domin tabbatar da nasarar gudanar da bikin Mauludin wanda ya zama wata kafa ta hadin kan mabiya Darikar Tijjaniyyah a fadin duniya.

 

Kafa Majalisar Darikar Tijjaniyyah Ta Duniya

A wani mataki na tabbatar da hadin kai na ‘yan Tijjaniyah a fadin duniya, an kafa ofishi na kasa da kasa da zai kula da yadda za mu yi nasarar kafa majalisar Darikar Tijjaniyah ta Duniya ‘World Tijjaniyyah Assembly’. Ta wannan ofishin da za a kafa majalisar, wannan majalisar za ta zama kafar karfafa hadin kai da aiki tare a tsakanin Shehunan Darikar Tijjaniyyah a fadin duniya da sauran mabiya akidoji daban-daban.

 

Wadannan shawarwarin sun zama wani sabon shafi ga ‘yan darikar Tijjaniyyah a fadin duniya. “Khalifa Sheikh Mahy Sheikh Ibrahim Niasse ya nemi dukakn ‘yan darika su hada kansu domin tabbatar da samun nasarar da aka sa a gaba. Ya kuma yi addu’ar Allah ya ba mu ikon aiwatar da wannan shawarwarin domin amfanar ‘yan darikar Tijjaniyyah da al’umma gaba daya,” in ji sanarwar.

 

Martanin ‘Yan Tijjaniyyah

An samu amincewa da murna a kan wadannan shawarwarin daga ‘yan darikar Tijjaniyyah a fadin Nijeriya. A tattaunawarsa da wannan jaridar, wani dan Tijjaniyyah daga Kano, Mallam Musa Bello, ya nuna jin dadinsa a kan shwarwarin: “Wannnan muhimman al’amura ne gare mu. Sheikh Tahir Usman Bauchi da Sheikh Shariff Saleh za su samar mana da jagorancin da ya kamata. Za kuma mu ci gaba da kasancewa tare da shugabancin Khalifa Niasse, musamman ganin yadda yake karfafa ‘yan Tijjaniyyah.”

 

Haka kum, sanannen malamin addnin musuluncin nan, Dakta Abdullahi Ahmad ya nuna jin dadinsa, musamman yadda ake shirin kafa ofishi na kasa da kasa “Wannan wani hangen nesa ne da zai karfafa ‘yan Tijjaniyyah tare da samar musu da murya daya a fadin duniya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Me Ya Sa Lee Hsien Loong Yake Da Karfin Gwiwa Kan Makomar Kasar Sin?

Next Post

Kasar Sin Za Ta Samar Da Ababen Hawa 100,000 Don Aikin Taksi Da Na Amfanin Kai Nan Da Shekarar 2030

Related

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

15 minutes ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

3 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

5 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

6 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

7 hours ago
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja
Labarai

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

9 hours ago
Next Post
Kasar Sin Za Ta Samar Da Ababen Hawa 100,000 Don Aikin Taksi Da Na Amfanin Kai Nan Da Shekarar 2030

Kasar Sin Za Ta Samar Da Ababen Hawa 100,000 Don Aikin Taksi Da Na Amfanin Kai Nan Da Shekarar 2030

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.