ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shehu Mahy Inyass Ya Sanar Da Sauye-sauye A Tafiyar Tijjaniya A Nijeriya

by Bello Hamza and Sulaiman
2 years ago
Mahy

A wani gaggarumar ci gaba da aka samu a tafiyar darikar Tijjaniya, Khalifa Sheikh Mahy Sheikh Ibrahim Inyass ya sanar da wasu sauye-sauye domin karfafa zumunci da hadin kai na darikar a fadin duniya baki daya, an bayyana haka ne a sanarwar da Khalifan ya fitar bayan tattaunawa tare da manyan masu ruwa da tsaki da manyan Shehunai.

 

Shawarar ta biyo bayan kammala bikin mauludin da aka yi na kwanan nan inda aka samu halartar ‘yan darikar Tijjaniyyah daga ko’ina a fadin duniya. Khalifa ya taya al’ummar Musulmai murnar wadannan bukukuwan da aka yi, ya kuma bukaci karin hadin kai a tsakanin al’umma da karin riko da koyarwar addinin Musulunci.

ADVERTISEMENT

Manyan shawarwarin da akia cimma sun hada da:

Dakatar da Ofishin Khalifan Tijjaniya A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

A wata shawara mai cike da tarihi, an dakatar da tafiyar da ofishin Khalifan Tijjaniyyah a Nijeriya. Sanarwar ta kuma bayyana cewa, haka na tattare da komawar Khalifa Muhammad Sanusi II kan karagar sarautar Kano. Sheikh Mahy ya ce, an yanke wannan shawarar ce domin saukaka tafiyar da shugabanci a tsakanin ‘yan darikar Tijjaniyyah a fadin Nijeriya.

 

Manyan Shehunan Tijjaniyyah Za Su Ci Gaba da Tafiyar Da Al’amurra

A halin yanzu manyan Shaihunai biyu na Darikar Tijjaniyyah a Nijeriya, Sheikh Tahir Usman Bauchi da Sheikh Sharif Ibrahim Saleh Al-Husaini ne za su ci gaba da kula da al’amurra. “Iliminsu, basirarsu da tsayuwarsu zai taimaka wajen jagorantar mabiya darika a Nijeriya kamar yadda suka yi a shekarun da suka gabata,” in ji Khalifah.

 

Shugabancin Kwamitin Maulud Na Kasa

A halin yanzu, gudanar da Mauludin Sheikh Ibrahim Niasse na Nijeriya zai zama karkashin jagorancin Sheikh Mahy Niasse kai tsaye tare da hadin gwiwar sauran Shehunai da Mukaddamai domin tabbatar da nasarar gudanar da bikin Mauludin wanda ya zama wata kafa ta hadin kan mabiya Darikar Tijjaniyyah a fadin duniya.

 

Kafa Majalisar Darikar Tijjaniyyah Ta Duniya

A wani mataki na tabbatar da hadin kai na ‘yan Tijjaniyah a fadin duniya, an kafa ofishi na kasa da kasa da zai kula da yadda za mu yi nasarar kafa majalisar Darikar Tijjaniyah ta Duniya ‘World Tijjaniyyah Assembly’. Ta wannan ofishin da za a kafa majalisar, wannan majalisar za ta zama kafar karfafa hadin kai da aiki tare a tsakanin Shehunan Darikar Tijjaniyyah a fadin duniya da sauran mabiya akidoji daban-daban.

 

Wadannan shawarwarin sun zama wani sabon shafi ga ‘yan darikar Tijjaniyyah a fadin duniya. “Khalifa Sheikh Mahy Sheikh Ibrahim Niasse ya nemi dukakn ‘yan darika su hada kansu domin tabbatar da samun nasarar da aka sa a gaba. Ya kuma yi addu’ar Allah ya ba mu ikon aiwatar da wannan shawarwarin domin amfanar ‘yan darikar Tijjaniyyah da al’umma gaba daya,” in ji sanarwar.

 

Martanin ‘Yan Tijjaniyyah

An samu amincewa da murna a kan wadannan shawarwarin daga ‘yan darikar Tijjaniyyah a fadin Nijeriya. A tattaunawarsa da wannan jaridar, wani dan Tijjaniyyah daga Kano, Mallam Musa Bello, ya nuna jin dadinsa a kan shwarwarin: “Wannnan muhimman al’amura ne gare mu. Sheikh Tahir Usman Bauchi da Sheikh Shariff Saleh za su samar mana da jagorancin da ya kamata. Za kuma mu ci gaba da kasancewa tare da shugabancin Khalifa Niasse, musamman ganin yadda yake karfafa ‘yan Tijjaniyyah.”

 

Haka kum, sanannen malamin addnin musuluncin nan, Dakta Abdullahi Ahmad ya nuna jin dadinsa, musamman yadda ake shirin kafa ofishi na kasa da kasa “Wannan wani hangen nesa ne da zai karfafa ‘yan Tijjaniyyah tare da samar musu da murya daya a fadin duniya.”

Mahy
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata
Mahy
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Kasar Sin Za Ta Samar Da Ababen Hawa 100,000 Don Aikin Taksi Da Na Amfanin Kai Nan Da Shekarar 2030

Kasar Sin Za Ta Samar Da Ababen Hawa 100,000 Don Aikin Taksi Da Na Amfanin Kai Nan Da Shekarar 2030

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.