• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shehu Mahy Inyass Ya Sanar Da Sauye-sauye A Tafiyar Tijjaniya A Nijeriya

by Bello Hamza and Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
Shehu Mahy Inyass Ya Sanar Da Sauye-sauye A Tafiyar Tijjaniya A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani gaggarumar ci gaba da aka samu a tafiyar darikar Tijjaniya, Khalifa Sheikh Mahy Sheikh Ibrahim Inyass ya sanar da wasu sauye-sauye domin karfafa zumunci da hadin kai na darikar a fadin duniya baki daya, an bayyana haka ne a sanarwar da Khalifan ya fitar bayan tattaunawa tare da manyan masu ruwa da tsaki da manyan Shehunai.

 

Shawarar ta biyo bayan kammala bikin mauludin da aka yi na kwanan nan inda aka samu halartar ‘yan darikar Tijjaniyyah daga ko’ina a fadin duniya. Khalifa ya taya al’ummar Musulmai murnar wadannan bukukuwan da aka yi, ya kuma bukaci karin hadin kai a tsakanin al’umma da karin riko da koyarwar addinin Musulunci.

Manyan shawarwarin da akia cimma sun hada da:

Dakatar da Ofishin Khalifan Tijjaniya A Nijeriya

Labarai Masu Nasaba

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

A wata shawara mai cike da tarihi, an dakatar da tafiyar da ofishin Khalifan Tijjaniyyah a Nijeriya. Sanarwar ta kuma bayyana cewa, haka na tattare da komawar Khalifa Muhammad Sanusi II kan karagar sarautar Kano. Sheikh Mahy ya ce, an yanke wannan shawarar ce domin saukaka tafiyar da shugabanci a tsakanin ‘yan darikar Tijjaniyyah a fadin Nijeriya.

 

Manyan Shehunan Tijjaniyyah Za Su Ci Gaba da Tafiyar Da Al’amurra

A halin yanzu manyan Shaihunai biyu na Darikar Tijjaniyyah a Nijeriya, Sheikh Tahir Usman Bauchi da Sheikh Sharif Ibrahim Saleh Al-Husaini ne za su ci gaba da kula da al’amurra. “Iliminsu, basirarsu da tsayuwarsu zai taimaka wajen jagorantar mabiya darika a Nijeriya kamar yadda suka yi a shekarun da suka gabata,” in ji Khalifah.

 

Shugabancin Kwamitin Maulud Na Kasa

A halin yanzu, gudanar da Mauludin Sheikh Ibrahim Niasse na Nijeriya zai zama karkashin jagorancin Sheikh Mahy Niasse kai tsaye tare da hadin gwiwar sauran Shehunai da Mukaddamai domin tabbatar da nasarar gudanar da bikin Mauludin wanda ya zama wata kafa ta hadin kan mabiya Darikar Tijjaniyyah a fadin duniya.

 

Kafa Majalisar Darikar Tijjaniyyah Ta Duniya

A wani mataki na tabbatar da hadin kai na ‘yan Tijjaniyah a fadin duniya, an kafa ofishi na kasa da kasa da zai kula da yadda za mu yi nasarar kafa majalisar Darikar Tijjaniyah ta Duniya ‘World Tijjaniyyah Assembly’. Ta wannan ofishin da za a kafa majalisar, wannan majalisar za ta zama kafar karfafa hadin kai da aiki tare a tsakanin Shehunan Darikar Tijjaniyyah a fadin duniya da sauran mabiya akidoji daban-daban.

 

Wadannan shawarwarin sun zama wani sabon shafi ga ‘yan darikar Tijjaniyyah a fadin duniya. “Khalifa Sheikh Mahy Sheikh Ibrahim Niasse ya nemi dukakn ‘yan darika su hada kansu domin tabbatar da samun nasarar da aka sa a gaba. Ya kuma yi addu’ar Allah ya ba mu ikon aiwatar da wannan shawarwarin domin amfanar ‘yan darikar Tijjaniyyah da al’umma gaba daya,” in ji sanarwar.

 

Martanin ‘Yan Tijjaniyyah

An samu amincewa da murna a kan wadannan shawarwarin daga ‘yan darikar Tijjaniyyah a fadin Nijeriya. A tattaunawarsa da wannan jaridar, wani dan Tijjaniyyah daga Kano, Mallam Musa Bello, ya nuna jin dadinsa a kan shwarwarin: “Wannnan muhimman al’amura ne gare mu. Sheikh Tahir Usman Bauchi da Sheikh Shariff Saleh za su samar mana da jagorancin da ya kamata. Za kuma mu ci gaba da kasancewa tare da shugabancin Khalifa Niasse, musamman ganin yadda yake karfafa ‘yan Tijjaniyyah.”

 

Haka kum, sanannen malamin addnin musuluncin nan, Dakta Abdullahi Ahmad ya nuna jin dadinsa, musamman yadda ake shirin kafa ofishi na kasa da kasa “Wannan wani hangen nesa ne da zai karfafa ‘yan Tijjaniyyah tare da samar musu da murya daya a fadin duniya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Me Ya Sa Lee Hsien Loong Yake Da Karfin Gwiwa Kan Makomar Kasar Sin?

Next Post

Kasar Sin Za Ta Samar Da Ababen Hawa 100,000 Don Aikin Taksi Da Na Amfanin Kai Nan Da Shekarar 2030

Related

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

13 hours ago
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
Rahotonni

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

13 hours ago
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa
Labarai

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

15 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

16 hours ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

17 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

18 hours ago
Next Post
Kasar Sin Za Ta Samar Da Ababen Hawa 100,000 Don Aikin Taksi Da Na Amfanin Kai Nan Da Shekarar 2030

Kasar Sin Za Ta Samar Da Ababen Hawa 100,000 Don Aikin Taksi Da Na Amfanin Kai Nan Da Shekarar 2030

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.