• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sheikh Dahiru Bauchi Ya Mara Wa Takarar Atiku Abubakar Baya

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Sheikh Dahiru Bauchi Ya Mara Wa Takarar Atiku Abubakar Baya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Malamin Darikar Tijjaniyya a Nijeriya, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya ayyana goyon bayan takarar Atiku Abubakar a matsayin shugaban kasa a zaben da za a fafata a ranar Asabar.

Sheikh Dahiru ce, zabin Atiku tamkar neman canji ne da halin da al’ummar kasar nan suka samu kansu a karkashin gwamnatin da ke ciki wato APC.

  • ‘Yan Bindiga Sun Harbe Shugaban APGA Har Lahira A Ebonyi
  • Tsarin MIDAS Ya Kawo Sauyin Yadda Ake Kula Da Iyakoki —Jere

Atiku dai shi ne dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP wanda ke neman kujerar tare da Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso na jam’iyyar NNPP, hadi da Peter Obi na LP gami da sauran.

A wani sakon sautin murya na ‘yan dakika da Shehin ya fitar da kuma wakilinmu ya tabbatar da ingancinsa daga hadiman Shehin, Sheikh ya ce, bai dace a cuci mumini har sau biyu a rami daya ba, don haka ne suke naman canji a kasar nan.

A sakon da ya aike wa ‘yan kasa na cewa: “Allah ya kawo mu lokacin zabe, jama’an kasa ‘yan uwana ‘yan Nijeriya. Annabi (S) yana cewa, bai kamata a ciji mumuni sau biyu a rami daya ba. Abu ya cijeka a wannan ramin to ya kamata ka dauki hannunka ka sanya a wani ramin kuma.

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

“Sabo da haka na ji wadansu mutane su na cewa a zabi wanda za a zaba ya daura mana a kan inda muka tsaya; to ai inda muka tsayan ba dadi muka ji balle mu daura a kai. Mutum sai ya ji dadi yake cewa a kara a mini, in bai ji dadi ba baya cewa a kara mini.

“Saboda haka ina wa’azi ina kira ina bada shawara a zabi inda za a samu canji ko Allah zai canza mana. Inda muka tsaya ba mu ji dadi ba balle a daura mana a kai.”

Dahiru Bauchi, ya ce, mutanensa sun fitar da Atiku a matsayin dan takararsu, don haka shi ma ya mara musu baya, “Mutane na sun bada shawarar cewa su Atiku za su zaba, ni kuma ba zan rabu da mutane ne ba. Zan nanata mutane ne da suke yin siyasa sun ce Atiku za su zaba tun da ga wanda za su zaba ba zan rabu da su ba ina tare da su. Allah ya zaba mana alkairi.”

Ya yi addu’ar cewa Allah sa a yi zaben lafiya a kammala lafiya kuma Allah sa a zabi shugabanni na kwarai da za su taimaki kasar nan, “Allah sa a samu shugaban da zai ji tausayin talakawa ba kamar yadda muka fito ba.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AtikuGoyon BayaSheikh Dahiru Usman BauchitakaraZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masanin NHC:Kusan An Kawo Karshen COVID-19 A Sin

Next Post

APC Ta Soki Sabon AIG Da Kwamishinonin ‘Yansanda 4 Kan Ziyartar Wike

Related

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

5 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

1 day ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

1 day ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

1 day ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

1 day ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

2 days ago
Next Post
APC Ta Soki Sabon AIG Da Kwamishinonin ‘Yansanda 4 Kan Ziyartar Wike

APC Ta Soki Sabon AIG Da Kwamishinonin 'Yansanda 4 Kan Ziyartar Wike

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.