• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sheikh Dahiru Bauchi Ya Mara Wa Takarar Atiku Abubakar Baya

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Sheikh Dahiru Bauchi Ya Mara Wa Takarar Atiku Abubakar Baya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Malamin Darikar Tijjaniyya a Nijeriya, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya ayyana goyon bayan takarar Atiku Abubakar a matsayin shugaban kasa a zaben da za a fafata a ranar Asabar.

Sheikh Dahiru ce, zabin Atiku tamkar neman canji ne da halin da al’ummar kasar nan suka samu kansu a karkashin gwamnatin da ke ciki wato APC.

  • ‘Yan Bindiga Sun Harbe Shugaban APGA Har Lahira A Ebonyi
  • Tsarin MIDAS Ya Kawo Sauyin Yadda Ake Kula Da Iyakoki —Jere

Atiku dai shi ne dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP wanda ke neman kujerar tare da Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso na jam’iyyar NNPP, hadi da Peter Obi na LP gami da sauran.

A wani sakon sautin murya na ‘yan dakika da Shehin ya fitar da kuma wakilinmu ya tabbatar da ingancinsa daga hadiman Shehin, Sheikh ya ce, bai dace a cuci mumini har sau biyu a rami daya ba, don haka ne suke naman canji a kasar nan.

A sakon da ya aike wa ‘yan kasa na cewa: “Allah ya kawo mu lokacin zabe, jama’an kasa ‘yan uwana ‘yan Nijeriya. Annabi (S) yana cewa, bai kamata a ciji mumuni sau biyu a rami daya ba. Abu ya cijeka a wannan ramin to ya kamata ka dauki hannunka ka sanya a wani ramin kuma.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

“Sabo da haka na ji wadansu mutane su na cewa a zabi wanda za a zaba ya daura mana a kan inda muka tsaya; to ai inda muka tsayan ba dadi muka ji balle mu daura a kai. Mutum sai ya ji dadi yake cewa a kara a mini, in bai ji dadi ba baya cewa a kara mini.

“Saboda haka ina wa’azi ina kira ina bada shawara a zabi inda za a samu canji ko Allah zai canza mana. Inda muka tsaya ba mu ji dadi ba balle a daura mana a kai.”

Dahiru Bauchi, ya ce, mutanensa sun fitar da Atiku a matsayin dan takararsu, don haka shi ma ya mara musu baya, “Mutane na sun bada shawarar cewa su Atiku za su zaba, ni kuma ba zan rabu da mutane ne ba. Zan nanata mutane ne da suke yin siyasa sun ce Atiku za su zaba tun da ga wanda za su zaba ba zan rabu da su ba ina tare da su. Allah ya zaba mana alkairi.”

Ya yi addu’ar cewa Allah sa a yi zaben lafiya a kammala lafiya kuma Allah sa a zabi shugabanni na kwarai da za su taimaki kasar nan, “Allah sa a samu shugaban da zai ji tausayin talakawa ba kamar yadda muka fito ba.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AtikuGoyon BayaSheikh Dahiru Usman BauchitakaraZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masanin NHC:Kusan An Kawo Karshen COVID-19 A Sin

Next Post

APC Ta Soki Sabon AIG Da Kwamishinonin ‘Yansanda 4 Kan Ziyartar Wike

Related

Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

4 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

7 hours ago
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Manyan Labarai

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

8 hours ago
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
Manyan Labarai

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

10 hours ago
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

24 hours ago
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?
Manyan Labarai

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

1 day ago
Next Post
APC Ta Soki Sabon AIG Da Kwamishinonin ‘Yansanda 4 Kan Ziyartar Wike

APC Ta Soki Sabon AIG Da Kwamishinonin 'Yansanda 4 Kan Ziyartar Wike

LABARAI MASU NASABA

Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

September 15, 2025
Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

September 15, 2025
Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

September 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.