• English
  • Business News
Thursday, July 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara Ɗaya A Ofis: An Buɗe Gasar Cin Kofin Babban Hafsan Sojojin Nijeriya A Katsina

by Muhammad and El-Zaharadeen Umar
1 year ago
in Labarai, Wasanni
0
Shekara Ɗaya A Ofis: An Buɗe Gasar Cin Kofin Babban Hafsan Sojojin Nijeriya A Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An buɗe gasar kwallon kafa ta cin kofin baban Hafsan Sojojin Nijeriya a Katsina domin taya shi murnar cika shekara ɗaya a ofis.

An shirya gasar ne da nufin ƙara kyautata alaƙa a tsakanin matasa, inda kulob 32 za su fafata a filin wasa na birget na 17 da kuma filin wasa na KCK da ke Katsina.

  • Ƴan Bindiga Sun Kai Farmaki, Sun Yi Kisa, Sun Kwashe Mutune 22 A Katsina
  • Jami’ar ‘Yar’aduwa Ta Katsina Ta Kama Hanyar Rugujewa – ASUU

Tunda farko da yake jawabi a taron bikin buɗe gasar, baban kwamanda mai kula da Birget na 17 da ke Katsina, Ibikunle Ademola Ajose, ya bayyana cewa shirya irin waɗannan wassani abu ne mai kyau, domin ta haka ne za a ƙara kulla alaƙa a tsakanin matasa.

Ya ƙara da cewa waɗanda suka shirya wannan gasa sun yi hangen nesa, kuma sun yi abin da yakamata a lokacin da ya dace, musamman don tunawa da shi babban Hafsan Sojojin Nijeriya, Christopher Gwabin Musa
.
A cewar baban kwamanda mai kula da birget na 17, Ibikunle Ademola, yana fatan za a yi wannan gasa a kammala cikin nasara ba tare da wata matsala ba, musamman tun da abin ya haɗa da matasa.

A wajen wannan biki dai kungiyoyin kwallo guda biyu ne suka kara, wato Sarkin Yaki da kuma K-Soro, wanda bayan an fafata daga ƙarshe kungiyar kwallon kafa ta K-Soro ta samu nasara da bugun daga kai sai mia tsaron gida.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

Dubun Wasu Mutane 20 Da Ake Zargi Da Safarar Makamai A Kwara Ta Cika

Yanzu dai za a ci gaba da waɗannan wassani a filin wasa na KCK, inda ake sa ran sauran kolab ɗin za su nuna bajintar su domin samun nasara a ƙarshen gasar.

A nasa jawabin, shugaban shirya wannan gasa domin taya baban Hafsan Sojojin Nijeriya, Janar Christopher Gwabin Musa, Malam Lawal BK ya bayyana cewa sun yi tunanin shirya gasar ne domin sada zumunci a tsakanin matasa.

Ya ƙara da cewa yanzu hanya mafi sauki da za a ja matasa a jiki, ita ce shirya irin wannan gasa, ya ce babu komai za a ɗora matasa a wata turba wadda za ta hana su yin tunanin abubuwa marasa kyau.

“Matasan mu yanzu idan ka kyale su, ba zamu yi tunanin irin wanda yakamata ba, amma shi wasan ƙwallon ƙafa abu ne da matasa ke so, to ko ba komi ka ɗebe masu kewa sannan ka sanya su nishadi ” inji shi

Kamar yadda aka tsara kungiyoyin kwallo kafa guda 32 ne za su fafata kuma wasa daya ne za a riƙa bugawa duk wanda ya samu nasara zai hau mataki na gaba.

Kazalika an ware kyaututtuka masu yawa wanda a ƙarshen gasar za a rabawa kungiyar da ta samu nasara.

Sauran kungiyoyin kwallon kafar da za su taka leda sun haɗa da Katsina Boys da Shooting Star da Durbi Strikers da KKT Strikers da Home Boys da Gawo Prof. da kuma Kamuwa United da Manaco ATC da dai sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Babban Hafsoshin Sojojin NijeriyaGasaKatsinaKwallon Kafa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ƴan Bindiga Sun Kai Farmaki, Sun Yi Kisa, Sun Kwashe Mutune 22 A Katsina

Next Post

Sojoji Da Mafarauta Sun Dakile Shirin ‘Yan Ta’adda Na Lalata Falwayar Wutar Lantarki A Yobe

Related

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi
Labarai

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

7 hours ago
Dubun Wasu Mutane 20 Da Ake Zargi Da Safarar Makamai A Kwara Ta Cika
Labarai

Dubun Wasu Mutane 20 Da Ake Zargi Da Safarar Makamai A Kwara Ta Cika

8 hours ago
PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde
Labarai

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

10 hours ago
Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025
Labarai

Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025

11 hours ago
Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili
Manyan Labarai

Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

14 hours ago
Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya
Manyan Labarai

Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya

15 hours ago
Next Post
Sojoji Da Mafarauta Sun Dakile Shirin ‘Yan Ta’adda Na Lalata Falwayar Wutar Lantarki A Yobe

Sojoji Da Mafarauta Sun Dakile Shirin ‘Yan Ta'adda Na Lalata Falwayar Wutar Lantarki A Yobe

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

July 16, 2025
Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

July 16, 2025
Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin

Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin

July 16, 2025
Dubun Wasu Mutane 20 Da Ake Zargi Da Safarar Makamai A Kwara Ta Cika

Dubun Wasu Mutane 20 Da Ake Zargi Da Safarar Makamai A Kwara Ta Cika

July 16, 2025
Jarin Kasar Sin Ya Bada Gudunmawa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Zimbabwe

Jarin Kasar Sin Ya Bada Gudunmawa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Zimbabwe

July 16, 2025
Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya

Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya

July 16, 2025
An Gudanar Da Taron Ministocin Wajen Kasashe Mambobin SCO A Tianjin

An Gudanar Da Taron Ministocin Wajen Kasashe Mambobin SCO A Tianjin

July 16, 2025
PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

July 16, 2025
Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka

Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka

July 16, 2025
Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025

Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025

July 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.