• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekarar Musulunci: Kiristoci Sun Bukaci A Bayar Da Hutu

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
Shekarar Musulunci: Kiristoci Sun Bukaci A Bayar Da Hutu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da ake shirin shiga sabuwar shekarar Musulunci a watan na Al- Muharram, wadda ke nuna kawo karshen shekara, tawagar mabiya Malaman addinin Kirista a jihar Kaduna, sun taya mabiya Addinin Musulunci da ke a fadin kasar nan murnar shirin shiga sabuwar shekara.

Kazalika, sun shawarce su da su kara yin kaimi wajen yin addu’oin samun zaman lafiya da hadin kai.

  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Wa Dahiru Mangal Jajen Rasuwar Matarsa
  • Gwamnan Bauchi Ya Rushe Shugabannin Riko Na Kananan Hukumomi

Fitaccen Fasto a jihar, Yohanna Buru ne, ya isar da sakon malaman mabiya addinin kirista a yayin da tawagar matasa Musulmi suka kai masa ziyara a gidansa da ke unguwar Sabon Tasha a Kaduna.

Matasan sun kai masa wannan ziyarar ne, bisa nufin kara karfafa dankon zumunci a tsakanin matasa mabiya addinin biyu da kuma kara wanzar da zaman lafiya a jihar.

Ziyarar ta su dai, ta zo ne daidai da zagayowar bikin ranar abota ta duniya da aka saba gudanarwa a duk ranar 30 ga watan Yulin kowacce shekara.

Labarai Masu Nasaba

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Buru ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta ayyana ranar shiga sabuwar shekarar ta Musulunci a matsayin ranar hutu ga Musulmi don Musulmi su gudanar da shagulgulan bakin ranar, mussaman ganin tuni, wasu jihohin da ke a kasar, tuni suka ayyana ranar a matsayin ranar hutu ga Musulmin da ke a jihohin su.

Sai dai, ya koka ganin cewa, Musulmin kasar nan, za su shigo cikin watan na Muharram dai dai da lokacin da ake ci gaba da samun tashin gwauron Zabi na kayan masarufi a kasar.

Ya yi kira ga Musulmi da su tallafa wa marasa karfi, marayu da mata zawarawa da kayan abinci a lokacin gudanar da bukukuwan bikin zagoyowar shekarar ta Musulunci.

Shi ma a na sa jawabin a lokacin ziyarar Fasto John Joseph, ya nanata mahimmancin zaman lafiya a daukacin fadin kasar nan.

Kazalika, ya yi kira, musamman ga matasa mabiya addinan biyu, da su gujewa furta kalaman kiyayya, su kuma rungumi dabi’ar son zaman lafiya a tsakaninsu.

Shi kuwa, shugaban kungiyar matasan Musulmi reshen jihar, Mallam Gambo Abdullahi Barnawa, ya godewa malaman mabiya addinin Kirista kan taya Musulmi murnar shiga sabuwar shekara, inda ya yi addu’ar kara dangon zumunci a tsakanin mabiya addinin biyu da ke fadin Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KiristociMalamaiMusulmiShekarar Musulunci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnonin Arewa Sun Yi Wa Dahiru Mangal Jajen Rasuwar Matarsa

Next Post

Xi Ya Tattauna Da Shugaban Aljeriya

Related

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

5 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

8 hours ago
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo
Labarai

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

11 hours ago
Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet
Labarai

Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet

13 hours ago
Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka
Manyan Labarai

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

15 hours ago
Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 
Manyan Labarai

Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

19 hours ago
Next Post
Xi Ya Tattauna Da Shugaban Aljeriya

Xi Ya Tattauna Da Shugaban Aljeriya

LABARAI MASU NASABA

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

August 21, 2025
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

August 21, 2025
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

August 21, 2025
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.