• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekarar Musulunci: Kiristoci Sun Bukaci A Bayar Da Hutu

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
Shekarar Musulunci: Kiristoci Sun Bukaci A Bayar Da Hutu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da ake shirin shiga sabuwar shekarar Musulunci a watan na Al- Muharram, wadda ke nuna kawo karshen shekara, tawagar mabiya Malaman addinin Kirista a jihar Kaduna, sun taya mabiya Addinin Musulunci da ke a fadin kasar nan murnar shirin shiga sabuwar shekara.

Kazalika, sun shawarce su da su kara yin kaimi wajen yin addu’oin samun zaman lafiya da hadin kai.

  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Wa Dahiru Mangal Jajen Rasuwar Matarsa
  • Gwamnan Bauchi Ya Rushe Shugabannin Riko Na Kananan Hukumomi

Fitaccen Fasto a jihar, Yohanna Buru ne, ya isar da sakon malaman mabiya addinin kirista a yayin da tawagar matasa Musulmi suka kai masa ziyara a gidansa da ke unguwar Sabon Tasha a Kaduna.

Matasan sun kai masa wannan ziyarar ne, bisa nufin kara karfafa dankon zumunci a tsakanin matasa mabiya addinin biyu da kuma kara wanzar da zaman lafiya a jihar.

Ziyarar ta su dai, ta zo ne daidai da zagayowar bikin ranar abota ta duniya da aka saba gudanarwa a duk ranar 30 ga watan Yulin kowacce shekara.

Labarai Masu Nasaba

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

Buru ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta ayyana ranar shiga sabuwar shekarar ta Musulunci a matsayin ranar hutu ga Musulmi don Musulmi su gudanar da shagulgulan bakin ranar, mussaman ganin tuni, wasu jihohin da ke a kasar, tuni suka ayyana ranar a matsayin ranar hutu ga Musulmin da ke a jihohin su.

Sai dai, ya koka ganin cewa, Musulmin kasar nan, za su shigo cikin watan na Muharram dai dai da lokacin da ake ci gaba da samun tashin gwauron Zabi na kayan masarufi a kasar.

Ya yi kira ga Musulmi da su tallafa wa marasa karfi, marayu da mata zawarawa da kayan abinci a lokacin gudanar da bukukuwan bikin zagoyowar shekarar ta Musulunci.

Shi ma a na sa jawabin a lokacin ziyarar Fasto John Joseph, ya nanata mahimmancin zaman lafiya a daukacin fadin kasar nan.

Kazalika, ya yi kira, musamman ga matasa mabiya addinan biyu, da su gujewa furta kalaman kiyayya, su kuma rungumi dabi’ar son zaman lafiya a tsakaninsu.

Shi kuwa, shugaban kungiyar matasan Musulmi reshen jihar, Mallam Gambo Abdullahi Barnawa, ya godewa malaman mabiya addinin Kirista kan taya Musulmi murnar shiga sabuwar shekara, inda ya yi addu’ar kara dangon zumunci a tsakanin mabiya addinin biyu da ke fadin Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KiristociMalamaiMusulmiShekarar Musulunci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnonin Arewa Sun Yi Wa Dahiru Mangal Jajen Rasuwar Matarsa

Next Post

Xi Ya Tattauna Da Shugaban Aljeriya

Related

Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

38 minutes ago
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS
Labarai

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

3 hours ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

5 hours ago
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

6 hours ago
Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan
Labarai

Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

6 hours ago
Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja
Tsaro

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

7 hours ago
Next Post
Xi Ya Tattauna Da Shugaban Aljeriya

Xi Ya Tattauna Da Shugaban Aljeriya

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

June 27, 2025
An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

June 27, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

June 27, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

June 27, 2025
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

June 27, 2025
WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

June 27, 2025
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

June 27, 2025
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.