ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekarar Musulunci: Kiristoci Sun Bukaci A Bayar Da Hutu

by Abubakar Abba
3 years ago
Shekarar Musulunci

A yayin da ake shirin shiga sabuwar shekarar Musulunci a watan na Al- Muharram, wadda ke nuna kawo karshen shekara, tawagar mabiya Malaman addinin Kirista a jihar Kaduna, sun taya mabiya Addinin Musulunci da ke a fadin kasar nan murnar shirin shiga sabuwar shekara.

Kazalika, sun shawarce su da su kara yin kaimi wajen yin addu’oin samun zaman lafiya da hadin kai.

  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Wa Dahiru Mangal Jajen Rasuwar Matarsa
  • Gwamnan Bauchi Ya Rushe Shugabannin Riko Na Kananan Hukumomi

Fitaccen Fasto a jihar, Yohanna Buru ne, ya isar da sakon malaman mabiya addinin kirista a yayin da tawagar matasa Musulmi suka kai masa ziyara a gidansa da ke unguwar Sabon Tasha a Kaduna.

ADVERTISEMENT

Matasan sun kai masa wannan ziyarar ne, bisa nufin kara karfafa dankon zumunci a tsakanin matasa mabiya addinin biyu da kuma kara wanzar da zaman lafiya a jihar.

Ziyarar ta su dai, ta zo ne daidai da zagayowar bikin ranar abota ta duniya da aka saba gudanarwa a duk ranar 30 ga watan Yulin kowacce shekara.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

Buru ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta ayyana ranar shiga sabuwar shekarar ta Musulunci a matsayin ranar hutu ga Musulmi don Musulmi su gudanar da shagulgulan bakin ranar, mussaman ganin tuni, wasu jihohin da ke a kasar, tuni suka ayyana ranar a matsayin ranar hutu ga Musulmin da ke a jihohin su.

Sai dai, ya koka ganin cewa, Musulmin kasar nan, za su shigo cikin watan na Muharram dai dai da lokacin da ake ci gaba da samun tashin gwauron Zabi na kayan masarufi a kasar.

Ya yi kira ga Musulmi da su tallafa wa marasa karfi, marayu da mata zawarawa da kayan abinci a lokacin gudanar da bukukuwan bikin zagoyowar shekarar ta Musulunci.

Shi ma a na sa jawabin a lokacin ziyarar Fasto John Joseph, ya nanata mahimmancin zaman lafiya a daukacin fadin kasar nan.

Kazalika, ya yi kira, musamman ga matasa mabiya addinan biyu, da su gujewa furta kalaman kiyayya, su kuma rungumi dabi’ar son zaman lafiya a tsakaninsu.

Shi kuwa, shugaban kungiyar matasan Musulmi reshen jihar, Mallam Gambo Abdullahi Barnawa, ya godewa malaman mabiya addinin Kirista kan taya Musulmi murnar shiga sabuwar shekara, inda ya yi addu’ar kara dangon zumunci a tsakanin mabiya addinin biyu da ke fadin Nijeriya.

Shekarar Musulunci
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
Manyan Labarai

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Next Post
Xi Ya Tattauna Da Shugaban Aljeriya

Xi Ya Tattauna Da Shugaban Aljeriya

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.