ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekarar Musulunci: Kiristoci Sun Bukaci A Bayar Da Hutu

by Abubakar Abba
3 years ago
Shekarar Musulunci

A yayin da ake shirin shiga sabuwar shekarar Musulunci a watan na Al- Muharram, wadda ke nuna kawo karshen shekara, tawagar mabiya Malaman addinin Kirista a jihar Kaduna, sun taya mabiya Addinin Musulunci da ke a fadin kasar nan murnar shirin shiga sabuwar shekara.

Kazalika, sun shawarce su da su kara yin kaimi wajen yin addu’oin samun zaman lafiya da hadin kai.

  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Wa Dahiru Mangal Jajen Rasuwar Matarsa
  • Gwamnan Bauchi Ya Rushe Shugabannin Riko Na Kananan Hukumomi

Fitaccen Fasto a jihar, Yohanna Buru ne, ya isar da sakon malaman mabiya addinin kirista a yayin da tawagar matasa Musulmi suka kai masa ziyara a gidansa da ke unguwar Sabon Tasha a Kaduna.

ADVERTISEMENT

Matasan sun kai masa wannan ziyarar ne, bisa nufin kara karfafa dankon zumunci a tsakanin matasa mabiya addinin biyu da kuma kara wanzar da zaman lafiya a jihar.

Ziyarar ta su dai, ta zo ne daidai da zagayowar bikin ranar abota ta duniya da aka saba gudanarwa a duk ranar 30 ga watan Yulin kowacce shekara.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Buru ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta ayyana ranar shiga sabuwar shekarar ta Musulunci a matsayin ranar hutu ga Musulmi don Musulmi su gudanar da shagulgulan bakin ranar, mussaman ganin tuni, wasu jihohin da ke a kasar, tuni suka ayyana ranar a matsayin ranar hutu ga Musulmin da ke a jihohin su.

Sai dai, ya koka ganin cewa, Musulmin kasar nan, za su shigo cikin watan na Muharram dai dai da lokacin da ake ci gaba da samun tashin gwauron Zabi na kayan masarufi a kasar.

Ya yi kira ga Musulmi da su tallafa wa marasa karfi, marayu da mata zawarawa da kayan abinci a lokacin gudanar da bukukuwan bikin zagoyowar shekarar ta Musulunci.

Shi ma a na sa jawabin a lokacin ziyarar Fasto John Joseph, ya nanata mahimmancin zaman lafiya a daukacin fadin kasar nan.

Kazalika, ya yi kira, musamman ga matasa mabiya addinan biyu, da su gujewa furta kalaman kiyayya, su kuma rungumi dabi’ar son zaman lafiya a tsakaninsu.

Shi kuwa, shugaban kungiyar matasan Musulmi reshen jihar, Mallam Gambo Abdullahi Barnawa, ya godewa malaman mabiya addinin Kirista kan taya Musulmi murnar shiga sabuwar shekara, inda ya yi addu’ar kara dangon zumunci a tsakanin mabiya addinin biyu da ke fadin Nijeriya.

Shekarar Musulunci
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027
Labarai

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
Xi Ya Tattauna Da Shugaban Aljeriya

Xi Ya Tattauna Da Shugaban Aljeriya

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.