• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekaru 60: DICON Ta Taimaka Wajen Samar Mana Da Makamai – Janar Musa

by Sadiq
1 year ago
in Labarai
0
Shekaru 60: DICON Ta Taimaka Wajen Samar Mana Da Makamai – Janar Musa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Hafsan rundunar tsaron Nijeriya, Janar Christopher Gwabin Musa, ya bayyana cewa ma’aikatar sarrarafa makamai ta Nijeriya (DICON), ta taimaka wajen samar wa rundunar kayayyakin aiki.

Kayayyakin sun sun hada da motocin yaki da kayayyakin sulken da rundunar soji ke bukata na aikin samar da tsaro a kasar.

  • Birtaniya Za Ta Wahala Idan Likitocin Nijeriya Suka Bar Kasar – Ministan Lafiya
  • Ban Taɓa Karɓar Cin Hanci Ko Taɓa Ƙuɗin Ƙananan Hukumomi Ba – Shekarau

Janar Musa, ya bayyana hakan ne, a taron kwanaki biyu da aka soma yau a Abuja na cikar ma’aikatar ta DICON shekaru 60 da kafuwa.

Nasarorin da ma’aikatar ta samu ba ya rasa nasaba da sanya hannu kan dokar ma’aikatar ta shekarar 2023 da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya rattaba hannu a kai a watan Nuwamban 2023.

Idan ba a manta ba, ya bai wa ma’aikatar damar cimma manyan nasarori gami da fadada ayyukanta domin ci gaban Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Tun da fari dai, Karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, ya bayyana cewa assasa ma’aikatar sarrafa makaman a shekarar 1964 alamu ne na cin gashin-kai da Nijeriya ta tabbatar, wajen harkokin tsaro da ci gaban kasa.

Ma’aikatar ta zama silar nasarar ayyukan tsaro a kasar tare da fara sayar wa kasashen ketare makamai.

A shekarun da ta kwashe, ma’aikatar ta yi namijin kokari wajen shimfida kyakkyawar manhajar samar da tsaro a kasar.

Sannan ta taimaka wa rundunar tsaron Nujeriya da kayayyaki, domin saukaka ayyukansu na tsaro.

Ministan, ya bayyana cewa ko shakka babu, a karkashin mulkin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ma’aikatar za ta ci gaba da samar da nasarori a wannan fannin tsaro.

A nasa jawabinsa, Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, wanda sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume, ya wakilta, ya ce shekaru 60 da kafuwar ma’aikatar sarrafa makamai alamu ne na tabbatar da tsantsar kishin kasa a harkar tsaro.

Shekaru 60 da suka gabata, ma’aikatar DICON ta himmatu ne, wajen sarrafa makamai da kayan yaki domin taimaka wa rundunar tsaro da sauran ma’aikatun tsaron Nijeriya a kokarinsu na wanzar da zaman lafiya a kasa baki daya.

Shugaban ya ce, hakika ma’aikatar DICON ta taka muhimmiyar rawa a samar wa dakarun Nijeriya da kayan aiki a lokacin yakin basasa domin tabbatar da kasantuwar Nijeriya kasa daya mai cin gashin-kanta.

Shugaba Tinubu, ya kara yin kira ga jagororin ma’aikatar da su kara himma da fadada tunani ga samar da kayayyakin zamani a shirin gwamnati na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’ummar kasar nan.

Har wa yau, ya yi kira ga ‘yan kasa su taimaka su bayar da goyon baya ga nasarar ma’aikatar.

Daga bisani, shugaban ya kaddamar da sabon tambarin ma’aikatar tare da littafi na musamman da aka wallafa na cikar DICON shekaru 60 da kafuwa.

Taron, ya samu halartar ministoci, shugabannin tsaro da jami’an kasashen waje da kamfanoni da manazarta harkokin tsaro da ‘yan jarida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DICONJanar MusaMa'aikataMatawalleMinistaTaroTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Birtaniya Za Ta Wahala Idan Likitocin Nijeriya Suka Bar Kasar – Ministan Lafiya

Next Post

WATA SABUWA: Ganduje Ya Nuna Rashin Jin Daɗi Bayan Tinubu Ya Masa Tayin Muƙamin Jakada

Related

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

14 minutes ago
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

1 hour ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

4 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya
Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

5 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

6 hours ago
Next Post
WATA SABUWA: Ganduje Ya Nuna Rashin Jin Daɗi Bayan Tinubu Ya Masa Tayin Muƙamin Jakada

WATA SABUWA: Ganduje Ya Nuna Rashin Jin Daɗi Bayan Tinubu Ya Masa Tayin Muƙamin Jakada

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.