• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekaru 60: DICON Ta Taimaka Wajen Samar Mana Da Makamai – Janar Musa

by Sadiq
1 year ago
in Labarai
0
Shekaru 60: DICON Ta Taimaka Wajen Samar Mana Da Makamai – Janar Musa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Hafsan rundunar tsaron Nijeriya, Janar Christopher Gwabin Musa, ya bayyana cewa ma’aikatar sarrarafa makamai ta Nijeriya (DICON), ta taimaka wajen samar wa rundunar kayayyakin aiki.

Kayayyakin sun sun hada da motocin yaki da kayayyakin sulken da rundunar soji ke bukata na aikin samar da tsaro a kasar.

  • Birtaniya Za Ta Wahala Idan Likitocin Nijeriya Suka Bar Kasar – Ministan Lafiya
  • Ban TaÉ“a KarÉ“ar Cin Hanci Ko TaÉ“a ƘuÉ—in Ƙananan Hukumomi Ba – Shekarau

Janar Musa, ya bayyana hakan ne, a taron kwanaki biyu da aka soma yau a Abuja na cikar ma’aikatar ta DICON shekaru 60 da kafuwa.

Nasarorin da ma’aikatar ta samu ba ya rasa nasaba da sanya hannu kan dokar ma’aikatar ta shekarar 2023 da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya rattaba hannu a kai a watan Nuwamban 2023.

Idan ba a manta ba, ya bai wa ma’aikatar damar cimma manyan nasarori gami da fadada ayyukanta domin ci gaban Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Tun da fari dai, Karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, ya bayyana cewa assasa ma’aikatar sarrafa makaman a shekarar 1964 alamu ne na cin gashin-kai da Nijeriya ta tabbatar, wajen harkokin tsaro da ci gaban kasa.

Ma’aikatar ta zama silar nasarar ayyukan tsaro a kasar tare da fara sayar wa kasashen ketare makamai.

A shekarun da ta kwashe, ma’aikatar ta yi namijin kokari wajen shimfida kyakkyawar manhajar samar da tsaro a kasar.

Sannan ta taimaka wa rundunar tsaron Nujeriya da kayayyaki, domin saukaka ayyukansu na tsaro.

Ministan, ya bayyana cewa ko shakka babu, a karkashin mulkin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ma’aikatar za ta ci gaba da samar da nasarori a wannan fannin tsaro.

A nasa jawabinsa, Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, wanda sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume, ya wakilta, ya ce shekaru 60 da kafuwar ma’aikatar sarrafa makamai alamu ne na tabbatar da tsantsar kishin kasa a harkar tsaro.

Shekaru 60 da suka gabata, ma’aikatar DICON ta himmatu ne, wajen sarrafa makamai da kayan yaki domin taimaka wa rundunar tsaro da sauran ma’aikatun tsaron Nijeriya a kokarinsu na wanzar da zaman lafiya a kasa baki daya.

Shugaban ya ce, hakika ma’aikatar DICON ta taka muhimmiyar rawa a samar wa dakarun Nijeriya da kayan aiki a lokacin yakin basasa domin tabbatar da kasantuwar Nijeriya kasa daya mai cin gashin-kanta.

Shugaba Tinubu, ya kara yin kira ga jagororin ma’aikatar da su kara himma da fadada tunani ga samar da kayayyakin zamani a shirin gwamnati na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’ummar kasar nan.

Har wa yau, ya yi kira ga ‘yan kasa su taimaka su bayar da goyon baya ga nasarar ma’aikatar.

Daga bisani, shugaban ya kaddamar da sabon tambarin ma’aikatar tare da littafi na musamman da aka wallafa na cikar DICON shekaru 60 da kafuwa.

Taron, ya samu halartar ministoci, shugabannin tsaro da jami’an kasashen waje da kamfanoni da manazarta harkokin tsaro da ‘yan jarida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DICONJanar MusaMa'aikataMatawalleMinistaTaroTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Birtaniya Za Ta Wahala Idan Likitocin Nijeriya Suka Bar Kasar – Ministan Lafiya

Next Post

WATA SABUWA: Ganduje Ya Nuna Rashin Jin Daɗi Bayan Tinubu Ya Masa Tayin Muƙamin Jakada

Related

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

10 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

15 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

16 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da ÆŠansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

17 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da ÆŠansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

18 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

19 hours ago
Next Post
WATA SABUWA: Ganduje Ya Nuna Rashin Jin Daɗi Bayan Tinubu Ya Masa Tayin Muƙamin Jakada

WATA SABUWA: Ganduje Ya Nuna Rashin Jin Daɗi Bayan Tinubu Ya Masa Tayin Muƙamin Jakada

LABARAI MASU NASABA

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.