ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

WATA SABUWA: Ganduje Ya Nuna Rashin Jin Daɗi Bayan Tinubu Ya Masa Tayin Muƙamin Jakada

by Naziru Adam Ibrahim
2 years ago
Ganduje

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu, ya yi wa shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Ganduje, tayin muƙamin jakada a ɗaya daga ƙasashen Afrika, kamar yadda wata majiya mai tushe ta tabbatar.

Kazalika, majiyar ta ce shugaban ya wakilta shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio ya sanar da Ganduje.

  • Shekaru 60: DICON Ta Taimaka Wajen Samar Mana Da Makamai – Janar Musa
  • Shugaban Majalisa Ya Janye Ƙudirin Dokar Dauri Ga Wanda Ya Ki Rera Taken Nijeriya

An naɗa Ganduje, a matsayin shugaban jam’iyyar APC na ƙasa a ranar 3 ga watan Agusta 2023, biyo bayan murabus ɗin da Abdullahi Adamu.

ADVERTISEMENT

A cewar majiyar Akpabio, ya shaida wa Ganduje tayin shugaban ƙasar na da nufin ceto shi daga shari’ar cin hanci da rashawa da yake fuskanta a Kano game da faifan bidiyon Dala na shekarar 2018.

Ya ce bidiyon ya janyo masa ba’a da gori a bainar jama’a, tare da matarsa da ɗansa da kuma sauran masu hannu cikin lamarin na sama da Naira biliyan 50.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Sai dai wata majiya, ta ce Ganduje ya ƙi amincewa da tayin, inda ya bayyana cewa zargin ƙarya ne, kuma zai yi nasara a shari’arsa a kotu wanda shugaban Tinubu da kansa ya sanar da Ganduje shiri na diflomasiyya tare da ba shi damar zaɓar wata ƙasa a Afirka.

Wata majiya ta kusa da Ganduje ta ce abin da shugaba Tinubu, ya fi so shi ne ya naɗa shi Jakadan Nijeriya a ƙasar Chadi, duba da cewar ya taɓa yin aiki a Ndjamena a matsayin babban sakataren hukumar kula da tafkin Chadi tsakanin 2009 zuwa 2011.

Jaridar Daily Nigeria ta ruwaito cewa kwanaki kaɗan bayan Shugaba Tinubu ya sanar da matakin ga Ganduje, an aike masa da wasiƙar wa’adi game da buƙatar ya gudanar da babban taron majalisar jam’iyyar APC na ƙasa.

Wasikar mai ɗauke da kwanan wata 9 ga watan Agusta, da sa hannun Shugaban Hadiman Tinubu, Femi Gbajabiamila, ta sanar da Ganduje cewa shugaban ƙasa zai samu halartar taron Majalisar Jam’iyyar a ranar 8 zuwa 19 ga Satumba, 2024.

Ko da aka tuntuɓi mai magana da yawun Ganduje, Edwin Olofu, ya ce mai gidansa bai yi masa bayani kan batun ba amma ya tabbatar da amincewar shugaban ƙasa na a gudanar da babban taron jam’iyyar.

Ganduje
Naziru Adam Ibrahim
+ postsBio
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Ya Kamata Farashin Siminti Ya Sauka — Umahi Ga Masana’antun Siminti
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Shugaba Tinubu Ya Isa Nairobi Domin Halartar Taron Tattalin Arzikin Nahiyar Afirka

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
KANSIEC Ta Sanya 10m A Matsayin Kuɗin Fom Na Takarar Ciyaman A Kano

KANSIEC Ta Sanya 10m A Matsayin Kuɗin Fom Na Takarar Ciyaman A Kano

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.