ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

WATA SABUWA: Ganduje Ya Nuna Rashin Jin Daɗi Bayan Tinubu Ya Masa Tayin Muƙamin Jakada

by Naziru Adam Ibrahim
2 years ago
Ganduje

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu, ya yi wa shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Ganduje, tayin muƙamin jakada a ɗaya daga ƙasashen Afrika, kamar yadda wata majiya mai tushe ta tabbatar.

Kazalika, majiyar ta ce shugaban ya wakilta shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio ya sanar da Ganduje.

  • Shekaru 60: DICON Ta Taimaka Wajen Samar Mana Da Makamai – Janar Musa
  • Shugaban Majalisa Ya Janye Ƙudirin Dokar Dauri Ga Wanda Ya Ki Rera Taken Nijeriya

An naɗa Ganduje, a matsayin shugaban jam’iyyar APC na ƙasa a ranar 3 ga watan Agusta 2023, biyo bayan murabus ɗin da Abdullahi Adamu.

ADVERTISEMENT

A cewar majiyar Akpabio, ya shaida wa Ganduje tayin shugaban ƙasar na da nufin ceto shi daga shari’ar cin hanci da rashawa da yake fuskanta a Kano game da faifan bidiyon Dala na shekarar 2018.

Ya ce bidiyon ya janyo masa ba’a da gori a bainar jama’a, tare da matarsa da ɗansa da kuma sauran masu hannu cikin lamarin na sama da Naira biliyan 50.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Sai dai wata majiya, ta ce Ganduje ya ƙi amincewa da tayin, inda ya bayyana cewa zargin ƙarya ne, kuma zai yi nasara a shari’arsa a kotu wanda shugaban Tinubu da kansa ya sanar da Ganduje shiri na diflomasiyya tare da ba shi damar zaɓar wata ƙasa a Afirka.

Wata majiya ta kusa da Ganduje ta ce abin da shugaba Tinubu, ya fi so shi ne ya naɗa shi Jakadan Nijeriya a ƙasar Chadi, duba da cewar ya taɓa yin aiki a Ndjamena a matsayin babban sakataren hukumar kula da tafkin Chadi tsakanin 2009 zuwa 2011.

Jaridar Daily Nigeria ta ruwaito cewa kwanaki kaɗan bayan Shugaba Tinubu ya sanar da matakin ga Ganduje, an aike masa da wasiƙar wa’adi game da buƙatar ya gudanar da babban taron majalisar jam’iyyar APC na ƙasa.

Wasikar mai ɗauke da kwanan wata 9 ga watan Agusta, da sa hannun Shugaban Hadiman Tinubu, Femi Gbajabiamila, ta sanar da Ganduje cewa shugaban ƙasa zai samu halartar taron Majalisar Jam’iyyar a ranar 8 zuwa 19 ga Satumba, 2024.

Ko da aka tuntuɓi mai magana da yawun Ganduje, Edwin Olofu, ya ce mai gidansa bai yi masa bayani kan batun ba amma ya tabbatar da amincewar shugaban ƙasa na a gudanar da babban taron jam’iyyar.

Ganduje
Naziru Adam Ibrahim
+ postsBio
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Ya Kamata Farashin Siminti Ya Sauka — Umahi Ga Masana’antun Siminti
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Shugaba Tinubu Ya Isa Nairobi Domin Halartar Taron Tattalin Arzikin Nahiyar Afirka

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
KANSIEC Ta Sanya 10m A Matsayin Kuɗin Fom Na Takarar Ciyaman A Kano

KANSIEC Ta Sanya 10m A Matsayin Kuɗin Fom Na Takarar Ciyaman A Kano

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.