• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekaru 60: DICON Ta Taimaka Wajen Samar Mana Da Makamai – Janar Musa

by Sadiq
11 months ago
in Labarai
0
Shekaru 60: DICON Ta Taimaka Wajen Samar Mana Da Makamai – Janar Musa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Hafsan rundunar tsaron Nijeriya, Janar Christopher Gwabin Musa, ya bayyana cewa ma’aikatar sarrarafa makamai ta Nijeriya (DICON), ta taimaka wajen samar wa rundunar kayayyakin aiki.

Kayayyakin sun sun hada da motocin yaki da kayayyakin sulken da rundunar soji ke bukata na aikin samar da tsaro a kasar.

  • Birtaniya Za Ta Wahala Idan Likitocin Nijeriya Suka Bar Kasar – Ministan Lafiya
  • Ban TaÉ“a KarÉ“ar Cin Hanci Ko TaÉ“a ƘuÉ—in Ƙananan Hukumomi Ba – Shekarau

Janar Musa, ya bayyana hakan ne, a taron kwanaki biyu da aka soma yau a Abuja na cikar ma’aikatar ta DICON shekaru 60 da kafuwa.

Nasarorin da ma’aikatar ta samu ba ya rasa nasaba da sanya hannu kan dokar ma’aikatar ta shekarar 2023 da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya rattaba hannu a kai a watan Nuwamban 2023.

Idan ba a manta ba, ya bai wa ma’aikatar damar cimma manyan nasarori gami da fadada ayyukanta domin ci gaban Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tun da fari dai, Karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, ya bayyana cewa assasa ma’aikatar sarrafa makaman a shekarar 1964 alamu ne na cin gashin-kai da Nijeriya ta tabbatar, wajen harkokin tsaro da ci gaban kasa.

Ma’aikatar ta zama silar nasarar ayyukan tsaro a kasar tare da fara sayar wa kasashen ketare makamai.

A shekarun da ta kwashe, ma’aikatar ta yi namijin kokari wajen shimfida kyakkyawar manhajar samar da tsaro a kasar.

Sannan ta taimaka wa rundunar tsaron Nujeriya da kayayyaki, domin saukaka ayyukansu na tsaro.

Ministan, ya bayyana cewa ko shakka babu, a karkashin mulkin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ma’aikatar za ta ci gaba da samar da nasarori a wannan fannin tsaro.

A nasa jawabinsa, Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, wanda sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume, ya wakilta, ya ce shekaru 60 da kafuwar ma’aikatar sarrafa makamai alamu ne na tabbatar da tsantsar kishin kasa a harkar tsaro.

Shekaru 60 da suka gabata, ma’aikatar DICON ta himmatu ne, wajen sarrafa makamai da kayan yaki domin taimaka wa rundunar tsaro da sauran ma’aikatun tsaron Nijeriya a kokarinsu na wanzar da zaman lafiya a kasa baki daya.

Shugaban ya ce, hakika ma’aikatar DICON ta taka muhimmiyar rawa a samar wa dakarun Nijeriya da kayan aiki a lokacin yakin basasa domin tabbatar da kasantuwar Nijeriya kasa daya mai cin gashin-kanta.

Shugaba Tinubu, ya kara yin kira ga jagororin ma’aikatar da su kara himma da fadada tunani ga samar da kayayyakin zamani a shirin gwamnati na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’ummar kasar nan.

Har wa yau, ya yi kira ga ‘yan kasa su taimaka su bayar da goyon baya ga nasarar ma’aikatar.

Daga bisani, shugaban ya kaddamar da sabon tambarin ma’aikatar tare da littafi na musamman da aka wallafa na cikar DICON shekaru 60 da kafuwa.

Taron, ya samu halartar ministoci, shugabannin tsaro da jami’an kasashen waje da kamfanoni da manazarta harkokin tsaro da ‘yan jarida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DICONJanar MusaMa'aikataMatawalleMinistaTaroTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Birtaniya Za Ta Wahala Idan Likitocin Nijeriya Suka Bar Kasar – Ministan Lafiya

Next Post

WATA SABUWA: Ganduje Ya Nuna Rashin Jin Daɗi Bayan Tinubu Ya Masa Tayin Muƙamin Jakada

Related

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya
Labarai

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

10 hours ago
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025
Labaran Kasuwanci

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

12 hours ago
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista
Labarai

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

14 hours ago
Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi

16 hours ago
2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu
Manyan Labarai

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

18 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Shettima Ya Ziyarci Buhari A Landan Cikin Sirri Don Duba Lafiyarsa

18 hours ago
Next Post
WATA SABUWA: Ganduje Ya Nuna Rashin Jin Daɗi Bayan Tinubu Ya Masa Tayin Muƙamin Jakada

WATA SABUWA: Ganduje Ya Nuna Rashin Jin Daɗi Bayan Tinubu Ya Masa Tayin Muƙamin Jakada

LABARAI MASU NASABA

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

July 13, 2025
NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.