• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Barcelona Ta Dauki Hanyar Lashe Gasar La liga?

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
Shin Barcelona Ta Dauki Hanyar Lashe Gasar La liga?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar kwallon kafa ta Barcelona ta ci gaba da jan ragamar teburin La Liga ta bana bayan ta bai wa abokiyar hamayyar ta Real Madrid tazarar maki takwas karo na biyu a kakar nan.

Barcelona ta doke Sebilla 3-0 a wasan mako na 20 da suka kara a filin wasa na Nou Camp ranar Lahadi kuma hakan ya sa kungiyar da Dabi ke jan ragama ta hada maki 53 ta ci gaba da zama a matakin farko, ita kuwa Real Madrid ta biyu tana da maki 45.

  • Barcelona Ta Dawo Cikin Hayyacinta – Cewar Laporta

A wasan da aka buga na mako na 20, Barcelona ce ta hada maki uku a tsakanin kungiyoyi shidan teburin babbar gasar ta Sifaniya wanda hakan yake nufin akwai ci gaba sosai a kungiyar.

Cikin kungiyoyin shidan farko Atletico Madrid ce ta tashi 1-1 da Getafe ranar Asabar, Celta Bigo ta je ta doke Real Betis 4-3 ranar Lahadi sannan a ranar Lahadin Real Madrid ta yi rashin nasara da ci 1-0 a gidan Mallorca da wanda Balladolid ta je ta ci Sociedad 1-0 a karshen mako.

Barcelona ta ci kwallo ukun ta hannun Jordi Alba da Gabi da kuma Raphinha a wasan da ta yi kuma kawo yanzu saura wasanni 18 kenan maki 54 suka rage a karkare wasannin babbar gasar ta Sifaniya ta bana.

Labarai Masu Nasaba

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Barcelona ta bai wa Real Madrid tazarar maki takwas, ko a iya cewa watakila kungiyar na kan hanyar lashe gasar La Liga na kakar nan duba da irin tafiyar wahainiyar da Real Madrid take yi?

A tarihin gasar ta La Liga, duk kungiyar da ta bayar da tazarar maki takwas ko fiye da haka, bayan buga wasa 20 ita ce kan lashe kofin shekarar kuma karo takwas a baya da Barcelona ta ja ragamar teburin La Liga, bayan wasa 20 ta kuma bai wa Real Madrid tazarar maki takwas ko

fiye da hakan, ita ce ta lashe kofin.
Ga jerin kakar da Barcelona ta yi wannan bajintar

Kakar wasa ta 1997 zuwa 1998 da kakar wasa ta 1998 zuwa 1999 da kakar wasa ra 2004 zuwa 2005 da kakar wasa ta 2005 zuwa 2006 da kakar wasa ta 2008 zuwa 2009 da kakar wasa ta 2010 zuwa 2011 da kakar wasa ta 2012 zuwa 2013 da kakar wasa ta 2015 zuwa 2016 da kakar wasa ta 2017 zuwa 2018 da kuma kakar wasa ta 2018 zuwa 2019.

Da yake kwallon kafa ce alkaluma kan iya canjawa a kowanne lokaci, kuma komai zai iya faruwa musamman a kokarin lashe kofin kakar wasan da muke ciki ta 2022 zuwa 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-15 Na Kasar Sin Sun Kammala Tattakin Farko A Wajen Tashar Binciken Samaniya

Next Post

Ya Kamata Amurka Ta Dakatar Da Sanyawa Sauran Kasashe Takunkumi Bisa Radin Kanta

Related

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu
Wasanni

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

14 hours ago
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan
Wasanni

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

16 hours ago
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal
Wasanni

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

17 hours ago
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona
Wasanni

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

2 days ago
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG
Wasanni

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

4 days ago
Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5
Wasanni

Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

6 days ago
Next Post
Ya Kamata Amurka Ta Dakatar Da Sanyawa Sauran Kasashe Takunkumi Bisa Radin Kanta

Ya Kamata Amurka Ta Dakatar Da Sanyawa Sauran Kasashe Takunkumi Bisa Radin Kanta

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.