• English
  • Business News
Sunday, June 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Barcelona Ta Dauki Hanyar Lashe Gasar La liga?

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
Shin Barcelona Ta Dauki Hanyar Lashe Gasar La liga?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar kwallon kafa ta Barcelona ta ci gaba da jan ragamar teburin La Liga ta bana bayan ta bai wa abokiyar hamayyar ta Real Madrid tazarar maki takwas karo na biyu a kakar nan.

Barcelona ta doke Sebilla 3-0 a wasan mako na 20 da suka kara a filin wasa na Nou Camp ranar Lahadi kuma hakan ya sa kungiyar da Dabi ke jan ragama ta hada maki 53 ta ci gaba da zama a matakin farko, ita kuwa Real Madrid ta biyu tana da maki 45.

  • Barcelona Ta Dawo Cikin Hayyacinta – Cewar Laporta

A wasan da aka buga na mako na 20, Barcelona ce ta hada maki uku a tsakanin kungiyoyi shidan teburin babbar gasar ta Sifaniya wanda hakan yake nufin akwai ci gaba sosai a kungiyar.

Cikin kungiyoyin shidan farko Atletico Madrid ce ta tashi 1-1 da Getafe ranar Asabar, Celta Bigo ta je ta doke Real Betis 4-3 ranar Lahadi sannan a ranar Lahadin Real Madrid ta yi rashin nasara da ci 1-0 a gidan Mallorca da wanda Balladolid ta je ta ci Sociedad 1-0 a karshen mako.

Barcelona ta ci kwallo ukun ta hannun Jordi Alba da Gabi da kuma Raphinha a wasan da ta yi kuma kawo yanzu saura wasanni 18 kenan maki 54 suka rage a karkare wasannin babbar gasar ta Sifaniya ta bana.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Wasa Biyar Da Suka Taka Rawar Gani A Kofin Zakarun Turai

Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila

Barcelona ta bai wa Real Madrid tazarar maki takwas, ko a iya cewa watakila kungiyar na kan hanyar lashe gasar La Liga na kakar nan duba da irin tafiyar wahainiyar da Real Madrid take yi?

A tarihin gasar ta La Liga, duk kungiyar da ta bayar da tazarar maki takwas ko fiye da haka, bayan buga wasa 20 ita ce kan lashe kofin shekarar kuma karo takwas a baya da Barcelona ta ja ragamar teburin La Liga, bayan wasa 20 ta kuma bai wa Real Madrid tazarar maki takwas ko

fiye da hakan, ita ce ta lashe kofin.
Ga jerin kakar da Barcelona ta yi wannan bajintar

Kakar wasa ta 1997 zuwa 1998 da kakar wasa ta 1998 zuwa 1999 da kakar wasa ra 2004 zuwa 2005 da kakar wasa ta 2005 zuwa 2006 da kakar wasa ta 2008 zuwa 2009 da kakar wasa ta 2010 zuwa 2011 da kakar wasa ta 2012 zuwa 2013 da kakar wasa ta 2015 zuwa 2016 da kakar wasa ta 2017 zuwa 2018 da kuma kakar wasa ta 2018 zuwa 2019.

Da yake kwallon kafa ce alkaluma kan iya canjawa a kowanne lokaci, kuma komai zai iya faruwa musamman a kokarin lashe kofin kakar wasan da muke ciki ta 2022 zuwa 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-15 Na Kasar Sin Sun Kammala Tattakin Farko A Wajen Tashar Binciken Samaniya

Next Post

Ya Kamata Amurka Ta Dakatar Da Sanyawa Sauran Kasashe Takunkumi Bisa Radin Kanta

Related

UEFA
Wasanni

‘Yan Wasa Biyar Da Suka Taka Rawar Gani A Kofin Zakarun Turai

14 hours ago
Muhammad Salah: Gwarzon Afirka A Firimiyar Ingila
Wasanni

Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila

1 day ago
Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi
Wasanni

Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

2 days ago
De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City
Wasanni

De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City

3 days ago
Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye Aikinsa
Wasanni

Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye Aikinsa

3 days ago
Manchester City Ta Kammala Daukar Rayan Cherki Daga Lyon
Wasanni

Manchester City Ta Kammala Daukar Rayan Cherki Daga Lyon

4 days ago
Next Post
Ya Kamata Amurka Ta Dakatar Da Sanyawa Sauran Kasashe Takunkumi Bisa Radin Kanta

Ya Kamata Amurka Ta Dakatar Da Sanyawa Sauran Kasashe Takunkumi Bisa Radin Kanta

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya

Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya

June 15, 2025
Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC

Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC

June 15, 2025
PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin

PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin

June 15, 2025
An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai

An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai

June 15, 2025
Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano

Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano

June 15, 2025
Dan Asalin Tudun Loess

Dan Asalin Tudun Loess

June 15, 2025
Ba Zai Manta Da Shawarar Mahaifinsa Ba

Ba Zai Manta Da Shawarar Mahaifinsa Ba

June 15, 2025
Ganduje Ya Noƙe Kan Furta Ko Shettima Zai Yi Takara Da Tinubu A 2027

Ganduje Ya Noƙe Kan Furta Ko Shettima Zai Yi Takara Da Tinubu A 2027

June 15, 2025
Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila

Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila

June 15, 2025
APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu

APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu

June 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.