ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Barcelona Ta Dauki Hanyar Lashe Gasar La liga?

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Barcelona

Kungiyar kwallon kafa ta Barcelona ta ci gaba da jan ragamar teburin La Liga ta bana bayan ta bai wa abokiyar hamayyar ta Real Madrid tazarar maki takwas karo na biyu a kakar nan.

Barcelona ta doke Sebilla 3-0 a wasan mako na 20 da suka kara a filin wasa na Nou Camp ranar Lahadi kuma hakan ya sa kungiyar da Dabi ke jan ragama ta hada maki 53 ta ci gaba da zama a matakin farko, ita kuwa Real Madrid ta biyu tana da maki 45.

  • Barcelona Ta Dawo Cikin Hayyacinta – Cewar Laporta

A wasan da aka buga na mako na 20, Barcelona ce ta hada maki uku a tsakanin kungiyoyi shidan teburin babbar gasar ta Sifaniya wanda hakan yake nufin akwai ci gaba sosai a kungiyar.

ADVERTISEMENT

Cikin kungiyoyin shidan farko Atletico Madrid ce ta tashi 1-1 da Getafe ranar Asabar, Celta Bigo ta je ta doke Real Betis 4-3 ranar Lahadi sannan a ranar Lahadin Real Madrid ta yi rashin nasara da ci 1-0 a gidan Mallorca da wanda Balladolid ta je ta ci Sociedad 1-0 a karshen mako.

Barcelona ta ci kwallo ukun ta hannun Jordi Alba da Gabi da kuma Raphinha a wasan da ta yi kuma kawo yanzu saura wasanni 18 kenan maki 54 suka rage a karkare wasannin babbar gasar ta Sifaniya ta bana.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Barcelona ta bai wa Real Madrid tazarar maki takwas, ko a iya cewa watakila kungiyar na kan hanyar lashe gasar La Liga na kakar nan duba da irin tafiyar wahainiyar da Real Madrid take yi?

A tarihin gasar ta La Liga, duk kungiyar da ta bayar da tazarar maki takwas ko fiye da haka, bayan buga wasa 20 ita ce kan lashe kofin shekarar kuma karo takwas a baya da Barcelona ta ja ragamar teburin La Liga, bayan wasa 20 ta kuma bai wa Real Madrid tazarar maki takwas ko

fiye da hakan, ita ce ta lashe kofin.
Ga jerin kakar da Barcelona ta yi wannan bajintar

Kakar wasa ta 1997 zuwa 1998 da kakar wasa ta 1998 zuwa 1999 da kakar wasa ra 2004 zuwa 2005 da kakar wasa ta 2005 zuwa 2006 da kakar wasa ta 2008 zuwa 2009 da kakar wasa ta 2010 zuwa 2011 da kakar wasa ta 2012 zuwa 2013 da kakar wasa ta 2015 zuwa 2016 da kakar wasa ta 2017 zuwa 2018 da kuma kakar wasa ta 2018 zuwa 2019.

Da yake kwallon kafa ce alkaluma kan iya canjawa a kowanne lokaci, kuma komai zai iya faruwa musamman a kokarin lashe kofin kakar wasan da muke ciki ta 2022 zuwa 2023.

Barcelona
Abba Ibrahim Wada
+ postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Har Yanzu Nijeriya Tana Fatan Zuwa Kofin Duniya Na 2026
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Mece Ce Matsalar Real Madrid? 
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Ko Ka San Dalilin Da Zai Bai Wa Nijeriya Damar Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Next Post
Ya Kamata Amurka Ta Dakatar Da Sanyawa Sauran Kasashe Takunkumi Bisa Radin Kanta

Ya Kamata Amurka Ta Dakatar Da Sanyawa Sauran Kasashe Takunkumi Bisa Radin Kanta

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.