• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Dawowar Ahmad Musa Za Ta Taimaka Wa Kano Pillars?

by Abba Ibrahim Wada
11 months ago
in Wasanni
0
Shin Dawowar Ahmad Musa Za Ta Taimaka Wa Kano Pillars?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A satin da ya gabata ne kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars, ta tabbatar da cewa tsofaffin ‘yan wasanta guda biyu, Ahmad Musa da Shehu Abdullahi sun koma kungiyar domin buga kakar wasa ta 2024 zuwa 2025.

Sanarwa da mai magana da yawun kungiyar, Abubakar Isa Dandago, ya fitar a shafinsa na Facebook, ta kara da cewa ‘yan wasan guda biyu sun koma kungiyar ne bayan kammala kulla yarjejeniya da shugabannin kungiyar kuma tuni ma sun buga wasan da kungiyar ta samu nasara a kan Sunshines Stars da ci 2-0 a ranar Lahadin da ta gabata a gasar firimiyar Nijeriya.

  • Shin Usman Abdalla Zai Iya Dawo Da Martabar Kano Pillars?
  • Kokarin Farfado Da Ilimi: Gwamnan Kano Ya Zama Gwarzo A Tsakanin Gwamnoni

Ahmad Musa, mai shekara 31 a duniya ya buga wasa a kungiyar ta Kano karo biyu a baya, inda ya buga wasa a Kano Pillars a kakar wasa ta 2009 zuwa 2010 da kuma shekara ta 2021 kuma ya yi bajinta sosai a wannan lokacin.

Shima dan wasa Shehu Abdullahi kuma, dan asalin Jihar Sakkwato, wanda ba shi da kungiya tun shekarar 2023, ya buga wasa a kungiyar a shekara ta 2012 kuma shi ma kamar Ahamd Musa, ya wakilci tawagar Super Eagles ta Nijeriya a wasanni daban-daban.

Sai dai kafin Ahmad Musa ya koma Kano Pillars, zakarun gasar Firimiyar Nijeriya, Rangers international, sun nemi ya koma kungiyar amma tsohon kyaftin din na Super Eagles ta Nijeriya, ya fi son buga wa Kano Pillars wasa.

Labarai Masu Nasaba

Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

Kofin Duniya: Lookman Da Dessers Sun Isa Sansanin Super Eagles A Uyo

A kakar wasan Ahmed Musa ta farko a Kano Pillars a Shekarar 2009, ya lashe kyautar wanda ya fi zura kwallo a raga a gasar Firimiyar Nijeriya, inda ya kammala gasar da kwallaye 18 wanda hakan ne ya ja hankalin kungiyar BBB Benlo ta kasar Netherlands ta dauke shi.

Har ila yau, Ahmad Musa ya buga wasa a kungiyoyin CSKA Moscow ta kasar Rasha da Leceister City ta Ingila, sai kuma Al Nassr ta kasar Saudiyya kafin ya koma kasar Turkiyya inda nan ma ya buga kakar wasa guda daya.

Shin Zai Taimakawa Kano Pillars?

A wasansa na farko a kungiyar ta Kano Pillars, Ahamd Musa ya zura kwallaye biyu, sannan ya barar da fanareti a wasansa na farko bayan ya dawo kungiyar ta Pillars, a wasan da ‘SAI MASU GIDA’ ta doke Sunshine Stars da ci biyu da nema a filin wasa na Muhammad Dikko da ke

Jihar Katsina a ranar Lahadi 6 ga watan Oktoban shekarar 2024 kuma wasan shi ne wasa na biyar na gasar Firimiyar Nijeriya na kakar wasa ta 2024 zuwa 2025.

Dan wasan ya zura kwallonsa ta farko a minti hudu da fara wasa, sannan ya kara jefa kwallo ta biyu a minti shida bayan dawowa daga hutun rabin lokaci, sai dai saura kiris Musa ya samu nasarar cin kwallo uku rigis a wasan, amma ya yi rashin nasara, inda ya barar da bugun fanareti a minti na 70 a wasan.

Da yake bayyana farin cikinsa, Ahmed Musa ya rubuta a shafinsa na Facebook cewa, “na yi farin cikin dawowa Kano Pillars. Ina godiya ga dukkan ma’aikatan kungiyar da abokan wasana da masu horar da ‘yanwasa bisa wannan damar da suka ba ni. Sannan magoya bayannmu da ma duk wadanda suka zo kallonmu, muna godiya. Zura kwallo biyun nan da na yi somin-tabi ne,” in ji shi.

A shekarar 2009 da ya fara buga wasa a Kano Pillars, Ahamd Musa ya zura kwallaye 18 ciki n wasanni 25 da ya buga kafin ya tafi kungiyar kwallon kafa ta BBB Benlo ta kasar Netherland da ke buga babbar gasar kasar.

Sannan ya sake dawowa a shekarar 2021 bayan ya bar kungiyar Al Nassr ta Saudiya, inda ya buga wasanni 8. Sai kuma wannan kakar da ya dawo, bayan ya bar kungiyar Sibasspor ta Turkiyya a shekarar 2024.

Tuni masana suke ganin dawowar Ahamd Musa za ta taimakawa kungiyar musamman wajen zura kwallo a raga kasancewarsa kwararre ne a wannan fannin tun da a baya an ga yadda ya nuna bajinta a gasar ta Nijeriya da ma irin kokarin da ya yi a kungiyar BBB Benlo da CSKA Moscow ta kasar Rasha.

Sannan zuwansa Kano Pillars zai taimaka wa matasan ‘yan wasan gaba na kungiyar wajen koyar iya zura kwallo a raga tare kuma da koyon dabaru kala-kala wajen iya sarrafa kwallo a yadi na 18 da ma irin gudun da ake bukatar dan wasan gaba ya dinga yi wajen neman zura kwallo a raga.

Ba ma iya ‘yan wasan gaba ba, su kansu ragowar ‘yan wasan kungiyar za su samu kwarewa sosai kasancewar Ahamd Musa ya kware sosai saboda ya buga wasa a manyan kungiyoyi a Nahiyar Turai, sannan kuma ya buga wasa da manyan ‘yan wasa a duniya ciki har da Leonel Messi a gasar cin kofin duniya da Nijeriya ta buga da Argentina.

Shi ma dan wasa Shehu Abdullahi zai taimakawa ‘yan wasan kungiyar ta Kano Pillars saboda yadda ya buga wasa a Nahiyar Turai da ma tawagar Super eagles ta Nijeriya, sannan daukar atisayen da za su yi da ragowar ‘yan wasa zai sake bude tunanin ragowar ‘yan wasa.

Dawowar Ahamd Musa da Shehu Abdullahi Kano Pillars ba iya Kano Pillars zai taimaka ba, har da gasar Firimiya baki daya saboda kwararru ne wadanda suka buga wasa a Nahiyar Turai sannan kuma hakan zai bude hanyar wasu ‘yan wasan na Nijeriya da suke buga wasa a Turai su dinga dawowa suna taimaka wa kungiyoyi na gida domin bunkasa gasar cikin gida tare

kuma da samun kudin shiga ga kungiyoyi da ita kanta hukumar da ke kula da shirya gasar.

Kungiyar Kano Pillars dai ba ta buga wasanninta a gida Jihar Kano, yanzu tana buga wasa ne a filin wasa na Muhammadi Dikko dake jihar Katsina a matsayin gidanta, saka makamakon gyara da ake yi a filin wasa na Sani Abacha dake kofar mata a Kano, idan har kungiyar ta koma buga wasa a Kano ana ganin abin zai fi armashi.

Yanzu dai abin jira a gani shi ne ko fara wasan da kafar dama zai ta dore bisa la’akari da yadda a baya ya koma kungiyar kuma ya buga mata wasanni 8 ba tare da cin kwallo ko daya ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kano PillarsPillarsWasanni
ShareTweetSendShare
Previous Post

Har Yanzu Garuruwa 24 Na Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara Da Katsina

Next Post

Yadda Na Juya Jarin Naira 15,000 Zuwa Babbar Harka – Safara’u

Related

Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo
Wasanni

Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

1 day ago
Lookman
Wasanni

Kofin Duniya: Lookman Da Dessers Sun Isa Sansanin Super Eagles A Uyo

2 days ago
Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG
Wasanni

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

4 days ago
Isak Na Dab Da Zama Ɗan Wasa Mafi Tsada A Tarihin Firimiya
Wasanni

Isak Na Dab Da Zama Ɗan Wasa Mafi Tsada A Tarihin Firimiya

5 days ago
Yadda Kungiyoyin Firimiyar Ingila Suka Shirya Wa Kakar Bana
Wasanni

Yadda Kungiyoyin Firimiyar Ingila Suka Shirya Wa Kakar Bana

6 days ago
‘Yan Wasan Afirka Da Ake Ganin Za Su Yi Abin Kirki A Kakar Bana
Wasanni

‘Yan Wasan Afirka Da Ake Ganin Za Su Yi Abin Kirki A Kakar Bana

6 days ago
Next Post
Yadda Na Juya Jarin Naira 15,000 Zuwa Babbar Harka – Safara’u

Yadda Na Juya Jarin Naira 15,000 Zuwa Babbar Harka - Safara'u

LABARAI MASU NASABA

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

September 5, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

September 5, 2025
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 5, 2025
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

September 5, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

September 5, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.