• English
  • Business News
Friday, July 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Dawowar Ahmad Musa Za Ta Taimaka Wa Kano Pillars?

by Abba Ibrahim Wada
10 months ago
in Wasanni
0
Shin Dawowar Ahmad Musa Za Ta Taimaka Wa Kano Pillars?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A satin da ya gabata ne kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars, ta tabbatar da cewa tsofaffin ‘yan wasanta guda biyu, Ahmad Musa da Shehu Abdullahi sun koma kungiyar domin buga kakar wasa ta 2024 zuwa 2025.

Sanarwa da mai magana da yawun kungiyar, Abubakar Isa Dandago, ya fitar a shafinsa na Facebook, ta kara da cewa ‘yan wasan guda biyu sun koma kungiyar ne bayan kammala kulla yarjejeniya da shugabannin kungiyar kuma tuni ma sun buga wasan da kungiyar ta samu nasara a kan Sunshines Stars da ci 2-0 a ranar Lahadin da ta gabata a gasar firimiyar Nijeriya.

  • Shin Usman Abdalla Zai Iya Dawo Da Martabar Kano Pillars?
  • Kokarin Farfado Da Ilimi: Gwamnan Kano Ya Zama Gwarzo A Tsakanin Gwamnoni

Ahmad Musa, mai shekara 31 a duniya ya buga wasa a kungiyar ta Kano karo biyu a baya, inda ya buga wasa a Kano Pillars a kakar wasa ta 2009 zuwa 2010 da kuma shekara ta 2021 kuma ya yi bajinta sosai a wannan lokacin.

Shima dan wasa Shehu Abdullahi kuma, dan asalin Jihar Sakkwato, wanda ba shi da kungiya tun shekarar 2023, ya buga wasa a kungiyar a shekara ta 2012 kuma shi ma kamar Ahamd Musa, ya wakilci tawagar Super Eagles ta Nijeriya a wasanni daban-daban.

Sai dai kafin Ahmad Musa ya koma Kano Pillars, zakarun gasar Firimiyar Nijeriya, Rangers international, sun nemi ya koma kungiyar amma tsohon kyaftin din na Super Eagles ta Nijeriya, ya fi son buga wa Kano Pillars wasa.

Labarai Masu Nasaba

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

A kakar wasan Ahmed Musa ta farko a Kano Pillars a Shekarar 2009, ya lashe kyautar wanda ya fi zura kwallo a raga a gasar Firimiyar Nijeriya, inda ya kammala gasar da kwallaye 18 wanda hakan ne ya ja hankalin kungiyar BBB Benlo ta kasar Netherlands ta dauke shi.

Har ila yau, Ahmad Musa ya buga wasa a kungiyoyin CSKA Moscow ta kasar Rasha da Leceister City ta Ingila, sai kuma Al Nassr ta kasar Saudiyya kafin ya koma kasar Turkiyya inda nan ma ya buga kakar wasa guda daya.

Shin Zai Taimakawa Kano Pillars?

A wasansa na farko a kungiyar ta Kano Pillars, Ahamd Musa ya zura kwallaye biyu, sannan ya barar da fanareti a wasansa na farko bayan ya dawo kungiyar ta Pillars, a wasan da ‘SAI MASU GIDA’ ta doke Sunshine Stars da ci biyu da nema a filin wasa na Muhammad Dikko da ke

Jihar Katsina a ranar Lahadi 6 ga watan Oktoban shekarar 2024 kuma wasan shi ne wasa na biyar na gasar Firimiyar Nijeriya na kakar wasa ta 2024 zuwa 2025.

Dan wasan ya zura kwallonsa ta farko a minti hudu da fara wasa, sannan ya kara jefa kwallo ta biyu a minti shida bayan dawowa daga hutun rabin lokaci, sai dai saura kiris Musa ya samu nasarar cin kwallo uku rigis a wasan, amma ya yi rashin nasara, inda ya barar da bugun fanareti a minti na 70 a wasan.

Da yake bayyana farin cikinsa, Ahmed Musa ya rubuta a shafinsa na Facebook cewa, “na yi farin cikin dawowa Kano Pillars. Ina godiya ga dukkan ma’aikatan kungiyar da abokan wasana da masu horar da ‘yanwasa bisa wannan damar da suka ba ni. Sannan magoya bayannmu da ma duk wadanda suka zo kallonmu, muna godiya. Zura kwallo biyun nan da na yi somin-tabi ne,” in ji shi.

A shekarar 2009 da ya fara buga wasa a Kano Pillars, Ahamd Musa ya zura kwallaye 18 ciki n wasanni 25 da ya buga kafin ya tafi kungiyar kwallon kafa ta BBB Benlo ta kasar Netherland da ke buga babbar gasar kasar.

Sannan ya sake dawowa a shekarar 2021 bayan ya bar kungiyar Al Nassr ta Saudiya, inda ya buga wasanni 8. Sai kuma wannan kakar da ya dawo, bayan ya bar kungiyar Sibasspor ta Turkiyya a shekarar 2024.

Tuni masana suke ganin dawowar Ahamd Musa za ta taimakawa kungiyar musamman wajen zura kwallo a raga kasancewarsa kwararre ne a wannan fannin tun da a baya an ga yadda ya nuna bajinta a gasar ta Nijeriya da ma irin kokarin da ya yi a kungiyar BBB Benlo da CSKA Moscow ta kasar Rasha.

Sannan zuwansa Kano Pillars zai taimaka wa matasan ‘yan wasan gaba na kungiyar wajen koyar iya zura kwallo a raga tare kuma da koyon dabaru kala-kala wajen iya sarrafa kwallo a yadi na 18 da ma irin gudun da ake bukatar dan wasan gaba ya dinga yi wajen neman zura kwallo a raga.

Ba ma iya ‘yan wasan gaba ba, su kansu ragowar ‘yan wasan kungiyar za su samu kwarewa sosai kasancewar Ahamd Musa ya kware sosai saboda ya buga wasa a manyan kungiyoyi a Nahiyar Turai, sannan kuma ya buga wasa da manyan ‘yan wasa a duniya ciki har da Leonel Messi a gasar cin kofin duniya da Nijeriya ta buga da Argentina.

Shi ma dan wasa Shehu Abdullahi zai taimakawa ‘yan wasan kungiyar ta Kano Pillars saboda yadda ya buga wasa a Nahiyar Turai da ma tawagar Super eagles ta Nijeriya, sannan daukar atisayen da za su yi da ragowar ‘yan wasa zai sake bude tunanin ragowar ‘yan wasa.

Dawowar Ahamd Musa da Shehu Abdullahi Kano Pillars ba iya Kano Pillars zai taimaka ba, har da gasar Firimiya baki daya saboda kwararru ne wadanda suka buga wasa a Nahiyar Turai sannan kuma hakan zai bude hanyar wasu ‘yan wasan na Nijeriya da suke buga wasa a Turai su dinga dawowa suna taimaka wa kungiyoyi na gida domin bunkasa gasar cikin gida tare

kuma da samun kudin shiga ga kungiyoyi da ita kanta hukumar da ke kula da shirya gasar.

Kungiyar Kano Pillars dai ba ta buga wasanninta a gida Jihar Kano, yanzu tana buga wasa ne a filin wasa na Muhammadi Dikko dake jihar Katsina a matsayin gidanta, saka makamakon gyara da ake yi a filin wasa na Sani Abacha dake kofar mata a Kano, idan har kungiyar ta koma buga wasa a Kano ana ganin abin zai fi armashi.

Yanzu dai abin jira a gani shi ne ko fara wasan da kafar dama zai ta dore bisa la’akari da yadda a baya ya koma kungiyar kuma ya buga mata wasanni 8 ba tare da cin kwallo ko daya ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kano PillarsPillarsWasanni
ShareTweetSendShare
Previous Post

Har Yanzu Garuruwa 24 Na Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara Da Katsina

Next Post

Yadda Na Juya Jarin Naira 15,000 Zuwa Babbar Harka – Safara’u

Related

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa
Wasanni

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

2 days ago
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu
Wasanni

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

3 days ago
Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo
Wasanni

Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo

3 days ago
Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro
Wasanni

Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro

4 days ago
Kamfanin Puma Zai Biya Man City Fam Biliyan 1 A Shekara 10 Domin Samar Wa Kungiyar Kayan Wasa
Wasanni

Kamfanin Puma Zai Biya Man City Fam Biliyan 1 A Shekara 10 Domin Samar Wa Kungiyar Kayan Wasa

6 days ago
Lamine Yamal Na Fuskantar Bincike Kan Bikin Zagayowar Ranar Haihuwarsa A Spain
Wasanni

Lamine Yamal Na Fuskantar Bincike Kan Bikin Zagayowar Ranar Haihuwarsa A Spain

6 days ago
Next Post
Yadda Na Juya Jarin Naira 15,000 Zuwa Babbar Harka – Safara’u

Yadda Na Juya Jarin Naira 15,000 Zuwa Babbar Harka - Safara'u

LABARAI MASU NASABA

majalisar kasa

‘Yan Majalisa Sun Zargi Hukumomin Gwamnati Da Wawure Sama Da Naira Biliyan 103.8

July 25, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Mene Ne Birnin Zamani Na Al’umma

Fahimtar Sabon Tunani: Mene Ne Birnin Zamani Na Al’umma

July 25, 2025
Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

July 25, 2025
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

July 25, 2025
Amcon

Majalisa Ta Ba Wa Shugaban NNPCL Awa 24 Ya Bayyana Gabanta Ko Ta Sa A Kamo Shi

July 25, 2025
Jiragen NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Lalata Baburansu 40 Da Bindigu 6 A Borno

Wasu Mahara Sun Sake Kashe Mutum 14 A Wani Kauyen Jihar Filato

July 25, 2025

Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya

July 25, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi

July 25, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Hukumar ‘Yansanda Ta Yi Wa Wasu Manyan Jami’anta Karin Girma

July 25, 2025
Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.