ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Usman Abdalla Zai Iya Dawo Da Martabar Kano Pillars?

by Sulaiman and Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Kano Pillars

Tun bayan da kungiyar ta tabbatar da sabon kociyan, tuni masu sharhi a kan kwallon kafa a Nijeriya suka fara tattaunawa a kan ko sabon mai koyarwar zai kai kungiyar ga nasara bayan koma baya da aka samu a ‘yan shekarun nan.

 

Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta gabatar da sabon kociyanta, Usman Abdallah a farkon wannan watan, wanda zai ja ragamar kungiyar kan yarjejeniyar kakar wasa guda biyu da cewar za a tsawaita masa wata 12 idan ya taka rawar gani.

ADVERTISEMENT
  • Jan Aikin Da Ke Gaban Sababbin Shugabannin Kano Pillars
  • Dalilan Amai Da Gudawa Na Yara Lokacin Fitar Hakori

Kano Pillars ce kan gaba a yawan magoya baya a fadin kasar nan, magoya baya na hakika da suke cika filin wasa na Sani Abacha, duk ranar da take buga wasa a gida haka kuma dubban magoya bayanta kan bi kungiyar wasannin da take yi a waje da ya hada da na Premier ko na kalubalen kasar, saboda kishin da suke yi wa kungiyar.

 

LABARAI MASU NASABA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

Kano Pillars ta lashe kofin Premier na Nijeriya hudu da na kalubale biyu, wadda sannan ta wakilci Nijeriya a gasar cin kofin Afirka na ‘Champions League’ da ‘Confederation Cup’ a shekarun baya, lokacin da kungiyar take kan ganiyarta. Kungiyar kan taka rawar gani a gasar Premier ta Nijeriya, musamman karawa da Enyimba da Rangers da National da babban wasan hamayya tsakanin kungiyar da kuma kungiyar Katsina United da dai sauransu.

 

To sai dai kungiyar ta ci karo da koma baya, wadda rabon da ta dauki kofin Premier tun 2014, amma ta lashe FA Cup a 2019, wadda rabon da wata kungiya a Kano ta lashe shi tun 1953, sannan kuma rabon da kungiyar ta buga gasar Afirka tun 2020, wadda aka yi waje da ita a zagayen neman shiga wasannin, wanda aka fi sani da ‘Play-Off’.

 

Kungiyar Kano Pillars ta ci karo da matsaloli da yawa da ya kassara kwazon kungiyar tun daga rashin bayar da kudi a lokacin da ya dace daga gwamnati, sannan wasu matsalolin ana danganta su da rashin daukar ‘yan wasan da suka dace da rashin kwazon ‘yan wasa da yawan tarzoma daga magoya a gida da dai sauransu.

 

A kakar wasa ta 2020 zuwa 2021 aka ci tarar Kano Pillars Naira miliyan bakwai da dubu dari biyar, bayan da aka samu kungiyar da karya dokar hukumar gasar kasar da ta NFF. Dokar ta kunshi hana nuna wasa kai tsaye a talabijin da tayar da hatsaniya daga ‘yan kallo a karawa tsakanin Akwa United da Kano Pillars.

 

Pillars ta fadi daga gasar Premier ta kasa ranar 16 ga watan Yulin 2022, bayan matsalolin da suka baibaye ta kuma kungiyar ta fuskanci hukuncin masu gudanar da gasar Premier ta Nijeriya, bayan da aka samu shugabanta Surajo Janbul a karawa da Dakkada.

 

A 2019 Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da nada Surajo Sha’aibu Yahaya da ake kira Jambul, wanda ya maye gurbin Alhaji Tukur Babangida, sai dai Jambul ya karbi ragama lokacin da Pillars ke dab da lashe ‘Federation Cup.” da kuma ta biyu a babbar gasa ta kasa.

 

To sai dai a kakar aka yi waje da Pillars a CAF Champions League a wasannin cike gurbi, inda Asante Kotoko ta Ghana ta ci 5-2 gida da waje, haka kuma a kakar gaba aka yi waje da Pillars dagga CAF Confederation Cup, inda wata karamar kungiya daga Senegal ta yi nasara 3-1 gida da waje.

 

Sakamakon hatsaniyar da magoya bayan Pillers ke yi a yayin da kungiyar take wasa ya sa kungiyar aka dauke ta daga buga wasannin ta na gida a filin was ana Sani Abacha, hakan ya sa ta je filaye daban-daban har guda hudu waje.

 

Da farko an mayar da Kano Pillar buga buga wasannin gida a filin wasana Ahmadu Bello dake Kaduna, daga nan ta koma filin Muhammadu Dikko a Katsina, sannan a Katsina ma an samu hatsaniya, inda aka mayar da kungiyar buga wasanninta Babban Birnin Tarayya Abuja, kafin daga baya ta koma gida filin wasa na Sani Abacha.

 

Bayan da Pillars ta dawo gida sai ta tsinci kanta a kasan teburi daga nan aka fara cuku-cukun yadda kungiyar za ta ci gaba da zama a Premier League inda daga nan ne kuma hankalin magoya baya ya tashi kan yadda Pillars ta tsinci kanta a halin kaka-ni-ka yi, wadanda suka zargi shugabanta da rashin kwarewa.

 

Matsin da Jambul ya fuskanta daga wajen magoya baya ya sa ya dauki doka a hannunsa, lokacin da kungiyar ke barar da maki a gida domin lokacin da Pillars ke buga mako na 31 da Dakkada a gida, kuma masu gida na cin kwallo daya, sai Dakkada ta farke dab da za a tashi daga wasan. Daga nan ne Jambul ya shiga fili da cin zarafin mataimakin alkalin wasa da bukatar a soke kwallon da aka ci Pillars, sai dai hakan ya harzuka masu gudanar da Premier, wadanda suka kori Jambul daga baya suka ce za su dauki matakin sha’ria a kansa.

 

Pillars ta karkare a mataki na 19 da maki 45 a kakar, bayan da ta ci wasa tara da canjaras tara aka doke ta karawa 20.Haka kuma an zura kwallo 50 a ragar Pillars, ita kuma ta ci 26 a kakar bana da hakan ya sa ta yi ban kwana da babbar gasa ta Nijeriya da aka karkare.

 

Dawo Da Ibrahim Galadima

Bayan da Gwamnatin Jihar Kano ta sallami Surajo Shu’aibu Yahaya, sai ta nada Alhaji Ibrahim Galadima a matakin rikon kwarya inda daga nan ne Pillars ta nada Babangida Little a matakin sabon shugaban kungiyar, wanda hakan ba ta canja zani ba, kan kalubalen da kungiyar ke fuskanta.

 

Domin shima ya yi fama da na sa matsalolin da yawa, har da daukar sabon koci Offor Paul, wanda ya yi kwana 19 aka maye gurbinsa da Usman Abdallah sai dai kafin nan kungiyar ta sallami Audu Mai Kaba kafin kammala kakar bara, bayan da ta dakatar da shi ta kuma nada Ahmed Garba Yaro-Yaro a matakin rikon kwarya.

 

Kano Pillars ta kare a mataki na 11 a kakar da ta wuce bayan wasanni 38, wadda ba ta samu gurbin wakiltar Nijeriya ba a gasar Afiirka a bana, kuma Pillars za ta fara buga Premier ta Nijeriya ta bana da Ikorodu a Sani Abacha a kakar 2024 zuwa 2025.

Wane ne Usman Abdalla, sabon kociyan Kano Pillars

Sunan mai mkoyarwa Usman Abdalla ba boyayyen suna bane a tarihin kwallon kafa a Nijeriya, kuma ya buga wasa a gida da kuma Afirka kafin Turai, wanda ya fara daga Sanka Bipers ta Kano, sannan ya yi UNTL ta Kaduna da Rocks ta Kaduna da Stationery Stores ta Lagas da kuma Mogas 90 ta Jamhuriyar Benin.

 

Sannan ya buga wasa a Kano State Academic da wakilatar Jihar Kano a wasannin kasa da ake kira Festibal a shekarar 1980 da wakiltar Nijeriya ta matasa ‘‘yan kasa da shekara 20 zuwa 23 tare da dan uwansa Hassan Abdallah.

 

Sai dai a 1991 ya koma buga wasa a kungiyar Al Arabic da kuma kungiyar Bayer Leberkusen, ya kuma je Singapore, inda ya buga wasa a Jurong FC da Khalsa FC da kuma Gombak United FC kafin ya yi ritaya daga buga wasa a shekarar 2006. Usman Abdalla ya fara aikin horar da kwallon kafa a kasar Faransa da EPS FC da FC Sete da FC Frontignan da kuma Bollene FC, bayan da ya mallaki lasisin horarwa daga Turai a Ingila, sannan ya kuma halarci sanin makamar aikin kociyan kungiyoyin Afirka da hukumar kwallon kafar Afirka.

 

A Nijeriya ya koyar da kungiyar Enyimba da lashe kofin Premier Nijeriya a kungiyar da taka rawar gani a gasar Afirka ta Champions League, sai dai kafin ya karbi aikin kociyan Enyimba ya yi mataimaki a Pillars da jan ragamar karamar kungiyar.

 

Da farko ya je Enyimba a matakin mataimakin Paul Aigbogun daga baya aka bashi ragamar jan kungiyar, wanda ya kai dab da karshe a gasar cin kofin Zakarun Afirka wato ‘Champions League’, haka kuma ya horar da Wikki Tourist ta Garin Bauchi da Katsina United daga nan ya je hutu, inda yanzu kuma ya dawo Kano Pillars a karo na biyu, amma wannan dawowar ba a matsayin mataimaki ba, a matsayin mai koyarwa wanda kuma ake ganin kwarewarsa da ilimin sanin kwallo zai taimakawa kungiyar a kakar wasan da za a fara a nan gaba kadan.

Kano Pillars
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Kano Pillars
Abba Ibrahim Wada
Website |  + posts Bio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Next Post
Batun ‘Yan Mata Masu Yanga Wajen Tsallaka Titi

Batun ‘Yan Mata Masu Yanga Wajen Tsallaka Titi

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.