• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin APC Na Zabar Sabon Kakakin Majalisar Wakilai Ya Tada Kura

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Shirin APC Na Zabar Sabon Kakakin Majalisar Wakilai Ya Tada Kura
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matakin da jam’iyyar APC mai mulki ta dauka na ayyana Honarabul Abbas Tajuddeen daga Jihar Kaduna a matsayin wanda take so ya zama shugaban majalisar wakilai da Ben Kalu daga Jihar Abia a matsayin mataimakinsa ya bar baya da kura.

A ranar Litinin ne jam’iyyar ta fitar da sunayen ‘yan majalisar dokokin da ta ke so su zama shugabannin majalisun dokoki ta 10 bayan da, a cewarta, ta tuntubi zababben shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.

  • Kotun Koli Ta Tabbatar Da Nasarar Adeleke A Matsayin Gwamnan Osun
  • ‘Yansanda Sun Kama Kauraye 72 Da Ake Zargi Da Kwacen Wayar Salula A Katsina

A bangaren majalisar dattawa, APC ta zabi Sanata Godswill Akpabio da Barau a matsayin wadanda take su zama shugaba da mataimakinsa.

Sai dai matakin da ta dauka a majalisar wakilai bai yi wa wasu manyan ‘yan majalisa dadi ba, abin da ake gani zai iya haddasa rikici.

Tuni wasu daga cikin wadanda suke zawarcin kujerar suka hau dokin na-ki, inda suka yi watsi da matakin jam’iyyar.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

Wadanda suke zawarcin kujerar shugaban majalisar tarayyar da suka ki amincewa da wannan mataki sun hada da Honarabul Idris Wase da Alhassan Ado Doguwa da Sada-Soli Jibiya.

Sauran sun hada da Honorabul Mukhtar Betara da kuma Ahmed Jaji.

Wasu daga cikin zababbun ‘yan majalisar wakilan wadanda suka nuna rashin jin dadinsu dangane da matakin jam’iyyar APC sun gudanar da wani taro a Abuja a ranar Litinin.

Sun kwatanta wannan mataki da uwar jam’iyyar ta dauka a matsayin yunkurin yi musu dauki-dora.

Cikin mahalarta taron har da Honarabul Wase da Ado Doguwa da Yusuf Gagdi and Sada-Soli da Mohammed Monguno.

Honorabul Wase shi ne mataimakin kakakin majalisar tarayya, kuma ya bayyana cewa wanda jam’iyyar APC ta zaba, Abbas Tajuddeen, ba mutum ba ne da ‘yan majalisa suka sani sosai.

Ya caccaki matakin da APC ta dauka, inda ya ce bai kamata a dauki irin wannan mataki ba tare da tuntubar masu ruwa da tsaki ba.

Shi ma Alhassan Ado Doguwa, wanda a yanzu shi ne shugaban masu rinjaye, ya bayyana cewa dole ne a bar majalisar ta rika zabar shugabanninta.

Ya bayyana cewa hakkinsu ne zabar shugaba a majalisa kuma bai kamata wasu daga waje su rika zaba mata shugaba ba.

“Wani sako da nake son aikawa shi ne majalisa wuri ne da dole ne a bari ya rinka zaba wa kansa shugaba. Batun wanda zai jagorance mu, wata matsala ce wadda ta shafe mu, mu kadai ba matsalar wani ba ce,” in ji Doguwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KuraMajalisar WakilaiShugabanniTinubuZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotun Koli Ta Tabbatar Da Nasarar Adeleke A Matsayin Gwamnan Osun

Next Post

Xi Ya Aikawa Takwaransa Na Ruwanda Sakon Jaje Game Da Balain Ruwan Sama

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

4 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

9 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

15 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

19 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

20 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

1 day ago
Next Post
Xi Ya Aikawa Takwaransa Na Ruwanda Sakon Jaje Game Da Balain Ruwan Sama

Xi Ya Aikawa Takwaransa Na Ruwanda Sakon Jaje Game Da Balain Ruwan Sama

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.