• Leadership Hausa
Monday, October 2, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin APC Na Zabar Sabon Kakakin Majalisar Wakilai Ya Tada Kura

by Sadiq
5 months ago
in Manyan Labarai
0
Shirin APC Na Zabar Sabon Kakakin Majalisar Wakilai Ya Tada Kura
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matakin da jam’iyyar APC mai mulki ta dauka na ayyana Honarabul Abbas Tajuddeen daga Jihar Kaduna a matsayin wanda take so ya zama shugaban majalisar wakilai da Ben Kalu daga Jihar Abia a matsayin mataimakinsa ya bar baya da kura.

A ranar Litinin ne jam’iyyar ta fitar da sunayen ‘yan majalisar dokokin da ta ke so su zama shugabannin majalisun dokoki ta 10 bayan da, a cewarta, ta tuntubi zababben shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.

  • Kotun Koli Ta Tabbatar Da Nasarar Adeleke A Matsayin Gwamnan Osun
  • ‘Yansanda Sun Kama Kauraye 72 Da Ake Zargi Da Kwacen Wayar Salula A Katsina

A bangaren majalisar dattawa, APC ta zabi Sanata Godswill Akpabio da Barau a matsayin wadanda take su zama shugaba da mataimakinsa.

Sai dai matakin da ta dauka a majalisar wakilai bai yi wa wasu manyan ‘yan majalisa dadi ba, abin da ake gani zai iya haddasa rikici.

Tuni wasu daga cikin wadanda suke zawarcin kujerar suka hau dokin na-ki, inda suka yi watsi da matakin jam’iyyar.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Amince Da Biyan Ma’aikata Karin Albashin N35,000 Na Wucin Gadi

Ilimin ‘Ya’ya Mata: Kano Ta Fara Bai Wa ‘Yan Mata 45,000 Tallafin N20, 000

Wadanda suke zawarcin kujerar shugaban majalisar tarayyar da suka ki amincewa da wannan mataki sun hada da Honarabul Idris Wase da Alhassan Ado Doguwa da Sada-Soli Jibiya.

Sauran sun hada da Honorabul Mukhtar Betara da kuma Ahmed Jaji.

Wasu daga cikin zababbun ‘yan majalisar wakilan wadanda suka nuna rashin jin dadinsu dangane da matakin jam’iyyar APC sun gudanar da wani taro a Abuja a ranar Litinin.

Sun kwatanta wannan mataki da uwar jam’iyyar ta dauka a matsayin yunkurin yi musu dauki-dora.

Cikin mahalarta taron har da Honarabul Wase da Ado Doguwa da Yusuf Gagdi and Sada-Soli da Mohammed Monguno.

Honorabul Wase shi ne mataimakin kakakin majalisar tarayya, kuma ya bayyana cewa wanda jam’iyyar APC ta zaba, Abbas Tajuddeen, ba mutum ba ne da ‘yan majalisa suka sani sosai.

Ya caccaki matakin da APC ta dauka, inda ya ce bai kamata a dauki irin wannan mataki ba tare da tuntubar masu ruwa da tsaki ba.

Shi ma Alhassan Ado Doguwa, wanda a yanzu shi ne shugaban masu rinjaye, ya bayyana cewa dole ne a bar majalisar ta rika zabar shugabanninta.

Ya bayyana cewa hakkinsu ne zabar shugaba a majalisa kuma bai kamata wasu daga waje su rika zaba mata shugaba ba.

“Wani sako da nake son aikawa shi ne majalisa wuri ne da dole ne a bari ya rinka zaba wa kansa shugaba. Batun wanda zai jagorance mu, wata matsala ce wadda ta shafe mu, mu kadai ba matsalar wani ba ce,” in ji Doguwa.

Tags: KuraMajalisar WakilaiShugabanniTinubuZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotun Koli Ta Tabbatar Da Nasarar Adeleke A Matsayin Gwamnan Osun

Next Post

Xi Ya Aikawa Takwaransa Na Ruwanda Sakon Jaje Game Da Balain Ruwan Sama

Related

Tinubu Ya Amince Da Biyan Ma’aikata Karin Albashin N35,000 Na Wucin Gadi
Manyan Labarai

Tinubu Ya Amince Da Biyan Ma’aikata Karin Albashin N35,000 Na Wucin Gadi

32 mins ago
Mata
Manyan Labarai

Ilimin ‘Ya’ya Mata: Kano Ta Fara Bai Wa ‘Yan Mata 45,000 Tallafin N20, 000

3 hours ago
BUA
Manyan Labarai

Daga Gobe 2 Ga Oktoba Farashin Buhun Simintin BUA Ya Koma N3,500 – Kamfanin

14 hours ago
Shekara 100 Da Kafa IAR: Da Sakamakon Bincikenmu Aka Kafa Ginshikin Tattalin Arzikin Arewacin Nijeriya —Farfesa Ishiyaku
Manyan Labarai

Shekara 100 Da Kafa IAR: Da Sakamakon Bincikenmu Aka Kafa Ginshikin Tattalin Arzikin Arewacin Nijeriya —Farfesa Ishiyaku

21 hours ago
Batun Yadda Samari Ke Barin Taimakon Iyaye Su Kashe Wa ‘Yan Mata Kudi
Madubin Rayuwa

Batun Yadda Samari Ke Barin Taimakon Iyaye Su Kashe Wa ‘Yan Mata Kudi

22 hours ago
APC
Manyan Labarai

Jawabin Shugaba Tinubu Kan Cikar Nijeriya Shekaru 63 Da Samun ‘Yancin Kai

1 day ago
Next Post
Xi Ya Aikawa Takwaransa Na Ruwanda Sakon Jaje Game Da Balain Ruwan Sama

Xi Ya Aikawa Takwaransa Na Ruwanda Sakon Jaje Game Da Balain Ruwan Sama

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Amince Da Biyan Ma’aikata Karin Albashin N35,000 Na Wucin Gadi

Tinubu Ya Amince Da Biyan Ma’aikata Karin Albashin N35,000 Na Wucin Gadi

October 2, 2023
Mata

Ilimin ‘Ya’ya Mata: Kano Ta Fara Bai Wa ‘Yan Mata 45,000 Tallafin N20, 000

October 2, 2023
Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

October 1, 2023
Tinubu

Ranar ‘Yanci: Tinubu Ya Kara Wa Kananan Ma’aikata N25,000 Kan Albashinsu

October 1, 2023
Hangzhou

Birnin Hangzhou Ya Samu Karuwar Masu Yawon Bude Ido Albarkacin Gasar Wasanni Ta Asiya Dake Gudana

October 1, 2023
Syria

Shugaban Syria: Manyan Tsare-tsare Uku Na duniya Su Ne Jagororin Sabuwar Duniya

October 1, 2023
BUA

Daga Gobe 2 Ga Oktoba Farashin Buhun Simintin BUA Ya Koma N3,500 – Kamfanin

October 1, 2023
Kasar Sin

Ofishin Jakadancin Kasar Sin Dake Najeriya Ya Shirya Bikin Murnar Cikar Sin Shekaru 74 Da Kafuwa

October 1, 2023
Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

October 1, 2023
Amurka

Amurka Ita Ce “Daular Karya”Ta Ko Wace Fuska

October 1, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.