ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin APC Na Zabar Sabon Kakakin Majalisar Wakilai Ya Tada Kura

by Sadiq
3 years ago
APC

Matakin da jam’iyyar APC mai mulki ta dauka na ayyana Honarabul Abbas Tajuddeen daga Jihar Kaduna a matsayin wanda take so ya zama shugaban majalisar wakilai da Ben Kalu daga Jihar Abia a matsayin mataimakinsa ya bar baya da kura.

A ranar Litinin ne jam’iyyar ta fitar da sunayen ‘yan majalisar dokokin da ta ke so su zama shugabannin majalisun dokoki ta 10 bayan da, a cewarta, ta tuntubi zababben shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.

  • Kotun Koli Ta Tabbatar Da Nasarar Adeleke A Matsayin Gwamnan Osun
  • ‘Yansanda Sun Kama Kauraye 72 Da Ake Zargi Da Kwacen Wayar Salula A Katsina

A bangaren majalisar dattawa, APC ta zabi Sanata Godswill Akpabio da Barau a matsayin wadanda take su zama shugaba da mataimakinsa.

ADVERTISEMENT

Sai dai matakin da ta dauka a majalisar wakilai bai yi wa wasu manyan ‘yan majalisa dadi ba, abin da ake gani zai iya haddasa rikici.

Tuni wasu daga cikin wadanda suke zawarcin kujerar suka hau dokin na-ki, inda suka yi watsi da matakin jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Wadanda suke zawarcin kujerar shugaban majalisar tarayyar da suka ki amincewa da wannan mataki sun hada da Honarabul Idris Wase da Alhassan Ado Doguwa da Sada-Soli Jibiya.

Sauran sun hada da Honorabul Mukhtar Betara da kuma Ahmed Jaji.

Wasu daga cikin zababbun ‘yan majalisar wakilan wadanda suka nuna rashin jin dadinsu dangane da matakin jam’iyyar APC sun gudanar da wani taro a Abuja a ranar Litinin.

Sun kwatanta wannan mataki da uwar jam’iyyar ta dauka a matsayin yunkurin yi musu dauki-dora.

Cikin mahalarta taron har da Honarabul Wase da Ado Doguwa da Yusuf Gagdi and Sada-Soli da Mohammed Monguno.

Honorabul Wase shi ne mataimakin kakakin majalisar tarayya, kuma ya bayyana cewa wanda jam’iyyar APC ta zaba, Abbas Tajuddeen, ba mutum ba ne da ‘yan majalisa suka sani sosai.

Ya caccaki matakin da APC ta dauka, inda ya ce bai kamata a dauki irin wannan mataki ba tare da tuntubar masu ruwa da tsaki ba.

Shi ma Alhassan Ado Doguwa, wanda a yanzu shi ne shugaban masu rinjaye, ya bayyana cewa dole ne a bar majalisar ta rika zabar shugabanninta.

Ya bayyana cewa hakkinsu ne zabar shugaba a majalisa kuma bai kamata wasu daga waje su rika zaba mata shugaba ba.

“Wani sako da nake son aikawa shi ne majalisa wuri ne da dole ne a bari ya rinka zaba wa kansa shugaba. Batun wanda zai jagorance mu, wata matsala ce wadda ta shafe mu, mu kadai ba matsalar wani ba ce,” in ji Doguwa.

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Xi Ya Aikawa Takwaransa Na Ruwanda Sakon Jaje Game Da Balain Ruwan Sama

Xi Ya Aikawa Takwaransa Na Ruwanda Sakon Jaje Game Da Balain Ruwan Sama

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.