• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Inganta Lafiya: An Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,213 A Zamfara

by Leadership Hausa
2 years ago
in Labarai
0
Shirin Inganta Lafiya: An Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,213 A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Zamfara ta kammala kashi na uku na Shirin Inganta Lafiyar al’umma Kyauta, inda aka duba mutane sama da 2,213.

Shirin na musamman da aka fara a watan Yulin bara, an samu nasarar duba lafiyar mutane masu fama da amosanin ido, gwaiwa, yoyon fitsari da aikin musamman tare da wayar da kan mutane sanin hanyoyin kauce wa kamuwa da cututtuka domin kiwon lafiyar su.

  • Gwamnan Zamfara Ya Raba Wa Makarantu 250 Kayan Karatu Da Fitilu Masu Amfani Da Hasken Rana A Jihar
  • Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Tashar Motocin Tilera Biyu A Birnin Gusau

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa an duba lafiyar mutane sama da 2,213 a yayin shirin a matakin farko da na biyu da na uku.

A cewar sa, kashi na uku ya kasance tsakanin ranakun 23 zuwa 25 ga watan Fabrairun 2024.

Sanarwar ta ce, “Gwamnatin Gwamna Dauda Lawal ta ƙaddamar da wani shirin inganta lafiyar jama’a kyauta domin bayar da tallafin kiwon lafiya ga mabuƙata. Shirin yana ba da magani kyauta ga mutanen da ke fama da yanayin lalurar rashin lafiya ta yau da kullum kamar su amosanin ido, amosanin mara, gwaiwa da yoyon fitsari.

Labarai Masu Nasaba

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

“Baya taimakon kiwon lafiya, shirin yana ilimantar da jama’a game da muhimmancin kiyaye lafiya da walwala. Wannan yunƙuri mataki ne mai kyau na inganta lafiya da jin daɗin al’umma gaba ɗaya.

“Ya zuwa yanzu an yi amfani da na’urorin zamani a shirin inganta lafiyar mutane 2,213 don ba da kulawa ta musamman ga majinyata daga karkara da birane, wanda ya ƙunshi ƙananan hukumomi 14 na jihar. Wannan tsarin ya bai wa marasa lafiya a wurare masu nisa damar samun kulawar kiwon lafiya da suke buƙata daga ƙwararrun likitoci.

“Shirin, a dukkan matakai, an samu masu lalurar gwaiwa 876, amosanin ido 931, da masu yoyon fitsari 84.

“Cibiyoyin da aka ware domin wayar da kan jama’a, sun haɗa da Babban Asibitin Gusau, Babban Asibitin Sarki Fahad, Asibitin Ƙwararru na Yariman Bakura, kuma za a tura dukkan waɗanda cutar tasu ta yi tsanani zuwa ga babban asibitin Tarayya da ke Gusau.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DaudaDubiyaLafiyaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Sin Ke Dora Muhimmanci Ga Zamanintarwa Da Ci Gaba Mai Inganci

Next Post

Matakin Kona Kai Da Sojin Amurka Ya Dauka Ya Diga Ayar Tambaya Ga ‘Yan Siyasar Amurka

Related

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

38 minutes ago
Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

2 hours ago
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya
Labarai

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

3 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

5 hours ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

5 hours ago
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

8 hours ago
Next Post
Matakin Kona Kai Da Sojin Amurka Ya Dauka Ya Diga Ayar Tambaya Ga ‘Yan Siyasar Amurka

Matakin Kona Kai Da Sojin Amurka Ya Dauka Ya Diga Ayar Tambaya Ga ‘Yan Siyasar Amurka

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

September 16, 2025
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.