• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Raba Wa Makarantu 250 Kayan Karatu Da Fitilu Masu Amfani Da Hasken Rana A Jihar

by Hussein Yero
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Raba Wa Makarantu 250 Kayan Karatu Da Fitilu Masu Amfani Da Hasken Rana A Jihar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani biki da aka gudanar a yau Laraba a Gusau, babban birnin Jihar Zamfara, gwamna Dauda Lawal ya kaddamar da rabon kayayyakin karatu a makarantun firamare 250 a fadin jihar.

Tallafin kayan karatun, hadin gwiwa ne tsakanin hukumar Ilimin bai daya ta Jihar (ZUBEB) da ta kasa (UBE) da kuma hukumar kula da Karatun kananan yara ta majalisar dinkin Duniya (UNICEF).

  • Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan Mutane 5, 10 Sun Jikkata A Hanyar Legas Zuwa Ibadan
  • Matsalar Tsaro: Za A Rufe Duk Layin Da Ba A Haɗa Shi Da NIN Ba – NCC

A jawabinsa, gwamna Dauda Lawal ya bayyana cewa, kayayyakin da za a raba na makarantu 250 ne, wadanda suka kunshi Littattafan Karatu 242,176 na fani daban-daban, ECCDE 200, ECCDE kujeru da tebura 25, kayan gwaje-gwaje 8,210 da Fitilu masu amfani da hasken rana daga UNICEF (NLP) don samar da haske a makarantun.

A yayin bikin kaddamar da kayayyakin, Gwamna Lawal ya bayyana cewa, jihar Zamfara da ke fama da karancin ilimi a Nijeriya, za ta ci gaba da bada tallafi da hadin kai ga abokan huldar kasa da kasa domin ciyar da ilimi gaba a jihar.

Ya ce, “Na yi farin cikin kasancewa a wannan gagarumin taron na raba kayan karatu ga dalibai a wannan sashin namu na ilimi. Wannan karamcin na daya daga cikin dimbin ayyukan da jihar Zamfara ke amfana da su.

Labarai Masu Nasaba

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

“Muna aikin gyaran makarantun Sakandare 60 a fadin jihar nan karkashin hukumar taimakon al’umma da ci gaban al’umma ta bankin duniya (CSDA). Kowace karamar hukuma tana da makarantun sakandare shida (6) da ake gyarawa, yayin da babban birnin jihar Gusau ke da takwas (8).

“Dokar ta-baci na ilimi da aka ayyana a jihar, bata ta’allaka ga ilimin farko da sakandare kawai ba har da manyan makarantu. Mun sanya dokar ta-baci a manyan makarantun jihar.”

Bugu da kari, gwamnan ya bayyana matakan da gwamnatinsa ta dauka na sasanta basussukan WAEC da NECO da gwamnatocin baya na jihar suka gaza biya.

Gwamna Dauda ya Kuma tabbatar da cewa, duk Shugaban Makarantar da aka samu wajan karkatar da kayan da aka raba ko aka sace Fitilun, to, a bakin aikin shugaban.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnan ZamfaraInganta Ilimi a ZamfaraTabarbarewar ilimi a Yankin Arewa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin: Abun Da Aka Sa Gaba Shi Ne Farfado Da Zaman Lafiya

Next Post

Tinubu Ya Tafi Kasar Qatar Don Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kasuwanci

Related

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa
Labarai

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

3 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

4 hours ago
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma
Labarai

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

5 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

6 hours ago
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano
Manyan Labarai

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

7 hours ago
Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba
Labarai

Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba

8 hours ago
Next Post
Tinubu Ya Tafi Kasar Qatar Don Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kasuwanci

Tinubu Ya Tafi Kasar Qatar Don Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kasuwanci

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.