ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Raba Wa Makarantu 250 Kayan Karatu Da Fitilu Masu Amfani Da Hasken Rana A Jihar

by Hussein Yero
2 years ago
Zamfara

A wani biki da aka gudanar a yau Laraba a Gusau, babban birnin Jihar Zamfara, gwamna Dauda Lawal ya kaddamar da rabon kayayyakin karatu a makarantun firamare 250 a fadin jihar.

Tallafin kayan karatun, hadin gwiwa ne tsakanin hukumar Ilimin bai daya ta Jihar (ZUBEB) da ta kasa (UBE) da kuma hukumar kula da Karatun kananan yara ta majalisar dinkin Duniya (UNICEF).

  • Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan Mutane 5, 10 Sun Jikkata A Hanyar Legas Zuwa Ibadan
  • Matsalar Tsaro: Za A Rufe Duk Layin Da Ba A Haɗa Shi Da NIN Ba – NCC

A jawabinsa, gwamna Dauda Lawal ya bayyana cewa, kayayyakin da za a raba na makarantu 250 ne, wadanda suka kunshi Littattafan Karatu 242,176 na fani daban-daban, ECCDE 200, ECCDE kujeru da tebura 25, kayan gwaje-gwaje 8,210 da Fitilu masu amfani da hasken rana daga UNICEF (NLP) don samar da haske a makarantun.

ADVERTISEMENT

A yayin bikin kaddamar da kayayyakin, Gwamna Lawal ya bayyana cewa, jihar Zamfara da ke fama da karancin ilimi a Nijeriya, za ta ci gaba da bada tallafi da hadin kai ga abokan huldar kasa da kasa domin ciyar da ilimi gaba a jihar.

Ya ce, “Na yi farin cikin kasancewa a wannan gagarumin taron na raba kayan karatu ga dalibai a wannan sashin namu na ilimi. Wannan karamcin na daya daga cikin dimbin ayyukan da jihar Zamfara ke amfana da su.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

“Muna aikin gyaran makarantun Sakandare 60 a fadin jihar nan karkashin hukumar taimakon al’umma da ci gaban al’umma ta bankin duniya (CSDA). Kowace karamar hukuma tana da makarantun sakandare shida (6) da ake gyarawa, yayin da babban birnin jihar Gusau ke da takwas (8).

“Dokar ta-baci na ilimi da aka ayyana a jihar, bata ta’allaka ga ilimin farko da sakandare kawai ba har da manyan makarantu. Mun sanya dokar ta-baci a manyan makarantun jihar.”

Bugu da kari, gwamnan ya bayyana matakan da gwamnatinsa ta dauka na sasanta basussukan WAEC da NECO da gwamnatocin baya na jihar suka gaza biya.

Gwamna Dauda ya Kuma tabbatar da cewa, duk Shugaban Makarantar da aka samu wajan karkatar da kayan da aka raba ko aka sace Fitilun, to, a bakin aikin shugaban.

Zamfara
Hussein Yero
+ postsBio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Ɗan Takarar Sanata A Zamfara Ya Koka Kan Yi Wa Rayuwarsa Barazana
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Abdulaziz Yari Ya Bukaci Limamai Su Ƙara Addu’a Kan Yaƙi Da Ƴan Bindiga A Zamfara
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Matawalle Ya Buƙaci Magoya Bayansa Su Mara Wa Shugaba Tinubu, Gwamna Lawal Baya
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Majalisar Zamfara Ta Dakatar Da Shugabannin Kananan Hukumomi Biyu Kan Zargin Almundahanar Kuɗaɗe

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Tinubu Ya Tafi Kasar Qatar Don Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kasuwanci

Tinubu Ya Tafi Kasar Qatar Don Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kasuwanci

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.