Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya aika da tawagar gwamnatin tarayya zuwa jihar Neja domin jajanta wa gwamnatin jihar da al’ummar Mokwa bisa mummunar ambaliya da ta hallaka mutane fiye da 151 tare da raba sama da mutum 3,000 da muhallansu.
Tawagar ta haɗa da Ministan Watsa Labarai da Wayar da kan Jama’a, Mohammed Idris, da Ministan harkokin Jin ƙai Farfesa Nentawe Yilwatda.
- Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sanadin Ambaliya A Neja Ya Karu Zuwa 115
- Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas
Minista Idris ya bayyana cewa shugaban ƙasa ya damu matuƙa da iftila’in da ya auku, inda ya umarci Hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA) da ta tura kayan agaji da taimako cikin gaggawa. Ya kuma bayyana cewa ana shirin ƙara fadada wayar da kan jama’a musamman ga waɗanda ke zaune a yankunan da ake fama da ambaliya.
A nasa jawabin, Farfesa Yilwatda ya ce gwamnatin tarayya ta umurci Hukumar Kula da ’Yan Gudun Hijira da wadanda Aka Raba da Gidajensu da ta ci gaba da ba da tallafi ga waɗanda lamarin ya rutsa da su, bayan NEMA ta kammala aikinta na farko. Ya tabbatar da cewa gwamnatin tarayya za ta ɗauki matakan sake gina manyan hanyoyi da gine-ginen da ambaliya ta lalata.
Mataimakin Gwamnan Neja, Kwamared Yakubu Garba, ya gode wa shugaban ƙasa bisa wannan saurin kai agaji da nuna kulawa. Ya bayyana cewa gidaje 264 da gidajen iyali 503 sun rushe, yayin da gada uku da hanyoyin cikin gari suka lalace gaba daya, lamarin da ya jefa Mokwa cikin matsanancin hali.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp