ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samarwa Sojoji Manyan Makamai Ne Mafita – Shugaban Ƙaramar Hukumar Bukuyum

by Abubakar Sulaiman
1 week ago
shugaban

Shugaban Ƙaramar Hukumar Bukuyum a Jihar Zamfara, Abubakar Umar Faru, ya buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta bai wa jami’an tsaro makamai na zamani domin ƙaddamar da cikakken farmaki a kan ƴan bindiga da ke ɓoye a Gandun Dajin Gando.

A wata hira da ya yi da DCL Hausa, Faru ya bayyana cewa ya mika cikakkun bayanan wuraren da ƴan bindigar ke fakewa jami’an tsaro, amma ya ce rashin manyan kayan yaƙi na hana su shiga dajin domin kawo ƙarshen matsalar gaba ɗaya.

  • Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Sabon Tsarin Ci Gaban Zamfara Na Shekaru 10
  • Uwargidan Shugaban Kasa Ta Bai Wa Nakasassu 250 Tallafi A Zamfara

Ya ƙara da cewa Gandun Dajin Gando ya zama babbar mafakar ƴan bindiga, musamman bayan wasu daga cikinsu da suka yi sulhu a sassan Katsina da Birnin Gwari a Jihar Kaduna sun koma Zamfara. A cewarsa, wannan sauyin wuri ya ƙara tsananta matsalar tsaro a yankin.

ADVERTISEMENT

Shugaban ƙaramar hukumar ya yabawa ƙoƙarin jami’an tsaro da ke yankin, amma ya jaddada cewa sai an kai farmaki kai tsaye cikin daji kafin a iya murƙushe ƴan bindigar. Ya kuma zargi ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, da gazawa wajen amfani da matsayinsa domin kawo ƙarshen matsalar, duk da kasancewarsa ɗan asalin Zamfara.

Faru ya ce gwamnatin jiha da ƙananan hukumomi na ƙoƙari gwargwadon ikon da kundin tsarin mulki ya ba su, amma ya bayyana cewa ikon bayar da umarni ga jami’an tsaro na hannun gwamnatin tarayya ne. Gandun Dajin Gando, wanda a baya ake amfani da shi wajen noma da kiwo, ya zama cibiyar ƴan bindiga, lamarin da ya haddasa ƙaura da durƙushewar harkokin noma a Zamfara.

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Next Post
Abubuwan Da Ba Ku Ji Ba Kan Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi

Abubuwan Da Ba Ku Ji Ba Kan Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.