ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Sabon Tsarin Ci Gaban Zamfara Na Shekaru 10

by Sulaiman
6 months ago
Gwamna Lawal

Gwamna Dauda Lawal ya ƙaddamar da sabon Tsarin Ci Gaban Jihar Zamfara na 2025 zuwa 2034, wani tsari mai dogon zango da aka gina bisa bincike, bayanai, da tattaunawa da ƙwararru domin sake fasalin jihar a shekaru goma masu zuwa.

 

An gabatar da shirin ne a sakateriyar JB Yakubu da ke Gusau a ranar Juma’a, a wani taron da ya tattaro manyan jami’an gwamnati, shugabannin gargajiya da na addini, da ƙwararrun masana a fannin bunƙasar tattalin arziki.

ADVERTISEMENT
  • Sin Na Kokarin Yin Kirkire-kirkire Don Sa Kaimi Ga Samun Moriyar Juna A Duniya
  • Ƴansanda Sun Fara Tabbatar Da Dokar Hana Zirga-zigar Babura A Kano

A cewar mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, gwamnatin jihar ta ɗauki kwamitin KPMG a matsayin babban mai ba da shawara domin aikin tsare-tsaren.

 

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

A tsawon watanni takwas, kwamitin KPMG ya yi aiki tare da Majalisar Zartarwa ta Jihar Zamfara da sauran masu ruwa da tsaki wajen haɗa gagarumin shirin da ya ƙunshi muhimman fannoni na ci gaba.

 

Da yake jawabi yayin ƙaddamarwar, Gwamna Lawal ya bayyana wannan tsari a matsayin shiri mafi inganci da Zamfara ta samu a tarihi, wanda ya yi daidai da manyan tsare-tsaren ci gaban ƙasa da na duniya.

 

Ya ambaci tsarin SDG, Babban Tsarin Ci Gaba na 2050, da Ajandar 2063 ta Tarayyar Afrika a matsayin muhimman ginshiƙai da tsarin ya jingina da su.

 

Gwamnan ya ce, sabon Tsarin Ci Gaban ya fayyace komai dalla-dalla, yana kuma ɗauke da ma’auni da hanyoyin sa ido domin a gano yadda ake tafiya a mataki-mataki.

 

“Mun gina shirin ne kan bayanai ingantattu da haɗin kan jama’a. A cikin wannan tsari, muna hango Zamfara da ta zama abin misali wajen ci gaban tattalin arziki a Nijeriya, hatta a nahiyar Afrika,” in ji shi.

 

Ya bayyana ginshiƙan tsari guda shida da za su zama tubalin aiwatarwa: Tattalin Arziki, Ababen More Rayuwa, Jinƙai da Walwalar Jama’a, Jarin Ɗan Adam, Gwamnati Mai Gaskiya da Nagarta, Kare Muhalli da Ɗorewar Albarkatun Ƙasa.

 

Gwamna Lawal ya ce, jihar za ta ci gajiyar ƙarfin ta a noman zamani da albarkatun ƙasa, ta hanyar haɗin gwiwa da cibiyoyi irin su MoFI da Bankin Vi Gaban Afrika, domin ƙara yawan amfanin gona, faɗaɗa ayyuka, da rage talauci da rashin tsaro.

 

“A yau ba magana kawai muke yi ba — muna kafa tubalin gobe. Muna gyara makomar Zamfara. Muna mayar da fata ga matasa, kariya ga masu rauni, da damar arziki ga al’umma,” in ji shi.

 

Ya ce, ƙaddamar da shirin ba wata manufa ta siyasa ba ce, illa wani sabon salo da jihar ke shiga domin ceto kanta daga koma baya.

 

“Lokacin da Zamfara ta haɗu da ƙalubale, ba da kuka muka tashi ba. Mun tashi da hangen nesa da jajircewa ne. Wannan tsari shi ne sabuwar hanyar da za ta zame mana haske a gaba,” in ji gwamnan.

 

A taron, Sakataren Gwamnati na Jihar Zamfara, Mallam Abubakar Nakwada; Shugaban Ma’aikata, Mukhtar Lugga; da Kwamishinan Tsare-Tsare da Kasafin Kuɗi, Abdulmalik Abubakar Gajam, sun gabatar da jawabai masu nuni da muhimmancin sabon tsarin.

Gwamna Lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
An Yi Taron Kara Wa Juna Sani Kan Kare Hakkokin Dan Adam Na Sin Da Afirka Ta Kudu A Pretoria

An Yi Taron Kara Wa Juna Sani Kan Kare Hakkokin Dan Adam Na Sin Da Afirka Ta Kudu A Pretoria

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.