ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Sabon Tsarin Ci Gaban Zamfara Na Shekaru 10

by Sulaiman
7 months ago
Gwamna Lawal

Gwamna Dauda Lawal ya ƙaddamar da sabon Tsarin Ci Gaban Jihar Zamfara na 2025 zuwa 2034, wani tsari mai dogon zango da aka gina bisa bincike, bayanai, da tattaunawa da ƙwararru domin sake fasalin jihar a shekaru goma masu zuwa.

 

An gabatar da shirin ne a sakateriyar JB Yakubu da ke Gusau a ranar Juma’a, a wani taron da ya tattaro manyan jami’an gwamnati, shugabannin gargajiya da na addini, da ƙwararrun masana a fannin bunƙasar tattalin arziki.

ADVERTISEMENT
  • Sin Na Kokarin Yin Kirkire-kirkire Don Sa Kaimi Ga Samun Moriyar Juna A Duniya
  • Ƴansanda Sun Fara Tabbatar Da Dokar Hana Zirga-zigar Babura A Kano

A cewar mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, gwamnatin jihar ta ɗauki kwamitin KPMG a matsayin babban mai ba da shawara domin aikin tsare-tsaren.

 

LABARAI MASU NASABA

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

A tsawon watanni takwas, kwamitin KPMG ya yi aiki tare da Majalisar Zartarwa ta Jihar Zamfara da sauran masu ruwa da tsaki wajen haɗa gagarumin shirin da ya ƙunshi muhimman fannoni na ci gaba.

 

Da yake jawabi yayin ƙaddamarwar, Gwamna Lawal ya bayyana wannan tsari a matsayin shiri mafi inganci da Zamfara ta samu a tarihi, wanda ya yi daidai da manyan tsare-tsaren ci gaban ƙasa da na duniya.

 

Ya ambaci tsarin SDG, Babban Tsarin Ci Gaba na 2050, da Ajandar 2063 ta Tarayyar Afrika a matsayin muhimman ginshiƙai da tsarin ya jingina da su.

 

Gwamnan ya ce, sabon Tsarin Ci Gaban ya fayyace komai dalla-dalla, yana kuma ɗauke da ma’auni da hanyoyin sa ido domin a gano yadda ake tafiya a mataki-mataki.

 

“Mun gina shirin ne kan bayanai ingantattu da haɗin kan jama’a. A cikin wannan tsari, muna hango Zamfara da ta zama abin misali wajen ci gaban tattalin arziki a Nijeriya, hatta a nahiyar Afrika,” in ji shi.

 

Ya bayyana ginshiƙan tsari guda shida da za su zama tubalin aiwatarwa: Tattalin Arziki, Ababen More Rayuwa, Jinƙai da Walwalar Jama’a, Jarin Ɗan Adam, Gwamnati Mai Gaskiya da Nagarta, Kare Muhalli da Ɗorewar Albarkatun Ƙasa.

 

Gwamna Lawal ya ce, jihar za ta ci gajiyar ƙarfin ta a noman zamani da albarkatun ƙasa, ta hanyar haɗin gwiwa da cibiyoyi irin su MoFI da Bankin Vi Gaban Afrika, domin ƙara yawan amfanin gona, faɗaɗa ayyuka, da rage talauci da rashin tsaro.

 

“A yau ba magana kawai muke yi ba — muna kafa tubalin gobe. Muna gyara makomar Zamfara. Muna mayar da fata ga matasa, kariya ga masu rauni, da damar arziki ga al’umma,” in ji shi.

 

Ya ce, ƙaddamar da shirin ba wata manufa ta siyasa ba ce, illa wani sabon salo da jihar ke shiga domin ceto kanta daga koma baya.

 

“Lokacin da Zamfara ta haɗu da ƙalubale, ba da kuka muka tashi ba. Mun tashi da hangen nesa da jajircewa ne. Wannan tsari shi ne sabuwar hanyar da za ta zame mana haske a gaba,” in ji gwamnan.

 

A taron, Sakataren Gwamnati na Jihar Zamfara, Mallam Abubakar Nakwada; Shugaban Ma’aikata, Mukhtar Lugga; da Kwamishinan Tsare-Tsare da Kasafin Kuɗi, Abdulmalik Abubakar Gajam, sun gabatar da jawabai masu nuni da muhimmancin sabon tsarin.

Gwamna Lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
  • Sulaiman
    Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya
  • Sulaiman
    Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara
  • Sulaiman
    Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

MASU ALAKA

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara
Labarai

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi
Labarai

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
Next Post
An Yi Taron Kara Wa Juna Sani Kan Kare Hakkokin Dan Adam Na Sin Da Afirka Ta Kudu A Pretoria

An Yi Taron Kara Wa Juna Sani Kan Kare Hakkokin Dan Adam Na Sin Da Afirka Ta Kudu A Pretoria

LABARAI MASU NASABA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.