ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Sabon Tsarin Ci Gaban Zamfara Na Shekaru 10

by Sulaiman
9 months ago
Gwamna Lawal

Gwamna Dauda Lawal ya ƙaddamar da sabon Tsarin Ci Gaban Jihar Zamfara na 2025 zuwa 2034, wani tsari mai dogon zango da aka gina bisa bincike, bayanai, da tattaunawa da ƙwararru domin sake fasalin jihar a shekaru goma masu zuwa.

 

An gabatar da shirin ne a sakateriyar JB Yakubu da ke Gusau a ranar Juma’a, a wani taron da ya tattaro manyan jami’an gwamnati, shugabannin gargajiya da na addini, da ƙwararrun masana a fannin bunƙasar tattalin arziki.

ADVERTISEMENT
  • Sin Na Kokarin Yin Kirkire-kirkire Don Sa Kaimi Ga Samun Moriyar Juna A Duniya
  • Ƴansanda Sun Fara Tabbatar Da Dokar Hana Zirga-zigar Babura A Kano

A cewar mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, gwamnatin jihar ta ɗauki kwamitin KPMG a matsayin babban mai ba da shawara domin aikin tsare-tsaren.

 

LABARAI MASU NASABA

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

A tsawon watanni takwas, kwamitin KPMG ya yi aiki tare da Majalisar Zartarwa ta Jihar Zamfara da sauran masu ruwa da tsaki wajen haɗa gagarumin shirin da ya ƙunshi muhimman fannoni na ci gaba.

 

Da yake jawabi yayin ƙaddamarwar, Gwamna Lawal ya bayyana wannan tsari a matsayin shiri mafi inganci da Zamfara ta samu a tarihi, wanda ya yi daidai da manyan tsare-tsaren ci gaban ƙasa da na duniya.

 

Ya ambaci tsarin SDG, Babban Tsarin Ci Gaba na 2050, da Ajandar 2063 ta Tarayyar Afrika a matsayin muhimman ginshiƙai da tsarin ya jingina da su.

 

Gwamnan ya ce, sabon Tsarin Ci Gaban ya fayyace komai dalla-dalla, yana kuma ɗauke da ma’auni da hanyoyin sa ido domin a gano yadda ake tafiya a mataki-mataki.

 

“Mun gina shirin ne kan bayanai ingantattu da haɗin kan jama’a. A cikin wannan tsari, muna hango Zamfara da ta zama abin misali wajen ci gaban tattalin arziki a Nijeriya, hatta a nahiyar Afrika,” in ji shi.

 

Ya bayyana ginshiƙan tsari guda shida da za su zama tubalin aiwatarwa: Tattalin Arziki, Ababen More Rayuwa, Jinƙai da Walwalar Jama’a, Jarin Ɗan Adam, Gwamnati Mai Gaskiya da Nagarta, Kare Muhalli da Ɗorewar Albarkatun Ƙasa.

 

Gwamna Lawal ya ce, jihar za ta ci gajiyar ƙarfin ta a noman zamani da albarkatun ƙasa, ta hanyar haɗin gwiwa da cibiyoyi irin su MoFI da Bankin Vi Gaban Afrika, domin ƙara yawan amfanin gona, faɗaɗa ayyuka, da rage talauci da rashin tsaro.

 

“A yau ba magana kawai muke yi ba — muna kafa tubalin gobe. Muna gyara makomar Zamfara. Muna mayar da fata ga matasa, kariya ga masu rauni, da damar arziki ga al’umma,” in ji shi.

 

Ya ce, ƙaddamar da shirin ba wata manufa ta siyasa ba ce, illa wani sabon salo da jihar ke shiga domin ceto kanta daga koma baya.

 

“Lokacin da Zamfara ta haɗu da ƙalubale, ba da kuka muka tashi ba. Mun tashi da hangen nesa da jajircewa ne. Wannan tsari shi ne sabuwar hanyar da za ta zame mana haske a gaba,” in ji gwamnan.

 

A taron, Sakataren Gwamnati na Jihar Zamfara, Mallam Abubakar Nakwada; Shugaban Ma’aikata, Mukhtar Lugga; da Kwamishinan Tsare-Tsare da Kasafin Kuɗi, Abdulmalik Abubakar Gajam, sun gabatar da jawabai masu nuni da muhimmancin sabon tsarin.

Gwamna Lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

MASU ALAKA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Next Post
An Yi Taron Kara Wa Juna Sani Kan Kare Hakkokin Dan Adam Na Sin Da Afirka Ta Kudu A Pretoria

An Yi Taron Kara Wa Juna Sani Kan Kare Hakkokin Dan Adam Na Sin Da Afirka Ta Kudu A Pretoria

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.