ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Sabon Tsarin Ci Gaban Zamfara Na Shekaru 10

by Sulaiman
6 months ago
Gwamna Lawal

Gwamna Dauda Lawal ya ƙaddamar da sabon Tsarin Ci Gaban Jihar Zamfara na 2025 zuwa 2034, wani tsari mai dogon zango da aka gina bisa bincike, bayanai, da tattaunawa da ƙwararru domin sake fasalin jihar a shekaru goma masu zuwa.

 

An gabatar da shirin ne a sakateriyar JB Yakubu da ke Gusau a ranar Juma’a, a wani taron da ya tattaro manyan jami’an gwamnati, shugabannin gargajiya da na addini, da ƙwararrun masana a fannin bunƙasar tattalin arziki.

ADVERTISEMENT
  • Sin Na Kokarin Yin Kirkire-kirkire Don Sa Kaimi Ga Samun Moriyar Juna A Duniya
  • Ƴansanda Sun Fara Tabbatar Da Dokar Hana Zirga-zigar Babura A Kano

A cewar mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, gwamnatin jihar ta ɗauki kwamitin KPMG a matsayin babban mai ba da shawara domin aikin tsare-tsaren.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

A tsawon watanni takwas, kwamitin KPMG ya yi aiki tare da Majalisar Zartarwa ta Jihar Zamfara da sauran masu ruwa da tsaki wajen haɗa gagarumin shirin da ya ƙunshi muhimman fannoni na ci gaba.

 

Da yake jawabi yayin ƙaddamarwar, Gwamna Lawal ya bayyana wannan tsari a matsayin shiri mafi inganci da Zamfara ta samu a tarihi, wanda ya yi daidai da manyan tsare-tsaren ci gaban ƙasa da na duniya.

 

Ya ambaci tsarin SDG, Babban Tsarin Ci Gaba na 2050, da Ajandar 2063 ta Tarayyar Afrika a matsayin muhimman ginshiƙai da tsarin ya jingina da su.

 

Gwamnan ya ce, sabon Tsarin Ci Gaban ya fayyace komai dalla-dalla, yana kuma ɗauke da ma’auni da hanyoyin sa ido domin a gano yadda ake tafiya a mataki-mataki.

 

“Mun gina shirin ne kan bayanai ingantattu da haɗin kan jama’a. A cikin wannan tsari, muna hango Zamfara da ta zama abin misali wajen ci gaban tattalin arziki a Nijeriya, hatta a nahiyar Afrika,” in ji shi.

 

Ya bayyana ginshiƙan tsari guda shida da za su zama tubalin aiwatarwa: Tattalin Arziki, Ababen More Rayuwa, Jinƙai da Walwalar Jama’a, Jarin Ɗan Adam, Gwamnati Mai Gaskiya da Nagarta, Kare Muhalli da Ɗorewar Albarkatun Ƙasa.

 

Gwamna Lawal ya ce, jihar za ta ci gajiyar ƙarfin ta a noman zamani da albarkatun ƙasa, ta hanyar haɗin gwiwa da cibiyoyi irin su MoFI da Bankin Vi Gaban Afrika, domin ƙara yawan amfanin gona, faɗaɗa ayyuka, da rage talauci da rashin tsaro.

 

“A yau ba magana kawai muke yi ba — muna kafa tubalin gobe. Muna gyara makomar Zamfara. Muna mayar da fata ga matasa, kariya ga masu rauni, da damar arziki ga al’umma,” in ji shi.

 

Ya ce, ƙaddamar da shirin ba wata manufa ta siyasa ba ce, illa wani sabon salo da jihar ke shiga domin ceto kanta daga koma baya.

 

“Lokacin da Zamfara ta haɗu da ƙalubale, ba da kuka muka tashi ba. Mun tashi da hangen nesa da jajircewa ne. Wannan tsari shi ne sabuwar hanyar da za ta zame mana haske a gaba,” in ji gwamnan.

 

A taron, Sakataren Gwamnati na Jihar Zamfara, Mallam Abubakar Nakwada; Shugaban Ma’aikata, Mukhtar Lugga; da Kwamishinan Tsare-Tsare da Kasafin Kuɗi, Abdulmalik Abubakar Gajam, sun gabatar da jawabai masu nuni da muhimmancin sabon tsarin.

Gwamna Lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
Labarai

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Next Post
An Yi Taron Kara Wa Juna Sani Kan Kare Hakkokin Dan Adam Na Sin Da Afirka Ta Kudu A Pretoria

An Yi Taron Kara Wa Juna Sani Kan Kare Hakkokin Dan Adam Na Sin Da Afirka Ta Kudu A Pretoria

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.