• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Ƙasar Liberia Joseph Boakai Ya Rage Albashinsa da Kashi 40%

by Abubakar Sulaiman
12 months ago
in Kasashen Ketare
0
Shugaban Ƙasar Liberia Joseph Boakai Ya Rage Albashinsa da Kashi 40%
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Shugaban ƙasar Liberia, Joseph Boakai, ya sanar da rage albashinsa na shekara da kashi 40% daga $13,400 zuwa $8,000. Wannan shawara ta zo ne a lokacin da jama’a ke kara matsa lamba kan albashin gwamnati da kuma yawan fushin talakawa game da tsadar rayuwa, inda kimanin kashi 20% na al’ummar ƙasar ke rayuwa a ƙasa da $2 a rana. Ofishin Shugaba Boakai ya bayyana cewa yana fatan kafa misali na shugabanci nagari da kuma nuna jituwa da al’ummar Liberia.

Sai dai kuma ra’ayoyi game da rage albashin sun sha bamban. Yayin da wasu ke yabawa da wannan mataki, wasu kuwa suna tambayar muhimmancinsa ganin cewa shugaban na ci gaba da karɓar wasu alawus-alawus da kuma kula da lafiyarsa.

Anderson D. Miamen na Cibiyar Gaskiya da Rikon Amana a Liberia ya kira matakin da cewa “mai kyau,” yayin da W. Lawrence Yealue II, wanda ƙungiyarsa ke fafutukar ganin gaskiya a cikin gwamnatin, ya bayyana matakin a matsayin “abin yabawa.”

  • Wane Irin Tasiri Magudin Gwaje-gwaje Da Kamfanonin Samar Da Motoci Na Japan Suka Yi Zai Yi Ga Kasar?
  • Ministan Harkokin Kasar Wajen Kasar Sin Da Takwaransa Na Iran Sun Tattauna Ta Wayar Tarho Kan Rikicin Isra’ila Da Iran

Shugaba Boakai ya kuma ƙuduri aniyar ƙarfafa hukumar kula da ayyukan Jama’a ta Liberia don tabbatar da biyan albashi na adalci ga ma’aikatan gwamnati. Tun lokacin da ya hau karagar mulki a watan Janairu, ya ba da fifiko wajen yaƙi da cin hanci da rashawa da kuma rashin darajar kuɗin ƙasar, ya bayyana kadarorinsa, sannan ya ba da umarnin gudanar da bincike kan ofishin shugaban ƙasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Liberia
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsoffin Shugabannin Sin Da Guinea Bissau Sun Taka Rawar Gani Wajen Kirkirar Zumunci Tsakanin Kasashen Biyu

Next Post

Hukumar Tsaron Yanar Gizo Ta Kasar Sin Ta Fayyace Wani Shirin Yaudara Na Amurka

Related

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?
Kasashen Ketare

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

2 hours ago
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025
Kasashen Ketare

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

4 hours ago
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17
Kasashen Ketare

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

17 hours ago
Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump
Kasashen Ketare

Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

4 days ago
Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?
Kasashen Ketare

Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?

6 days ago
Iran Ta Bayyana Sharaɗin Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje
Kasashen Ketare

Iran Ta Bayyana Sharaɗin Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje

1 week ago
Next Post
Hukumar Tsaron Yanar Gizo Ta Kasar Sin Ta Fayyace Wani Shirin Yaudara Na Amurka

Hukumar Tsaron Yanar Gizo Ta Kasar Sin Ta Fayyace Wani Shirin Yaudara Na Amurka

LABARAI MASU NASABA

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.