• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban INEC Ya Tafka Aika-Aika Fiye Da Emefiele, Ya Kamata A Kore Shi —Buba Galadima

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Shugaban INEC Ya Tafka Aika-Aika Fiye Da Emefiele, Ya Kamata A Kore Shi —Buba Galadima
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jigo a jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya yi kira ga shugaba Bola Tinubu da ya kori Mahmood Yakubu, Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC).

Ya yi magana ne a cikin wata hira da gidan talabijin na Channels.

  • Ganduje Ya Yi Allah-wadai Da Dakatar Da Albashin Ma’aikatan Da Gwamnatinsa Ta Dauka
  • Tinubu Na Bukatar Addu’a —Gbajabiamila

Galadima ya zargi shugaban INEC da yin zagon kasa ga ‘yan Nijeriya a zaben shugaban kasa da ya gabata.

Ya ce abin da Yakubu ya yi ya fi “zunuban” da Godwin Emefiele, Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya aikata.

“Dole ne shugaban INEC ya tafi, abin da ya yi ya fi abin da Godwin Emefiele ya yi. Ya hada baki da wasu mutane domin su muzgunawa ‘yan Nijeriya. Ya aikata laifi mafi girma da kowa zai yi,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a karkashin Yakubu ta sha suka sosai kan gazawarta na saka sakamakon zabe kamar yadda ta yi alkawari, lamarin da hukumar zaben ta dora alhakin tabarbarewar fasaha.

A wani taron manema labarai da ta gudanar a ranar Talata, tawagar da ke sa ido kan zabuka ta Tarayyar Turai ta ce amincewar da jama’a ke da ita ga hukumar ta yi matukar illa.

Amma da yake mayar da martani, Festus Okoye, ya ce matsalar da aka samu wajen dora sakamakon zaben shugaban kasa na ranar 25 ga watan Fabrairu, bai kamata ya kawar da dukan zaben da aka gudanar a asar baki daya ba.

“Ba daidai ba ne a yi la’akari da dukkan ayyukan hukumar bisa ga kura-kuran da aka samu a sakamakon zaben shugaban kasa,” in ji shi.

Da yake karin haske a hirar ta gidan talabijin, Galadima ya shaidawa tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP da kuma Peter Obi na jam’iyyar Labour cewa suna bata lokaci suna kalubalantar nasarar shugaba Bola Tinubu.

Obi da Atiku sun gurfana gaban kotu domin kalubalantar nasarar Tinubu.

Sai dai Galadima, wanda ya yi ikirarin cewa an daura auren ne da kura-kurai, ya kara da cewa sakamakon zaben shugaban kasa da kotuna ba ta taba yin watsi da shi ba tun 1979.

M“Wane dan siyasa ne ya yi nasara a kotu tun 1979 a Nijeriya a karar da ya shigar da shugaban kasa? Me ya sa za mu barnata biliyan 10 ko biliyan 15 saboda mun ji wasu na kashe irin wadannan biliyoyin kudi a shafukan sada zumunta a kotun; idan muna da irin wadannan kudade za mu yi amfani da su wajen shiryawa babban zaben 2027.

“Jam’iyyar NNPP tana da karfi, idan ban da INEC ta goge tambarinmu a wasu jihohi, da mun yi nasara fiye da yadda ake zato,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Buba GaladimaCBNEmefieleINECNNPP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ganduje Ya Yi Allah-wadai Da Dakatar Da Albashin Ma’aikatan Da Gwamnatinsa Ta Dauka

Next Post

Dalibai Sun ‘Yantar Da Fursunoni 6 A Gidan Yarin Suleja

Related

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

1 hour ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

20 hours ago
Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara
Manyan Labarai

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

2 days ago
Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin
Manyan Labarai

Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin

2 days ago
Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano
Manyan Labarai

Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano

2 days ago
Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

2 days ago
Next Post
Dalibai Sun ‘Yantar Da Fursunoni 6 A Gidan Yarin Suleja

Dalibai Sun 'Yantar Da Fursunoni 6 A Gidan Yarin Suleja

LABARAI MASU NASABA

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

August 9, 2025
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

August 9, 2025
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

August 9, 2025
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

August 9, 2025
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

August 9, 2025
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

August 9, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

August 9, 2025
Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

August 9, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

August 9, 2025
ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.