• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban INEC Ya Tafka Aika-Aika Fiye Da Emefiele, Ya Kamata A Kore Shi —Buba Galadima

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Shugaban INEC Ya Tafka Aika-Aika Fiye Da Emefiele, Ya Kamata A Kore Shi —Buba Galadima
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jigo a jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya yi kira ga shugaba Bola Tinubu da ya kori Mahmood Yakubu, Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC).

Ya yi magana ne a cikin wata hira da gidan talabijin na Channels.

  • Ganduje Ya Yi Allah-wadai Da Dakatar Da Albashin Ma’aikatan Da Gwamnatinsa Ta Dauka
  • Tinubu Na Bukatar Addu’a —Gbajabiamila

Galadima ya zargi shugaban INEC da yin zagon kasa ga ‘yan Nijeriya a zaben shugaban kasa da ya gabata.

Ya ce abin da Yakubu ya yi ya fi “zunuban” da Godwin Emefiele, Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya aikata.

“Dole ne shugaban INEC ya tafi, abin da ya yi ya fi abin da Godwin Emefiele ya yi. Ya hada baki da wasu mutane domin su muzgunawa ‘yan Nijeriya. Ya aikata laifi mafi girma da kowa zai yi,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a karkashin Yakubu ta sha suka sosai kan gazawarta na saka sakamakon zabe kamar yadda ta yi alkawari, lamarin da hukumar zaben ta dora alhakin tabarbarewar fasaha.

A wani taron manema labarai da ta gudanar a ranar Talata, tawagar da ke sa ido kan zabuka ta Tarayyar Turai ta ce amincewar da jama’a ke da ita ga hukumar ta yi matukar illa.

Amma da yake mayar da martani, Festus Okoye, ya ce matsalar da aka samu wajen dora sakamakon zaben shugaban kasa na ranar 25 ga watan Fabrairu, bai kamata ya kawar da dukan zaben da aka gudanar a asar baki daya ba.

“Ba daidai ba ne a yi la’akari da dukkan ayyukan hukumar bisa ga kura-kuran da aka samu a sakamakon zaben shugaban kasa,” in ji shi.

Da yake karin haske a hirar ta gidan talabijin, Galadima ya shaidawa tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP da kuma Peter Obi na jam’iyyar Labour cewa suna bata lokaci suna kalubalantar nasarar shugaba Bola Tinubu.

Obi da Atiku sun gurfana gaban kotu domin kalubalantar nasarar Tinubu.

Sai dai Galadima, wanda ya yi ikirarin cewa an daura auren ne da kura-kurai, ya kara da cewa sakamakon zaben shugaban kasa da kotuna ba ta taba yin watsi da shi ba tun 1979.

M“Wane dan siyasa ne ya yi nasara a kotu tun 1979 a Nijeriya a karar da ya shigar da shugaban kasa? Me ya sa za mu barnata biliyan 10 ko biliyan 15 saboda mun ji wasu na kashe irin wadannan biliyoyin kudi a shafukan sada zumunta a kotun; idan muna da irin wadannan kudade za mu yi amfani da su wajen shiryawa babban zaben 2027.

“Jam’iyyar NNPP tana da karfi, idan ban da INEC ta goge tambarinmu a wasu jihohi, da mun yi nasara fiye da yadda ake zato,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Buba GaladimaCBNEmefieleINECNNPP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ganduje Ya Yi Allah-wadai Da Dakatar Da Albashin Ma’aikatan Da Gwamnatinsa Ta Dauka

Next Post

Dalibai Sun ‘Yantar Da Fursunoni 6 A Gidan Yarin Suleja

Related

An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

1 hour ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

8 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

8 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

11 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

20 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

1 day ago
Next Post
Dalibai Sun ‘Yantar Da Fursunoni 6 A Gidan Yarin Suleja

Dalibai Sun 'Yantar Da Fursunoni 6 A Gidan Yarin Suleja

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.