• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban INEC Ya Tafka Aika-Aika Fiye Da Emefiele, Ya Kamata A Kore Shi —Buba Galadima

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Shugaban INEC Ya Tafka Aika-Aika Fiye Da Emefiele, Ya Kamata A Kore Shi —Buba Galadima
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jigo a jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya yi kira ga shugaba Bola Tinubu da ya kori Mahmood Yakubu, Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC).

Ya yi magana ne a cikin wata hira da gidan talabijin na Channels.

  • Ganduje Ya Yi Allah-wadai Da Dakatar Da Albashin Ma’aikatan Da Gwamnatinsa Ta Dauka
  • Tinubu Na Bukatar Addu’a —Gbajabiamila

Galadima ya zargi shugaban INEC da yin zagon kasa ga ‘yan Nijeriya a zaben shugaban kasa da ya gabata.

Ya ce abin da Yakubu ya yi ya fi “zunuban” da Godwin Emefiele, Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya aikata.

“Dole ne shugaban INEC ya tafi, abin da ya yi ya fi abin da Godwin Emefiele ya yi. Ya hada baki da wasu mutane domin su muzgunawa ‘yan Nijeriya. Ya aikata laifi mafi girma da kowa zai yi,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a karkashin Yakubu ta sha suka sosai kan gazawarta na saka sakamakon zabe kamar yadda ta yi alkawari, lamarin da hukumar zaben ta dora alhakin tabarbarewar fasaha.

A wani taron manema labarai da ta gudanar a ranar Talata, tawagar da ke sa ido kan zabuka ta Tarayyar Turai ta ce amincewar da jama’a ke da ita ga hukumar ta yi matukar illa.

Amma da yake mayar da martani, Festus Okoye, ya ce matsalar da aka samu wajen dora sakamakon zaben shugaban kasa na ranar 25 ga watan Fabrairu, bai kamata ya kawar da dukan zaben da aka gudanar a asar baki daya ba.

“Ba daidai ba ne a yi la’akari da dukkan ayyukan hukumar bisa ga kura-kuran da aka samu a sakamakon zaben shugaban kasa,” in ji shi.

Da yake karin haske a hirar ta gidan talabijin, Galadima ya shaidawa tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP da kuma Peter Obi na jam’iyyar Labour cewa suna bata lokaci suna kalubalantar nasarar shugaba Bola Tinubu.

Obi da Atiku sun gurfana gaban kotu domin kalubalantar nasarar Tinubu.

Sai dai Galadima, wanda ya yi ikirarin cewa an daura auren ne da kura-kurai, ya kara da cewa sakamakon zaben shugaban kasa da kotuna ba ta taba yin watsi da shi ba tun 1979.

M“Wane dan siyasa ne ya yi nasara a kotu tun 1979 a Nijeriya a karar da ya shigar da shugaban kasa? Me ya sa za mu barnata biliyan 10 ko biliyan 15 saboda mun ji wasu na kashe irin wadannan biliyoyin kudi a shafukan sada zumunta a kotun; idan muna da irin wadannan kudade za mu yi amfani da su wajen shiryawa babban zaben 2027.

“Jam’iyyar NNPP tana da karfi, idan ban da INEC ta goge tambarinmu a wasu jihohi, da mun yi nasara fiye da yadda ake zato,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Buba GaladimaCBNEmefieleINECNNPP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ganduje Ya Yi Allah-wadai Da Dakatar Da Albashin Ma’aikatan Da Gwamnatinsa Ta Dauka

Next Post

Dalibai Sun ‘Yantar Da Fursunoni 6 A Gidan Yarin Suleja

Related

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa
Manyan Labarai

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

2 hours ago
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…
Manyan Labarai

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

3 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

13 hours ago
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo

22 hours ago
Buhari Ba Mutum Ne Mai Son Abun Duniya Ba – Gowon
Manyan Labarai

Buhari Ba Mutum Ne Mai Son Abun Duniya Ba – Gowon

1 day ago
Tinubu Bai Taɓa Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Bai Taɓa Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista

1 day ago
Next Post
Dalibai Sun ‘Yantar Da Fursunoni 6 A Gidan Yarin Suleja

Dalibai Sun 'Yantar Da Fursunoni 6 A Gidan Yarin Suleja

LABARAI MASU NASABA

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

July 11, 2025
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

July 11, 2025
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.