• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kasar Amurka Ya Gana Da Wang Yi

by CGTN Hausa
2 years ago
Wang yi

Babban jami’in diflomasiyyar kasar Sin ya bayyana a jiya Juma’a cewa, yana ziyara a kasar Amurka domin tattaunawa da bangaren Amurka kan aiwatar da muhimman matsaya da shugabannin kasashen biyu suka cimma, ta yadda za a tabbatar da daidaito da hana zaman lafiya tsakanin Sin da Amurka daga tabarbarewa, da dawo da alakarsu kan ingantaccen tafarkin ci gaba nan ba da jimawa ba. 

Wang Yi, mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar ya bayyana hakan ne yayin ganawa da shugaban kasar Amurka Joe Biden a birnin Washington D.C.

  • Bayan Nasara A Kotun Ƙoli, Tinubu Zai Ci Gaba Da Aikin Gina Nagartacciyar Ƙasa – Minista
  • CMG Ta Gabatar Da bukukuwan Baje Kolin Al’adun Sin Na Musamman A “Palace of Nations” Da Kasar Masar

Ya shaida wa Biden cewa manufar kasar Sin daya tilo a duniya da sanarwoyin hadin gwiwa guda uku tsakanin Sin da Amurka, su ne ginshikai mafi muhimmanci na dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, wadanda dole ne a kiyaye su ba tare da tsangwama ba.

Wang ya ce, “Ya kamata mu mutunta ka’idoji guda uku na mutunta juna, da zaman lafiya da samun moriyar juna da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar don daidaita dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.” Ya kara da cewa hakan ba wai kawai ya dace da muhimman muradun kasashen biyu da al’ummomin kasashen biyu ba ne, har ma da fatan al’ummar duniya baki daya.

Biden ya yi karin haske kan matsayinsa na dora muhimmanci kan dangantakar dake tsakanin Amurka da kasar Sin. Ya ce, Amurka a shirye take ta ci gaba da tuntubar kasar Sin, tare da tinkarar kalubalen duniya baki daya.

LABARAI MASU NASABA

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Shi Ministan harkokin wajen kasar Sin dai, yana ziyarar kwanaki uku a Amurka daga ranar 26 ga wata.

A lokacin da yake tattaunawa da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken, Wang Yi ya kuma yi kira da a samar da “Abubuwa biyar da suka zama dole” a dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka. Ya ce dole ne bangarorin biyu su kiyaye fahimtar juna da shugabannin kasashen biyu suka cimma, da daidaita huldar dake tsakanin kasashen biyu, da barin hanyoyin sadarwa a bude, da daidaita bambance-bambance tsakanin kasashen biyu da sabani yadda ya kamata, kuma dole ne a inganta hadin gwiwar moriyar juna.

Wang Yi ya kuma gana da mai ba da shawara kan harkokin tsaro na kasar Amurka, Jake Sullivan, inda ya jaddada cewa, babban kalubale ga dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka shi ne “Yancin kai na Taiwan” .(Yahaya)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya
Daga Birnin Sin

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103
Daga Birnin Sin

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Next Post
Kotu Ta Tabbatar Da Zaben Fintiri A Matsayin Gwamnan Adamawa

Kotu Ta Tabbatar Da Zaben Fintiri A Matsayin Gwamnan Adamawa

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.