• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kasar Amurka Ya Gana Da Wang Yi

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugaban Kasar Amurka Ya Gana Da Wang Yi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban jami’in diflomasiyyar kasar Sin ya bayyana a jiya Juma’a cewa, yana ziyara a kasar Amurka domin tattaunawa da bangaren Amurka kan aiwatar da muhimman matsaya da shugabannin kasashen biyu suka cimma, ta yadda za a tabbatar da daidaito da hana zaman lafiya tsakanin Sin da Amurka daga tabarbarewa, da dawo da alakarsu kan ingantaccen tafarkin ci gaba nan ba da jimawa ba. 

Wang Yi, mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar ya bayyana hakan ne yayin ganawa da shugaban kasar Amurka Joe Biden a birnin Washington D.C.

  • Bayan Nasara A Kotun Ƙoli, Tinubu Zai Ci Gaba Da Aikin Gina Nagartacciyar Ƙasa – Minista
  • CMG Ta Gabatar Da bukukuwan Baje Kolin Al’adun Sin Na Musamman A “Palace of Nations” Da Kasar Masar

Ya shaida wa Biden cewa manufar kasar Sin daya tilo a duniya da sanarwoyin hadin gwiwa guda uku tsakanin Sin da Amurka, su ne ginshikai mafi muhimmanci na dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, wadanda dole ne a kiyaye su ba tare da tsangwama ba.

Wang ya ce, “Ya kamata mu mutunta ka’idoji guda uku na mutunta juna, da zaman lafiya da samun moriyar juna da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar don daidaita dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.” Ya kara da cewa hakan ba wai kawai ya dace da muhimman muradun kasashen biyu da al’ummomin kasashen biyu ba ne, har ma da fatan al’ummar duniya baki daya.

Biden ya yi karin haske kan matsayinsa na dora muhimmanci kan dangantakar dake tsakanin Amurka da kasar Sin. Ya ce, Amurka a shirye take ta ci gaba da tuntubar kasar Sin, tare da tinkarar kalubalen duniya baki daya.

Labarai Masu Nasaba

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shi Ministan harkokin wajen kasar Sin dai, yana ziyarar kwanaki uku a Amurka daga ranar 26 ga wata.

A lokacin da yake tattaunawa da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken, Wang Yi ya kuma yi kira da a samar da “Abubuwa biyar da suka zama dole” a dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka. Ya ce dole ne bangarorin biyu su kiyaye fahimtar juna da shugabannin kasashen biyu suka cimma, da daidaita huldar dake tsakanin kasashen biyu, da barin hanyoyin sadarwa a bude, da daidaita bambance-bambance tsakanin kasashen biyu da sabani yadda ya kamata, kuma dole ne a inganta hadin gwiwar moriyar juna.

Wang Yi ya kuma gana da mai ba da shawara kan harkokin tsaro na kasar Amurka, Jake Sullivan, inda ya jaddada cewa, babban kalubale ga dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka shi ne “Yancin kai na Taiwan” .(Yahaya)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CGTNCMGCRI Hausa
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Rufe Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Mutane Masu Bukata Ta Musamman Ta Asiya A Hangzhou

Next Post

Kotu Ta Tabbatar Da Zaben Fintiri A Matsayin Gwamnan Adamawa

Related

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
Daga Birnin Sin

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

3 hours ago
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

4 hours ago
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

5 hours ago
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari
Daga Birnin Sin

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

6 hours ago
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
Daga Birnin Sin

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

7 hours ago
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

9 hours ago
Next Post
Kotu Ta Tabbatar Da Zaben Fintiri A Matsayin Gwamnan Adamawa

Kotu Ta Tabbatar Da Zaben Fintiri A Matsayin Gwamnan Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.