ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CMG Ta Gabatar Da bukukuwan Baje Kolin Al’adun Sin Na Musamman A “Palace of Nations” Da Kasar Masar

by CGTN Hausa
3 years ago
Cmg

A jiya Alhamis ne kafar CMG da ofishin MDD dake Geneva, da tawagar dindindin ta wakilan Sin dake Geneva, suka yi hadin gwiwar gabatar da bikin baje kolin al’adun Sin na musamman, a fadar kasashen duniya ta “palace of nations”. 

Shugaban CMG Shen Haixiong, da shugaban kwamitin raya al’adu na ofishin MDD dake Geneva Francesco Pisano, da kuma zaunannen wakilin Sin dake ofishin MDD dake Geneva da sauran kungiyoyin kasa da kasa dake Swizerland Chen Xu, sun halarci bikin tare da ba da jawabai.

  • Jakadan Sin Mai Kula Da Shirin Kwance Damarar Makamai Ya Yi Kira Da A Tabbatar Da Ikon Kasashe Masu Tasowa Na Yin Amfani Da Kimiyya Da Fasaha Cikin Lumana
  • Kamata Ya Yi Gwamnatin Amurka Ta Yi La’Akari Da Dalilan Karbuwar Gwamnan Jihar California A Kasar Sin

Wakiliyar musamman mai ba da shawara kan harkokin siyasa da huldar abokantaka, a ofishin babban jami’in MDD dake Geneva Lidiya Grigoreva, da dai sauran hukumomin kasa da kasa na MDD dake Geneva, da zaunannun wakilan kasashe fiye da 30 sun halarci bikin.

ADVERTISEMENT

Cikin jawabin da ya gabatar, Shen Haixiong ya ce, al’adun Sin na bayyana mutuncin Sinawa, da kuma bayyana abubuwa mafi kyau a cikin al’adun bil Adama. Kaza lika kasar Sin na dukufa kan farfado da al’adun ta a sabon zamani. A matsayin kafa mafi girma dake watsa labarai a dukkanin fannoni na dandalolin daban-daban, Shen ya ce CMG na sauke nauyin dake wuyansa na shaida ci gaban al’adu, da ingiza mu’amalar al’adu, ban da wannan kuma, tana kokarin hada tunani da kimiyya da fasaha tare, ta yadda al’umommin kasa da kasa za su sada zumanta, da tutunbar juna, don zamanintar da al’ummar duniya cikin hadin kai.

Yayin bikin na musamman na wannan karo, mai taken “Mafarin al’adun Sin da ci gabansa”, an yi amfani da kimiyya da fasahar zamani, don jagorantar masu kallo, ta yadda za su fahimci al’adun Sin masu tsawon tarihin fiye da shekaru 5000, da ma yadda ake samun ci gaba bisa wannan tushe.

LABARAI MASU NASABA

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Sannan a jiya Alhamis 26 ga wata ne, kafar CMG ta kuma gudanar da wani biki don kaddamar da nune-nunen “Journey Through Civilizations” wato hanyar fahimtar wayewar kai a cibiyar al’adun kasar Sin dake Alkahira, babban birnin kasar Masar. Mataimakin shugaban sashen fadakar da al’umma na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, wanda kuma shi ne shugaban CMG, Shen Haixiong ya yi jawabi ta kafar bidiyo.

A yayin jawabinsa, Shen Haixiong ya bayyana cewa, a cikin dogon tarihi, kyawawan wayewar kan kasar Sin da na tsohuwar kasar Masar sun ba da gudummawa sosai ga ci gaban wayewar kan dan Adam. Bisa ga kyakkyawan tsarin shawarar wayewar kai ta duniya da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar, jama’ar kasar Sin suna aiki tukuru don gina al’ummar kasar mai wayewar kai ta zamani, da sa kaimi ga neman sabon ci gaban wayewar kan dan Adam. Shen Haixiong ya kara da cewa, CMG zai tabbatar da aikin watsa labaru, da yin kirkire-kirkire, da yada wayewar kan kasar Sin, da karfafa mu’amalar al’adu tsakanin Sin da kasashen Larabawa, da sa kaimi ga yin shawarwari tsakanin al’ummomin Sin da kasashen Larabawa, da ba da hikimomi da karfi wajen bunkasa fahimtar juna da dankon zumunci tsakanin jama’ar Sin da kasashen Larabawa, da inganta gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga Sin da kasashen Larabawa. (Masu Fassarawa: Amina Xu, Bilkisu Xin)

CMG
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

MASU ALAKA

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen
Daga Birnin Sin

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Next Post
Gwamnati Ta Samo Jarin Fiye Da Dala Biliyan 2 A Bangaren Wutar Lantarki

Gwamnati Ta Samo Jarin Fiye Da Dala Biliyan 2 A Bangaren Wutar Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
CMG

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
CMG

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.