ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CMG Ta Gabatar Da bukukuwan Baje Kolin Al’adun Sin Na Musamman A “Palace of Nations” Da Kasar Masar

by CGTN Hausa
3 years ago
Cmg

A jiya Alhamis ne kafar CMG da ofishin MDD dake Geneva, da tawagar dindindin ta wakilan Sin dake Geneva, suka yi hadin gwiwar gabatar da bikin baje kolin al’adun Sin na musamman, a fadar kasashen duniya ta “palace of nations”. 

Shugaban CMG Shen Haixiong, da shugaban kwamitin raya al’adu na ofishin MDD dake Geneva Francesco Pisano, da kuma zaunannen wakilin Sin dake ofishin MDD dake Geneva da sauran kungiyoyin kasa da kasa dake Swizerland Chen Xu, sun halarci bikin tare da ba da jawabai.

  • Jakadan Sin Mai Kula Da Shirin Kwance Damarar Makamai Ya Yi Kira Da A Tabbatar Da Ikon Kasashe Masu Tasowa Na Yin Amfani Da Kimiyya Da Fasaha Cikin Lumana
  • Kamata Ya Yi Gwamnatin Amurka Ta Yi La’Akari Da Dalilan Karbuwar Gwamnan Jihar California A Kasar Sin

Wakiliyar musamman mai ba da shawara kan harkokin siyasa da huldar abokantaka, a ofishin babban jami’in MDD dake Geneva Lidiya Grigoreva, da dai sauran hukumomin kasa da kasa na MDD dake Geneva, da zaunannun wakilan kasashe fiye da 30 sun halarci bikin.

ADVERTISEMENT

Cikin jawabin da ya gabatar, Shen Haixiong ya ce, al’adun Sin na bayyana mutuncin Sinawa, da kuma bayyana abubuwa mafi kyau a cikin al’adun bil Adama. Kaza lika kasar Sin na dukufa kan farfado da al’adun ta a sabon zamani. A matsayin kafa mafi girma dake watsa labarai a dukkanin fannoni na dandalolin daban-daban, Shen ya ce CMG na sauke nauyin dake wuyansa na shaida ci gaban al’adu, da ingiza mu’amalar al’adu, ban da wannan kuma, tana kokarin hada tunani da kimiyya da fasaha tare, ta yadda al’umommin kasa da kasa za su sada zumanta, da tutunbar juna, don zamanintar da al’ummar duniya cikin hadin kai.

Yayin bikin na musamman na wannan karo, mai taken “Mafarin al’adun Sin da ci gabansa”, an yi amfani da kimiyya da fasahar zamani, don jagorantar masu kallo, ta yadda za su fahimci al’adun Sin masu tsawon tarihin fiye da shekaru 5000, da ma yadda ake samun ci gaba bisa wannan tushe.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Sannan a jiya Alhamis 26 ga wata ne, kafar CMG ta kuma gudanar da wani biki don kaddamar da nune-nunen “Journey Through Civilizations” wato hanyar fahimtar wayewar kai a cibiyar al’adun kasar Sin dake Alkahira, babban birnin kasar Masar. Mataimakin shugaban sashen fadakar da al’umma na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, wanda kuma shi ne shugaban CMG, Shen Haixiong ya yi jawabi ta kafar bidiyo.

A yayin jawabinsa, Shen Haixiong ya bayyana cewa, a cikin dogon tarihi, kyawawan wayewar kan kasar Sin da na tsohuwar kasar Masar sun ba da gudummawa sosai ga ci gaban wayewar kan dan Adam. Bisa ga kyakkyawan tsarin shawarar wayewar kai ta duniya da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar, jama’ar kasar Sin suna aiki tukuru don gina al’ummar kasar mai wayewar kai ta zamani, da sa kaimi ga neman sabon ci gaban wayewar kan dan Adam. Shen Haixiong ya kara da cewa, CMG zai tabbatar da aikin watsa labaru, da yin kirkire-kirkire, da yada wayewar kan kasar Sin, da karfafa mu’amalar al’adu tsakanin Sin da kasashen Larabawa, da sa kaimi ga yin shawarwari tsakanin al’ummomin Sin da kasashen Larabawa, da ba da hikimomi da karfi wajen bunkasa fahimtar juna da dankon zumunci tsakanin jama’ar Sin da kasashen Larabawa, da inganta gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga Sin da kasashen Larabawa. (Masu Fassarawa: Amina Xu, Bilkisu Xin)

CMG
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Gwamnati Ta Samo Jarin Fiye Da Dala Biliyan 2 A Bangaren Wutar Lantarki

Gwamnati Ta Samo Jarin Fiye Da Dala Biliyan 2 A Bangaren Wutar Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.