• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kasar Sin Ya Yi Shawarwari Da Manyan Shugabannin Kasar Saudiyya Da Kuma Gana Da Shugabannin Wasu Kasashen Larabawa Bi da Bi

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugaban Kasar Sin Ya Yi Shawarwari Da Manyan Shugabannin Kasar Saudiyya Da Kuma Gana Da Shugabannin Wasu Kasashen Larabawa Bi da Bi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gana da sarkin masarautar Saudiyya, Salman bin Abdul Aziz Al Saud a fadarsa dake birnin Riyadh a ran 8 ga wata da yamma, agogon wuri.

Xi ya ce, kasarsa ta mayar da Saudiyya a matsayin wata muhimmiyar kasa dake taka rawar gani a harkokin duniya, inda take fatan kara mu’amalar manyan tsare-tsare tare da Saudiyya, da zurfafa hadin-gwiwa a bangarori daban-daban, a wani kokari na kiyaye moriyarsu, da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya.

  • Rashin Tsoma Baki Ya Sa Kasar Sin Ke Samun Karin Abokai

A nasa bangaren, sarki Salman ya yi marhabin lale da zuwan shugaba Xi, inda a cewarsa, yana matukar maida hankali kan raya dangantaka tare da kasar Sin, da kuma bayyana fatansa na samar da ci gaban huldodin kasashen biyu, bisa manyan tsare-tsare kuma daga dukkanin fannoni.

Shugabannin biyu sun kuma rattaba hannu kan yarjejeniyar kulla dangantakar abota bisa manyan tsare-tsare kuma daga dukkanin fannoni, tsakanin Jamhuriyar Jama’ar Kasar Sin da kasar Saudiyya, inda suka amince cewa, za su gana a kasashensu a kowace shekara.

A dai wannan rana, shugaba Xi ya yi shawarwari tare da yariman masarautar Saudiyya, kana firaministan kasar Muhammad bin Salman bin Abdel Aziz Al Saud, inda suka yarda cewa, za su daga matsayin shugabancin kwamitin hadin-gwiwar manyan jami’an kasashen biyu, zuwa matsayin firaminista.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

Shugabannin biyu sun kuma halarci bikin mika wa juna takardun yarjeniyoyin hadin-gwiwar kasashensu, a fannonin da suka shafi raya shawarar “ziri daya da hanya daya”, da aikin shari’a, da ilimi, da makamashin hydrogen, da zuba jari, da gidajen kwana da sauransu.

Bayan shawarwarin, shugaba Xi ya halarci bikin maraba da yariman Muhammad ya shirya masa, a madadin sarkin Salman bin Abdul Aziz Al Saud.

Sannan a wannan rana da yamma, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya kuma gana da takwaransa na kasar Masar, Abdel Fattah al Sisi a Riyadh, babban birnin kasar Saudiyya.

Yayin ganawar, Xi ya ce, bisa halin da ake ciki yanzu a duk duniya, da ma shiyyoyi daban-daban na fuskantar manyan sauye-sauye, yana da muhimmanci a raya huldodin Sin da Masar bisa manyan tsare-tsare kuma daga dukkan fannoi. Ya ce ya dace kasashen biyu su yi kokari tare, don neman cimma burin gina al’ummominsu masu kyakkyawar makoma ta bai daya, ta yadda za’a kara samar da sabon ci gaba, ga dangantakarsu bisa manyan tsare-tsare kuma daga dukkan fannoni.

A nasa bangaren, shugaba Sisi ya ce, ya zo kasar Sin don halartar bikin bude gasar wasannin Olympics ta lokacin hunturu da aka yi a watan Fabrairun bana a Beijing, inda ya yi shawarwari masu gamsarwa tare da shugaba Xi. Ya ce, ya ziyarci kasar Sin a wancan lokacin ne don goyon bayan kasar, da karfafa dangantaka tare da kasar. Sisi yana da yakinin cewa, a sabon wa’adin aikin shugaba Xi, dangantakar kasashen biyu za ta samu karin ci gaba, kana, kwalliya za ta biya kudin sabulu, wajen karfafa hadin-gwiwarsu a bangaren shawarar “ziri daya da hanya daya”.

Bugu da kari, da safiyar yau 9 ga wata ne, bi da bi shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwarorinsa na kasar Tunisiya Kais Saied da na kasar Mauritaniya Mohamed Ould Ghazouani da na kasar Djibouti Ismail Omar Guelleh da na kasar Somaliya Hassan Sheikh Mohamud da na Comoros Azali Assoumani da firaministan kasar Iraki Mohammed Shia al-Sudani da sarki Tamim Bin Hamad Al Thani na masarautar Qatar a birnin Riyadh, fadar mulkin kasar Saudiyya. (Murtala Zhang, Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Li Keqiang Ya Halarci Taron Tattaunawa Tare Da Shugabannin Manyan Hukumomin Tattalin Arzkin Duniya

Next Post

Gasar Cin Kofin Duniya: Croatia Ta Kora Brazil Gida

Related

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

15 hours ago
Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi
Daga Birnin Sin

Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

15 hours ago
Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba
Daga Birnin Sin

Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

16 hours ago
Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar

16 hours ago
Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025

17 hours ago
Gwamnatin Sin: Gwamnatin Jama’a Domin Jama’a
Daga Birnin Sin

Gwamnatin Sin: Gwamnatin Jama’a Domin Jama’a

17 hours ago
Next Post
Gasar Cin Kofin Duniya: Croatia Ta Kora Brazil Gida

Gasar Cin Kofin Duniya: Croatia Ta Kora Brazil Gida

LABARAI MASU NASABA

Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

August 6, 2025
Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

August 6, 2025
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

August 6, 2025
Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

August 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

August 6, 2025
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

August 6, 2025
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

August 5, 2025
Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

August 5, 2025
Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

August 5, 2025
Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

August 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.