• English
  • Business News
Sunday, June 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Nijeriya Na Gaba Zai Kashe Kudaden Haraji Ne Kan Biyan Bashi –IMF

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Shugaban Nijeriya Na Gaba Zai Kashe Kudaden Haraji Ne Kan Biyan Bashi –IMF
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

Asusun bayar da lamuni na duniya (IMF) ya bayyana cewa shugaban kasan Nijeriya da zai gaji Muhammadu Buhari bayan karewar wa’adin mulkinsa a ranar 29 ga watan Mayu na shekara mai zuwa, zai kashe kudaden harajin da Nijeriya za ta samu a wajen biyan bashi ne har zuwa shekarar 2026.

A halin yanzu dai, gwamnatin tarayya tana kashe kusan kaso 80 kan biyan bashi kadai, wanda ta bai wa ayyukan ci gaba na tsakanin kaso 15 zuwa 20.
Illar dai ita ce, kowani kobo 100 da aka samu, kasa da kobo 20 ne kadai ake tafiyartar da su wajen cika alkawarin da aka dauka lokacin yakin neman zabe.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Kwamitin Da Zai Lalubo Hanyar Magance Tsadar Kayan Masarufi

A haka kuma, gwamnatin tarayya tana shirin kara kinkimo wa Nijeriya bashin kari da na naira tiriliyan 46.63 kafin karshen shekarar 2022.

“Duk da karancin samun kudaden shiga, wanda akwai bukatar samar da ababen more rayuwa a Nijeriya. Yana da matukar muhimmanci a samu daidaituwar tattalin arziki a Nijeriya tare da samun kayayyakin more rayuwa da za su inganta harkokin al’umma,” in ji Mista Ari Aisen.
Ya kara da cewa Nijeriya a matsayinta na mai fitar da arzikin man fetur ta kasa samun alfanun karuwar farashin man fetur a duniya wajen samar da ayyukan ci gaba kasa, sakamakon makudan kudaden da take kashewa wajen biyan tallafi a bangaren man fetur.
IMF ya gargadi gwamnatin tarayya da ta gudanar da daukan matakin gaggawa wajen karuwar samar da kudaden shiga, idan kuma ba haka ba za ta ci gaba da biyan bashi har zuwa shekarar 2026.
Asusun ya ci gaba da bayyana cewa, bisa turbar da Nijeriya take a halin yanzu na tattalin arziki, kudaden ruwa na bashi za su lakume gaba daya kudaden shigan Nijeriya na tsawan shekaru hudu.
Wakilin IMF a Nijeriya, Mista Ari Aisen ya bayyana hakan lokacin da yake gabatar da rahoto kan tattalin arzikin yankin Afirka wanda ya gudana a Abuja.
Gwamnatin tarayya za ta kashe naira tiriliyan 3.61 wajen bayan bashi a cikin kasafin kudin Nijeriya na shekarar 2022.
Naira tiriliyan 3.61 da aka amfani da shi wajen biyan bashi shi ne kashi 34 na adadin yawan kudaden haraji da ake tsammanin gwamnatin tarayya za ta samu a 2022.
Nijeriya ta tsinci kanta a cikin mummunan bashi wanda ya kai na naira tiriliyan 45, yayin da ofishin kula da basuka ke kara shirin amso bashi na naira tiriliyan 6.39 domin a cike cibin kashafin kudi na shekarar 2022.
Gwamnatin Shugaban kasa Muhammadu Buhari tana fuskantar matsinlamba kan karuwar yawan basukan da ake bin kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yayin Da Atiku Ya Zama Kwamandan PDP A 2023…Kallo Ya Koma APC

Next Post

Yadda Mutanen Buhari Suka Sha Kaye A Zaben Fitar Da Gwanin APC A Kano

Related

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 day ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 week ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 week ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

4 weeks ago
IMF
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

4 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

4 weeks ago
Next Post
Wata Budurwa ‘Yar Shekara 28 Ta Kayar Da Dan Majalisa A Zaben Fidda Gwani Na APC A Inugu

Yadda Mutanen Buhari Suka Sha Kaye A Zaben Fitar Da Gwanin APC A Kano

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

June 1, 2025
Gwamnan kano

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

June 1, 2025
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

June 1, 2025
An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

June 1, 2025
Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

June 1, 2025
Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo

Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo

June 1, 2025
Yadda Za Ki Hada Funkasonki

Yadda Za Ki Hada Funkasonki

June 1, 2025
Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

May 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.