• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Nijeriya Na Gaba Zai Kashe Kudaden Haraji Ne Kan Biyan Bashi –IMF

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Shugaban Nijeriya Na Gaba Zai Kashe Kudaden Haraji Ne Kan Biyan Bashi –IMF
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

Asusun bayar da lamuni na duniya (IMF) ya bayyana cewa shugaban kasan Nijeriya da zai gaji Muhammadu Buhari bayan karewar wa’adin mulkinsa a ranar 29 ga watan Mayu na shekara mai zuwa, zai kashe kudaden harajin da Nijeriya za ta samu a wajen biyan bashi ne har zuwa shekarar 2026.

A halin yanzu dai, gwamnatin tarayya tana kashe kusan kaso 80 kan biyan bashi kadai, wanda ta bai wa ayyukan ci gaba na tsakanin kaso 15 zuwa 20.
Illar dai ita ce, kowani kobo 100 da aka samu, kasa da kobo 20 ne kadai ake tafiyartar da su wajen cika alkawarin da aka dauka lokacin yakin neman zabe.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Kwamitin Da Zai Lalubo Hanyar Magance Tsadar Kayan Masarufi

A haka kuma, gwamnatin tarayya tana shirin kara kinkimo wa Nijeriya bashin kari da na naira tiriliyan 46.63 kafin karshen shekarar 2022.

“Duk da karancin samun kudaden shiga, wanda akwai bukatar samar da ababen more rayuwa a Nijeriya. Yana da matukar muhimmanci a samu daidaituwar tattalin arziki a Nijeriya tare da samun kayayyakin more rayuwa da za su inganta harkokin al’umma,” in ji Mista Ari Aisen.
Ya kara da cewa Nijeriya a matsayinta na mai fitar da arzikin man fetur ta kasa samun alfanun karuwar farashin man fetur a duniya wajen samar da ayyukan ci gaba kasa, sakamakon makudan kudaden da take kashewa wajen biyan tallafi a bangaren man fetur.
IMF ya gargadi gwamnatin tarayya da ta gudanar da daukan matakin gaggawa wajen karuwar samar da kudaden shiga, idan kuma ba haka ba za ta ci gaba da biyan bashi har zuwa shekarar 2026.
Asusun ya ci gaba da bayyana cewa, bisa turbar da Nijeriya take a halin yanzu na tattalin arziki, kudaden ruwa na bashi za su lakume gaba daya kudaden shigan Nijeriya na tsawan shekaru hudu.
Wakilin IMF a Nijeriya, Mista Ari Aisen ya bayyana hakan lokacin da yake gabatar da rahoto kan tattalin arzikin yankin Afirka wanda ya gudana a Abuja.
Gwamnatin tarayya za ta kashe naira tiriliyan 3.61 wajen bayan bashi a cikin kasafin kudin Nijeriya na shekarar 2022.
Naira tiriliyan 3.61 da aka amfani da shi wajen biyan bashi shi ne kashi 34 na adadin yawan kudaden haraji da ake tsammanin gwamnatin tarayya za ta samu a 2022.
Nijeriya ta tsinci kanta a cikin mummunan bashi wanda ya kai na naira tiriliyan 45, yayin da ofishin kula da basuka ke kara shirin amso bashi na naira tiriliyan 6.39 domin a cike cibin kashafin kudi na shekarar 2022.
Gwamnatin Shugaban kasa Muhammadu Buhari tana fuskantar matsinlamba kan karuwar yawan basukan da ake bin kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yayin Da Atiku Ya Zama Kwamandan PDP A 2023…Kallo Ya Koma APC

Next Post

Yadda Mutanen Buhari Suka Sha Kaye A Zaben Fitar Da Gwanin APC A Kano

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

5 hours ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

6 hours ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

5 days ago
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Tambarin Dimokuradiyya

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

7 days ago
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

1 week ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

1 week ago
Next Post
Wata Budurwa ‘Yar Shekara 28 Ta Kayar Da Dan Majalisa A Zaben Fidda Gwani Na APC A Inugu

Yadda Mutanen Buhari Suka Sha Kaye A Zaben Fitar Da Gwanin APC A Kano

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.