ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Nijeriya Na Gaba Zai Kashe Kudaden Haraji Ne Kan Biyan Bashi –IMF

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
IMF

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Asusun bayar da lamuni na duniya (IMF) ya bayyana cewa shugaban kasan Nijeriya da zai gaji Muhammadu Buhari bayan karewar wa’adin mulkinsa a ranar 29 ga watan Mayu na shekara mai zuwa, zai kashe kudaden harajin da Nijeriya za ta samu a wajen biyan bashi ne har zuwa shekarar 2026.

A halin yanzu dai, gwamnatin tarayya tana kashe kusan kaso 80 kan biyan bashi kadai, wanda ta bai wa ayyukan ci gaba na tsakanin kaso 15 zuwa 20.
Illar dai ita ce, kowani kobo 100 da aka samu, kasa da kobo 20 ne kadai ake tafiyartar da su wajen cika alkawarin da aka dauka lokacin yakin neman zabe.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Kwamitin Da Zai Lalubo Hanyar Magance Tsadar Kayan Masarufi

A haka kuma, gwamnatin tarayya tana shirin kara kinkimo wa Nijeriya bashin kari da na naira tiriliyan 46.63 kafin karshen shekarar 2022.

ADVERTISEMENT

“Duk da karancin samun kudaden shiga, wanda akwai bukatar samar da ababen more rayuwa a Nijeriya. Yana da matukar muhimmanci a samu daidaituwar tattalin arziki a Nijeriya tare da samun kayayyakin more rayuwa da za su inganta harkokin al’umma,” in ji Mista Ari Aisen.
Ya kara da cewa Nijeriya a matsayinta na mai fitar da arzikin man fetur ta kasa samun alfanun karuwar farashin man fetur a duniya wajen samar da ayyukan ci gaba kasa, sakamakon makudan kudaden da take kashewa wajen biyan tallafi a bangaren man fetur.
IMF ya gargadi gwamnatin tarayya da ta gudanar da daukan matakin gaggawa wajen karuwar samar da kudaden shiga, idan kuma ba haka ba za ta ci gaba da biyan bashi har zuwa shekarar 2026.
Asusun ya ci gaba da bayyana cewa, bisa turbar da Nijeriya take a halin yanzu na tattalin arziki, kudaden ruwa na bashi za su lakume gaba daya kudaden shigan Nijeriya na tsawan shekaru hudu.
Wakilin IMF a Nijeriya, Mista Ari Aisen ya bayyana hakan lokacin da yake gabatar da rahoto kan tattalin arzikin yankin Afirka wanda ya gudana a Abuja.
Gwamnatin tarayya za ta kashe naira tiriliyan 3.61 wajen bayan bashi a cikin kasafin kudin Nijeriya na shekarar 2022.
Naira tiriliyan 3.61 da aka amfani da shi wajen biyan bashi shi ne kashi 34 na adadin yawan kudaden haraji da ake tsammanin gwamnatin tarayya za ta samu a 2022.
Nijeriya ta tsinci kanta a cikin mummunan bashi wanda ya kai na naira tiriliyan 45, yayin da ofishin kula da basuka ke kara shirin amso bashi na naira tiriliyan 6.39 domin a cike cibin kashafin kudi na shekarar 2022.
Gwamnatin Shugaban kasa Muhammadu Buhari tana fuskantar matsinlamba kan karuwar yawan basukan da ake bin kasar nan.

IMF
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Wata Budurwa ‘Yar Shekara 28 Ta Kayar Da Dan Majalisa A Zaben Fidda Gwani Na APC A Inugu

Yadda Mutanen Buhari Suka Sha Kaye A Zaben Fitar Da Gwanin APC A Kano

LABARAI MASU NASABA

Na Tsaya Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Tsaya Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026
Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

July 13, 2026
Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.