• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Nijeriya Na Gaba Zai Kashe Kudaden Haraji Ne Kan Biyan Bashi –IMF

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Shugaban Nijeriya Na Gaba Zai Kashe Kudaden Haraji Ne Kan Biyan Bashi –IMF
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

Asusun bayar da lamuni na duniya (IMF) ya bayyana cewa shugaban kasan Nijeriya da zai gaji Muhammadu Buhari bayan karewar wa’adin mulkinsa a ranar 29 ga watan Mayu na shekara mai zuwa, zai kashe kudaden harajin da Nijeriya za ta samu a wajen biyan bashi ne har zuwa shekarar 2026.

A halin yanzu dai, gwamnatin tarayya tana kashe kusan kaso 80 kan biyan bashi kadai, wanda ta bai wa ayyukan ci gaba na tsakanin kaso 15 zuwa 20.
Illar dai ita ce, kowani kobo 100 da aka samu, kasa da kobo 20 ne kadai ake tafiyartar da su wajen cika alkawarin da aka dauka lokacin yakin neman zabe.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Kwamitin Da Zai Lalubo Hanyar Magance Tsadar Kayan Masarufi

A haka kuma, gwamnatin tarayya tana shirin kara kinkimo wa Nijeriya bashin kari da na naira tiriliyan 46.63 kafin karshen shekarar 2022.

“Duk da karancin samun kudaden shiga, wanda akwai bukatar samar da ababen more rayuwa a Nijeriya. Yana da matukar muhimmanci a samu daidaituwar tattalin arziki a Nijeriya tare da samun kayayyakin more rayuwa da za su inganta harkokin al’umma,” in ji Mista Ari Aisen.
Ya kara da cewa Nijeriya a matsayinta na mai fitar da arzikin man fetur ta kasa samun alfanun karuwar farashin man fetur a duniya wajen samar da ayyukan ci gaba kasa, sakamakon makudan kudaden da take kashewa wajen biyan tallafi a bangaren man fetur.
IMF ya gargadi gwamnatin tarayya da ta gudanar da daukan matakin gaggawa wajen karuwar samar da kudaden shiga, idan kuma ba haka ba za ta ci gaba da biyan bashi har zuwa shekarar 2026.
Asusun ya ci gaba da bayyana cewa, bisa turbar da Nijeriya take a halin yanzu na tattalin arziki, kudaden ruwa na bashi za su lakume gaba daya kudaden shigan Nijeriya na tsawan shekaru hudu.
Wakilin IMF a Nijeriya, Mista Ari Aisen ya bayyana hakan lokacin da yake gabatar da rahoto kan tattalin arzikin yankin Afirka wanda ya gudana a Abuja.
Gwamnatin tarayya za ta kashe naira tiriliyan 3.61 wajen bayan bashi a cikin kasafin kudin Nijeriya na shekarar 2022.
Naira tiriliyan 3.61 da aka amfani da shi wajen biyan bashi shi ne kashi 34 na adadin yawan kudaden haraji da ake tsammanin gwamnatin tarayya za ta samu a 2022.
Nijeriya ta tsinci kanta a cikin mummunan bashi wanda ya kai na naira tiriliyan 45, yayin da ofishin kula da basuka ke kara shirin amso bashi na naira tiriliyan 6.39 domin a cike cibin kashafin kudi na shekarar 2022.
Gwamnatin Shugaban kasa Muhammadu Buhari tana fuskantar matsinlamba kan karuwar yawan basukan da ake bin kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yayin Da Atiku Ya Zama Kwamandan PDP A 2023…Kallo Ya Koma APC

Next Post

Yadda Mutanen Buhari Suka Sha Kaye A Zaben Fitar Da Gwanin APC A Kano

Related

Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

2 days ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Tambarin Dimokuradiyya

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

2 days ago
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

2 days ago
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

3 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

3 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

4 weeks ago
Next Post
Wata Budurwa ‘Yar Shekara 28 Ta Kayar Da Dan Majalisa A Zaben Fidda Gwani Na APC A Inugu

Yadda Mutanen Buhari Suka Sha Kaye A Zaben Fitar Da Gwanin APC A Kano

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.